Showing 189001 words to 192000 words out of 299981 words

Chapter 64 - Sarautar Mata By Makawa

04 Dec 2025

17646

shi su san mijina,
Dubu biyar mansur ya basu su raba suna ta murna da addua da jin dadi don gani suke kaman an basu dubu dari ne,
Ina dakin Inno gwago ta,aika akirani wai nazo mu gaisa da,su,
Banji dadi ba naso ace har,su tafi kada su ganni amma ba yadda zan yi dole nabi umurnin iyayyena ,
Katon hijjab ne ajikina mai ruwan milk color har kasa nashigo dakin acikin sanyin muryana na kamar ta rowa nai masu sannu da zuwa na,samu dan guri can nesa na tsugun na,
Mansur nake gayyarwa batare da na dago kaina ba naji muryan Hamza yana cewa,
Humaira ya muka samay ku kinzo gida kinga yan uwa kin zauna abinki baki ko tuna mu ko ?
Namiji ke nan baida kunya may yake nufi, watau, shi baima san anyi min wani abuba ke nan ko zamana nayi don kaina ko
Sun tambaya suna son wucewa dani amma sai su baba suke cewa, sun so ace tunda haihuwan fari zanyi na zauna har sai na haihu amma kuma idan suyi haka,basu kyautawa su Ummi ba,da mijin ta don haka su tafi idan an shirya zamu zo da gwagona da daya,daga cikin matan gidan don suga guri na,
Anyi sallama dasu akan cewa zuwa wani sati insha Allahu zamu dawo garin tare da yan uwa na,
Sukai muna sallama suka kama hanya bakin su dauke da maganan zancen labarin cikin dake a jikina da basu da labarin shi,,,

****** ********* ******
Ikon Allah inji Umma da mama da suke sauraren bayanin da Hamza din yake masu,
Yanzu ita yarinyan ga cikine ajikin ta har tai laulayinta a gidan nan ba wanda ya sani, mama hafsi ce take fadin haka,
Yanzu dai cikin watan shi nawa don a,lissafa a gani ita dai yanzu a lissafina watan ta na uku ke nan bata gidan nan, Umma ce mai fadin haka,
Wata bakwai da,wani abu, kenan sukace don sun so abarta can harta haihu amma kuma daga baya,sai suka ce idan sunyi haka basu kyautawa Baba Mudi ba,
Kaji gaskiya lalai Aisha taci sunan ta na yar Agwai halin irin na fulanin asali, watau ga kunya ga kuma zurfin ciki,
Yanzu ita mahaifiyarta ta san zancen cikin ke nan ko sukai muna rufafa akan shi ko yaya Umma ta kara tambaya a cikin son jin yadda abin yake,
Hamza yace anya kuwa suna da wanan labarin don dai da Baba ta fadamin gaskiya,
Mama hafsi cikin jin dadi take cewa Allah mun gode maka, kai kayin yadda kaso aduk lokacin da kaga dama yau dai dada zancen juya ya kare kuma a gidan nan sai anemi wata,
Mama hafsi ne taje gurin mama Rahana da zancen ita kuma ta tafi gurin Ummi duk sunyi mamakin jin wanan labarin su ma,
Nan Ummi take fadawa su mama,saude da Atika suma dai sunyi murnan fili tare da fatan Allah ya raba lafiya,
Zance ya fara dan yawo a,cikin shiya har maganan yakai ga kunnen, Sadiya da uwarta,
Ai kuwa ba karamin tashin hankali, suka shiga ba don duk sun rude,
Sadiya ranan bala,i tasa wai bata yarda ba na tafi na dauko ciki a waje an kananadeshi za ace wai nashi,
Ranshi ya baci yace wallahi kada tafara ta sheganta mashi cikin shi idan bata da hankali ne shi yana da shi,
Nan sukai ta sa in sa da ita take cewa wai ya ce baida kudi a ina ya samu kudin motan zuwa har garin mu guri na,
Don haka sai ya biyata kudin ta ko ayi bala,i a gidan don bazata yarda ba ya karbar mata kudi, ya tafi gurin matanshi da su,
Yace kudin ki dana karba a gaban ki nai laluran da zanyi dasu ba,wai su nayi amfani dasu zuwa garin su Aisha ba,
Tun suna yin fitinan a cikin daki har takai sun futo waje nan Sadiya ta rike mai wuya akan cewa sai ya bata kudin ta, ko ta yi karan shi,
Yana cewa sakeni amma ta rike shi gam nan kokuwa ya fara a,tsakanin su sai dambe ya kaure ,
Abinda yasa su Umma,saurin fitowa daga dakunan su da,sauri kena suna cewa su bari kada yajin mata ciwo,
Umma tana zuwa ta na kokarin jaye Sadiya ta sai Sadiya ta Juyo da karfi ta ture Umma da karfi tafadi zaune ta baya a cikin roban kullun (kamu) su saida bayan ta ya amsa,
Duk kullun ya zuba mata,ajiki yakuma bata ko ina na gidan gaba daya yai masu fenti,
Wani irin kara Umma ta sake da karfi tana fadin wayyo Allah na,zasu karasani sun halakani ni Rabi, yau na shiga uku na lalace,
Haka yasa Hanza dake dukan Sadiya ya,daina yayo kan Umma don ya taimaka mata,
Ina kasa tashi tayi ai sai yaranta suka,sa ihu suna cewa wayyo ta kashe muna uwar mu,
Su kuma Sa,a da Asmau sukai kan Sadiya da duka duk inda suka,samu bugu suke da kyat mutane suka kwace ta a hannun su,
Nan ta figi gyalen ta jina jina tai police station kai kara wai aga irin ta,asar da mijinta da kan nen shi sukai mata,
Ita kuma Umma aka kwashe zuwa dakin ta ana mata hitara sai nishi takeyi kamar zata mutu,
Hamza ya koma daki don ya cire rigar shi da,Sadiya ta yaga mai yai kaca kaca, dashi,
Mama tace kada yai saurin cirewa ya tafi dashi police station haka na don aga sheda,
Take zance ya gama ruda uguwa mutane suka,shiga zagin Sadiya nan Uwar ta tashigo gidan da nata tawagan,
Amma suna ganin irin ta,asan da akaiwa Umma sai jikin su yai sanyi dole akaje daukowa Umma mai duban kariya saboda a duba lafiyan ta,
Yan sanda sukazo gida din tafiya da Hamza nan mutanen Uguwa suka mara mashi baya irin su baba Mudi da,sauran dattijan uguwa,
An mayar da basain zancen an fahinci matsalace ta maurata don haka akace su tafi gida su sulhunta a tsakanin su,
Umma ta samu targade a kwatolon ta don haka dole sai an dan mata dori a kan shi kafanta ma ya,gwauce sai an ja matashi,
Anaja tana hawaye sai faman nishi da gumza na,wahala takeyi mutane suna mata sannu dafa wajen kofan ta,



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABUIDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,



Yana tsaye a bakin bakin gado yana dauko kaya daga cikin ledan shi, da ya,shigo dakina da shi,
Yana kokarin ciro kaya daga cikin ledan ban mai magana ba,sai samun guri da nayi na zauna a hannun kujera na,
Dan juyowa yayi inda nake zaune don tun da na,dawo a,wanan lokacin ne muka samu kebewa a tsakanin mu sai a wanan lokacin,
Sannu da,aiki yace min yana kokarin saka wani wando a jikin shi batare da ya jira na amsa mai ba yake ce min,
Kada faki dinga aikin da yafi karfin ki yanzu tunda kina a cikin condition kada kijawa kan ki ciwo,
Ban ce uffan ba,sai mikewan da nayi na kwashe kayan daudan da ya kwabe min a tsakar dakina,
Nafita da su har lokacin Sadiya tana zaune daga kofan ta tana dan bubuga kafan ta a hankali,
Kafin na koma dakin yafito zuwa kofan gidan ni kuma,sai na,wanke kayan daudan don ban son tara kayan wanki a,dakina,
Lokacin da nake shanya kayan ne naji muryan Sadiya a kaina tana fadin amma dai kin san cewa nice da hakkin wanke kayan nan bake ba ko,
Tankar ban ji ta ba nai banza da ita kamar badani takeyi ba,
Takara matsowa kusa da gurin da nake tsaye tana cewa, duk wani rawan kan da akeyi a kan dawowan ki ni bai rudani tunda nasan badon Allah akeyin shi ba,
Kafin na bata amsa sai muryan Ibrahim wanda ya shigo gida yayi alwala, muka ji yana cewa ke Sadiya iskan cin naki kuma har ya kawo ga wanan boyar Allah da bata ma,san kina yi ba,
Tace au ashe boyar Allah ce niko boyar ka ko ?
Gaf da ita ya karaso cikin nuna mata dan yatsa yake cewa wallahi wallahi iskanci kada ya kawo a kaina don zan iya maki mugun bungun da sai kin kwanta asibiti wallahi,
Mama tai sauri fitowa daga dakin ta tana cewa kada kafara kyale ta tai tayi tunda ita bata da marmari ,
Kayi abu ance ka barshi bata san ta barshi ba,sai ankai ga yadda ba,a son kaiwa sannan hankalinta ya kwanta,
Barta mama Wallahi ni yanzu sai nayi fata fata da ita Allah ko,
Tunda kaine Ubana ai sai ka yi mugani to aida kina da uban ne zakice mu na haka keda kike yar mace,
Haba yau ina wuta Sadiya ta saka Ibrahim nan ta hau zagi da ashar da zari sai da Ibrahim yakai ga zuba mata mari biyu masu kyau ta,samu guri ta nade kamar ta somay,
Sai can ta yanka wani iri uban ihu ta fadi kasa tana shure shure a cikin kasa,
Mama tace taufa ai kinkai ga yadda kike son akai ni wanan yarinyar masifan ki wallahi ya ishe ni a gidan nan haba dai yarinya sai kace iblishiya ,
Umma tana daki bakin ciki da takaici duk ya kumay ta sai jijiga kai take tana hadiyan zuciya don ta dauko wutan gasa kanta cikin gidan ta,
Hamza yana,daga kofan gida zaune a majalissan su duk suna jin irin hayaniyan da akeyi har zuwa fitowan Ibrahim yana huci,
Kunya da takaici duk sun rufe shi inda yake zaune cikin takaici da dana sanin auren Sadiya a rayuwan shi,
Tir da Allah dai kawai yan majalissan kofan gida suke mata don dama tunda ban gari ko ruwan sha,suka aika bata basu ko na,alwala balle wani abin, ta kai masu ko ina,su ma don ba haka muka saba zama dasu ba,

****** ********* ******
Saboda sanyin da akeyi dole kowa ya shige dakin shi don sanyi yayi yawa a ranan,
Daga massalaci Hamza gida yadawo dakin Umma ya fara shiga ya,samu mama tana hada mata maganin ta yai masu sannu da jiki,
Sai Mama ce ke cewa fadan ka dai ya koma a kan Ibrahim dashi akai fitinan yau kuma,
Tsaki kawai yaja tare da cewa kai Allah dai ya kyauta wanan hali na,Sadiya baiyi ba wallahi,
Yana tambayan Umma ko ta ci abinci mama tace ai yau sai kwano duk ta cinye,
Murmushi irin na mara lafiya Umma tayi tace badole na ba yau kwanon miyana da nama aciki har tsoka biyar ga mai da kamshi na tashi a miya sabanin karni da zai daki hancin mutum,
Sa,a datu tace wallahi ni yau har karawa nayi don dadin abinci bansan yadda akayi na cinye shi ba tas har wanda na karo duk na ciye,
Allah ya kyauta yace tare da mikewa ya na shirin barin dakin sai mama take ce mai tau matar kadai ta tafi gidan su tunda magariba,
Hmmm, Allah ya kyauta yace, tare da dan guntun murmusawa, kawai,
Babu inda zaka in taga dama taita zama can har abada amma babu mai binta, a gidan nan,
Umma ce ke wanan magana haka a hasale cikin dan daga muryan ta,alamar ranta ya baci,
Zaune nake abinka ga mai tsohon ciki gashi kuma na kwana biyu banyi aiki ba, sai naji duk yar gajiya ta kama min jikina,
Da,sallama dauke a bakin shi ya shigo dakin idanuwan shi a kaina inda nake dan gishingide gefen kujera na nai filo da shi,
Maimakon nai mashi sannu da zuwa irin yadda na saba yi mashi, da,farko sai kawai na,share shi kamar ban san shigowan shi ba dakin,
A, hankali yakai zaune gefe yana cewa Yay Allah tare da zama ya mike kafafunan shi kan shi yana a masangalin kujeran, danake zaune a kai,
Shiru ne ya,dan biyo baya dakin dagani har shi ba wanda yai magana sai can cikin wata kasalaliyar murya naji shi yana fadin
Hummai, wai fushi kike danine ko kuwa don naga kamar har yanzu baki huce ba still kina jin haushina, haka,
Sai naji ya wani furzo iska daga bakin shi tare da dunkule hannayen shi guri daya,
Cikin yar muryan da ba zai iya fassarata ba nake cewa akawo maka abinci ne yanzu,
Cikin dan marairaicewa yace idan na samu zanci ai, tunda za,a bani ai na gode,
Mikewa nayi na jawo dan stol din dakina na aje mai a gaban shi tare da kawo mai ruwan sha mai sanyi,
Fita na yi don na kwaso shanyin da na shanya da yamman nan ,sai naji sallaman wasu mata biyu,
Na dai karba sallama amma dana fahinci su Sadiya ce sai ban tsaya gaisawa dasu ba na shige ta gaban su kawai,
Suka bini da idanuwa caaaa suna kallon irin yadda na mulmule na koma gwanin ban sha,awa dani,
Dakin ta suka nufa a lokacin nai alkawarin nuna mata iyakarta nima, don daga kofan daki nake a zaune,
Yana daga ciki yana cin abinci hankalin shi kwance sai nake cewa badon naso ba yaya su Anty Hinda da yaranta ?
Sai da yai yar ajiyan zuciya yake cewa duk suna lafiya dazun na je na,fada masu cewa kin dawo ai,
Yana kai nan sai muryan Sadiya muka ji daga kofa tana cewa wai ana magana da kai, cikin wata murya kamar ta fada,
Da sauri naga ya,dago kai ya dan kalle ni tare da tsaki, yana cewa ita,wanan yaushe ta,dawo ne wai,,
Kodai yaushe ne sai ta jira idan girki yazo kanta sai bakin su gan ka don yanzu ba lokacin ta bane,
Murmushi yayi cikin mamaki yake cewa kema kin koyo naki kalar ke nan,
Banyi magana ba sai saya kofan dakin da nayi tare da,sa sakata, ta cikin dakin,
Gurin na samu daga gefen shi na zauna ina jin muryan su daga waje mama hafsi nacewa, tunda sun rufe kofa ai sai kuyi hakkuri ku tafi sai da safe ko,
Muryan ta,kamar rana,ba,dare ba rara take cewa aiko sai dai mu zuba da mutum a gidan nan don nafi mutum rashi nasiha,
Ni za,aiwa iyayyena wullakanci akan watacan wallahi kunyi kadan kuyi min rainin ayyo,
Na mika mai abin wanke hannu yawanke tare da ba shi abinda zai zuba ruwa acikin sa,
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,



Yana tsaye a bakin bakin gado yana dauko kaya daga cikin ledan shi, da ya,shigo dakina da shi,
Yana kokarin ciro kaya daga cikin ledan ban mai magana ba,sai samun guri da nayi na zauna a hannun kujera na,
Dan juyowa yayi inda nake zaune don tun da na,dawo a,wanan lokacin ne muka samu kebewa a tsakanin mu sai a wanan lokacin,
Sannu da,aiki yace min yana kokarin saka wani wando a jikin shi batare da ya jira na amsa mai ba yake ce min,
Kada faki dinga aikin da yafi karfin ki yanzu tunda kina a cikin condition kada kijawa kan ki ciwo,
Ban ce uffan ba,sai mikewan da nayi na kwashe kayan daudan da ya kwabe min a tsakar dakina,
Nafita da su har lokacin Sadiya tana zaune daga kofan ta tana dan bubuga kafan ta a hankali,
Kafin na koma dakin yafito zuwa kofan gidan ni kuma,sai na,wanke kayan daudan don ban son tara kayan wanki a,dakina,
Lokacin da nake shanya kayan ne naji muryan Sadiya a kaina tana fadin amma dai kin san cewa nice da hakkin wanke kayan nan bake ba ko,
Tankar ban ji ta ba nai banza da ita kamar badani takeyi ba,
Takara matsowa kusa da gurin da nake tsaye tana cewa, duk wani rawan kan da akeyi a kan dawowan ki ni bai rudani tunda nasan badon Allah akeyin shi ba,
Kafin na bata amsa sai muryan Ibrahim wanda ya shigo gida yayi alwala, muka ji yana cewa ke Sadiya iskan cin naki kuma har ya kawo ga wanan boyar Allah da bata ma,san kina yi ba,
Tace au ashe boyar Allah ce niko boyar ka ko ?
Gaf da ita ya karaso cikin nuna mata dan yatsa yake cewa wallahi wallahi iskanci kada ya kawo a kaina don zan iya maki mugun bungun da sai kin kwanta asibiti wallahi,
Mama tai sauri fitowa daga dakin ta tana cewa kada kafara kyale ta tai tayi tunda ita bata da marmari ,
Kayi abu ance ka barshi bata san ta barshi ba,sai ankai ga yadda ba,a son kaiwa sannan hankalinta ya kwanta,
Barta mama Wallahi ni yanzu sai nayi fata fata da ita Allah ko,
Tunda kaine Ubana ai sai ka yi mugani to aida kina da uban ne zakice mu na haka keda kike yar mace,
Haba yau ina wuta Sadiya ta saka Ibrahim nan ta hau zagi da ashar da zari sai da Ibrahim yakai ga zuba mata mari biyu masu kyau ta,samu guri ta nade kamar ta somay,
Sai can ta yanka wani iri uban ihu ta fadi kasa tana shure shure a cikin kasa,
Mama tace taufa ai kinkai ga yadda kike son akai ni wanan yarinyar masifan ki wallahi ya ishe ni

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login