Showing 204001 words to 207000 words out of 299981 words

Chapter 69 - Sarautar Mata By Makawa

04 Dec 2025

17694

nima yar adawa ce ke nan zan iya illanta yaron ke nan,
Allahu akbar kishiys kishiya duk da ta,san cewa bazan iya yiwa yaron komai ba amma,shedan ya,shiga ranta ya zugs ta kan cewa zan iya,
Tun lokacib ban kara shiga,asibiti ba,sai dai nayi girki na,aika masu dashi ko azo karban ruwan zafi ko da kuwa banji dadi sai na tashi na,dora masu an kai masu shi,

Kwanan yaron hudu da haihuwa yace ga garin ku ya tafiyan shi ya koma ga mahaliccin mu sarki Allah,
Nagama gajiya da yawan zaryan da nakeyi na,aikin da yai min yawa na gida, ni kadai don yanzu na saba da mu biyu ke bayayyan aiki,
Na watsa ruwa na dan zauna da niyar na gyara jikina riga kawai na,saka don na kasa tsaya na dan yi kwalliyan a,fuska na,
Kukan mutum da naji shigowa wiwi shine ya sa gabana faduwa lokaci guda da sauri na fito daga dakina sai Sadiya nagani tashigo da kukan ta tana kuka cikin tashin hankali,
Innalillahi wa inna alaihim rajjiun, na fadi tare da cewa may yafaru da sauri zarah ma tafito daga dakin su dauke da danta a kafadar ta ce badai yaron ya tafi ba,
Daga bayan mu mukaji muryan mama Sa,a tana cewa ya tafiyan shi an huta ai duk wanda yasa hannun shi a ciki sai yayi dariya mu gani shi,
Cikin hanzari zarah tace haba mama Sa,a don Allah kubar yaron ga ya huta dan wanan jaririn har wa zai tsonewa ido kuma Alkah ne dai baiyi shi rayayye ba kawai Allah yasa ya huta
Na amsa daga inda nake tsaye a sanyayye da amin ya Allah,
Nikan ina jin kalaman su kawai sai na juya zuwa dakina don nasan fitina suke ji ke nan,
Take barka ya koma gaisuwa sai da kanajin muryan Sadiya sama wai tana mayar da yadda,akayi,
Ina jin yadda wata mata take mata magana akan ta tausasa harshen don rashi tayi duk da,cewa yarone yarasu din,
Ajiyan zuciya na saukar cikin tausayawa yayin da nake tuna irin halin da naga yaron a,asibiti danaje,
Nima dai gani dai, don ban san yaya tawa haihuwan zata zo min ba sai kawai tausayin kaina ya kamani
Idanuwa na,suka kada sukai ja saboda tsoro da fargaban abinda kaje yadawo don nima din ai ina acikin damu tun farkon samuwar wanan cikin nawa har zuwa yanzu,
Sai wata zuciya take ce min ai lamarin damuwar ku ba,daya,bace don ke ba,wani mugun nufi kike kullawa a ran ki ba damuwa ce kawai irin ta yanayi idan yazo,
Allah ya kyauta nace a fili tare da dago jajayen idanuwa ina kallon kofan shigowa dakin nawa,
Hamzane ya shigo gidan alamar damuwa a tare dashi karara fuskan shi yanayin shi duk ya sauya cikin yan kwanakin nan,
Gurin ya samu daga gefena ya zauna bayan nai mashi sannu da zuwa naja bakina nai shiru tare da dan mayar da baya na akan masangalin kujera,
Tsayin lokacin babu wanda yai magana sai shiru da karan fankan sama da ke aiki a dakin
A hankali naji yana cewa wanan ban san yadda zamu kwashe da su ba don naji suna cewa wai sai na yanka masu ragon suna duk da yaron baida rai,
Cikin boye damuwata nake cewa idan kaga da hali ai sai ka yanka masu a,samu a rabu lafiya dasu,
Wakike tsanmanin zamu rabu lafiya dashi wa yan nan mutanen marasa mutunci kike nufi ai ba mutanen arziki bane sai anyi yadda ba,a so dasu,
Zarah ce tashigo tana cewa yaya ashe ka shigo yanzu Sa,ade ke fada min shigowan ka,
Ya amsa a sanyaye da cewa nashigo yanzu ban dade ba da shigowa ai,
Guri ta samu ta zauna tana cewa dama ina son magana da kaine ba,a gaban Umma ba akan zancen wanan maihaihuwar matar taka,
Naga sun samu Umma wai dolr ne a yanka masu ragon da kai niyar yankawa yaron tunda da sunan shi ka,saya,ragon,
Bazan yanka ba yace da karfi sai dai ayi yadda za,ayi basu da tausayi wallahi jahilan mutane ne na gaske,
Zarah tace ai bakama,san wani abin jahilci ba wai cewa,suke kashe yaron akayi wai asiri akai mashi yazo hakana tun yana ciki
Mikewa,nayi don nabar masu dakin ganin suna,shawaran su sai cewa sukayi lokaci guda zauna mana abinki aiba,wani magana bane akeyi,
Yace zai dai sayo mata nama a kasuwa taci kuma zanuwan da nai niyar bata zan iya bata su bazan fasa ba don akwai bukatan hakan,
Mamaki nayi inda ya,samo kudin sayen rago harda zannuwan da yake zance sai dai na hade a raina ina cewa kai namiji namiji kanin ajali,
Dubi iri yadda yake zuwa ya marairaice min cewa ya rasa inda zai shiga ya,samu kudi duk dan abin da nake tarawa nayi nawa rufin asirin idan ya tashi duk na kashesu a haihuwan Sadiya gurin girki da,sauran bukatun da,akeyi,
Nan dai ina sauraren rabi naji may sukace rabi kuma ina can ina tunane abina har suka,watse suka barni zaune turus gurin da,suka,samay ni, a dakin,

Ranan da aka cika sati daya da haihuwa sai ga Hamza da,kumshin nama a cikin takardan Suminti,
Dakin Sadiya wace tasha kwaliya da wani atampan da ta dinga don fita suna tasha huni tayi kwalliya tsab,
Labule ya,dan daga duk yanajin muryan mata a cikin dakin suna hira da ita a lokacin,
Yana magana ta fito daga,dakin sai yake mika mata naman duk da danye ne yasan cewa bazata yarda wani ya gyara mata ba bada yardan ta ba,
Yace cikin dakewar fuska don kada taga daman shi karbi wanan ki gyara kici tunda ba yaro,
Ya ce Zarah zata kawo maki zannuwan wanda na,samu saya suna gurin ta
Cabdijam tace tare da fadin wanan ma ai fadi ba gaskiya bane,
Jin abinda ta fadi yasa shi tsayawa ya juya yana kallon ta a cikin mamaki yake cewa may kike nufi da cabdijam,
Tace yaya zan haihu bayan yaro ya kai kwana hudu a,duniya zakace bazaka yanka mashi rago ba,
To bazan yaka ba ya bata amsa a takaice nan ta hau masifa da zage zage inda take shiga banan take fita ba ,
Sai da mama hafsi taje ta kira uwar ta,sai gata tundaga kofa take cewa ke tir da wanan hali naki na,fitina,
Yau kwanan ki nawa da,dan ki ya,mutu da har zakiyawa mutane wanan daga harshe haka,
Sati daya,da haihuwa yarinya har kin manta da abinda likita ya fada maki,
Idan kika jawa kanki hawan jini ke kika,sani don ba ruwan kowa da faduwan ki,
Maza shige daki ban son ganinki waje kuma tunda ke ba yar ido bace,
Mama ki duba,fa ki gani wai naman da,yakawo min a matsayin ragon da yai niyar yankamin,
Shige nace maki ban son abin kunya,a tsakar gida kike fadan naman suna irin haka,
Daga dakin ta murya sama wai ana,zaman sulhu da iyayyen su amma kamar a tsakar gida,akeyi,
Kai o,o Allah na gode ma da bakayi ni da irin wanan murya ba,sai kace mara kimtse nafadi mace matar aure take irin daga harshe haka babu dadin ji,
Muryan Hamza naji daga,daki yana fadi wallahi wallahi bazan yanka mata rago ba na rantse iyakar abinda zan iya yi mata ke nan nai mata,
Yai wuf yafito daga dakin ina jin sunackirancshi yana fadin nagaji ba zan dawo ba nagaji wallahi,
Macuci kawai azzalumi dan cin amana kawai sai kabiyani hakkina ranan lahira tunda hakkinane,
Allah ya kyauta na kara fadi naga yafita daga gidan nabi bayan shi da kallon haushi irin na takai,
Muna zaman zaman mu ya jawo muna fitinar duniya akan bakar jaraban shi,
Muruan Umma naji tana cewa tunda yace ba,ai yankaba baki kyaleshi ai danshine ko ba na,wani ba kwana nawa kin samu wani ba sai ai maki yadda kike so ba din,
Fita yayi daga gidan bai dawo ba har yamma ina kallon Sadiya tafito tana gyara naman da kanta tagama,dafa tashige daki da tallenta baki daya muma an sayo nama dashi muka dan watsa a miyan gida kowa ya,dan ci a gidan,
Sai dare ya,dawo dakin Umma Rabi ta fara shiga yakai wani lokaci a guri suna dan magana,wanda ba maijin mai suke fadi,
Sai washe garine Zarah take min gulma cewa dada mutumiyar ki jiya ko tayi balle dandane bataiwa kowa,ba tashige daki ta cinye abinta tas
Murmushi nayi nace ai yafi mata da ta rasa, baki daya fa,gara,data hakkura taci abinta,
Magana irin na shirka sadiya ke ta,sakewa akan mutuwan dan jaririn ta wai an kashe mata shi don bakin ciki kada agan shi a gidan ,
Habaici wanda zai sa mutum ya tanka mata,shi takan tayi kullun har da cewa wallahi mutum ya,bari ya gani yadda ya,sata kuka shima mai shi sai yayi,
Wata rana Hamza yana kwance daki tunda safe tafito take cewa wai wa ya,dauke mata, roban wanka inda ta,aje shi wallahi mutum komai tsafin shi sai dai ya barta inda ya ganta kawai
Batan fitowan shi daga daki ba sai jin muryan shi tayi yana cewa ke Sadiya jinan wanan zancen wallahi ya,isheni haka don bazan yarda da wanan mugu halin naki ba haka
Kullun mutum shi dai ke nan anyi mashi dai anyi tau yau ki fito ki fada muna,wanda yai maki a huta haba keni wallahi wanan halin bai min ba agidan nan ban son nakarajin zancen nan in har kina son mu zauna lafiya wallahi,



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABUIDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,


Sati biyu da haihuwan Sadiya nawayi gari da na kudu sai dai ban yarda kowa ya,fahinci halin da nake ciki ba a,gidan,
Badon komai ba,sai don sani halin yan gidn mu danayi saboda inajin irin yadda sukewa,Sadiya,go wai raki gareta amma yanzu tafi kowa surutu,
Yanayin danake ji haka na daure nai masu girki a tsatsaye batare da,sun fahince ni ba,
Wata classmate dina da mukai karatun health tare na kira tazo ta dubani batare da kowa ya fahinta ba,
Take ce min zuwa azahar zan iya haihuwa insha Allah nan taimin duk abinda ya dace tace idan time din yayi zata dawo ta duba stage din da nake,
Saya kofan dakina nayi ina ta faman nukurkusa ni kadai a cikin daki
Hamza ya shigo dakin a lokacin na,samu abin ya,dan lafa min sai gumin da na hada abinka,ga wanda bai san kai ba,
Kallon mamaki yake min yana cewa wanan zufan fa da kika hada haka kamar wace ke cikin oven,
Murmushi nai mashi kawai nace yanayi ne kawai daga barci nake shiyasa nai zufa haka,
Fita yayi daga dakin yana cewa bari ya sayo clean ya wanke wasu kaya nashi saboda yaga nagaji da yawa,
Barci ya dan dauke ni har ya dawo dakin ya kwashi kayan da zai wanke zuwa waje,ya fara wankin shi,
A cikin dan barcin da ya,fisgeni na rika ji sama sama kamar ana yanka min marana da wani irin guduma
Da,sauri na bude idanuwana tare da kokarin mikewa,saboda irin yadda nakejin abin yana min ba,sassauci a cikin shi
Duk yadda naso na mike na kasa hakan gashi a,kwai fanka,a,dakin amma,sai kice ba,iska cikin dakin gaba daya,
Hankalina,gaba,daya ya,daga tausayin kaina ya kamani sai naji kawai a kira min mama hafsi idan tana gida,
A raina nace idan hamza ya dawo sayen clean din da ya tafi sai na,fada mai yaiwa mama,magana tashigo guri na,
Sai dai kassh i a daga idanuwa na,sai naga har ya kwashi kayan wankin shi ashe ko yafita,dan bar cin da nayi,
Tausayin kaina ya kamani na dafe gefen hannun kujerana da karfin Allah,
Na fahinci baby na gaf da fitowa don haka,a wahalce nakara rugumar kujerar da karfin Allah,
Take duk illahirin jikina naji ya dauki rawa a lokaci guda na,fara dan nisawa,da dan karfi har naji abin ya,zo gap da fitowa,
Gabaki daya naji na wani sake kamar rayuwa na zai cire a lokaci daya kamin kiftawa da,bisimillah sai naji gabadaya abinda ke a cikin cikina na sullubo shi waje gaba daya har uwar tafiyan ,
Take kukan jarirai ya kaure gidan duk inda kake zaka iya jin kukan yar jaririyar dake kwance a kasan daki tana tsala ihu,
Idanuwana na lumshe a lokaci guda don ji nake kamar wani abune mai nauyi aka cire daga part din jikina,
A guje suka,kwaso zuwa dakina ina zaune gurfane a gefen kushin dina
Suna bude labulen dakin sukayi arba da yarinyar tana ta tsala ihu a tsakar daki ni kuma ina daga gefe daya,
Baki suka hada xarah da Asmau gurin cewa wallahi Umma Aisha ta haihu,
Kafin haka har mama dake dakin ta tafito tafado dakin nawa Hamza ya na daga kofa tsaye ya daga labulen dakin yana mamaki sai da mama tai mashi magana ya sake labulen,
Reza inji mama cikin nune na nuna mata inda suke ta dauko sabon reza ta yake cibin jaririyar dashi ta dauko zani dake saman gado ta nade yarinyar a cikin shi,
Ni dai ina zaune a gurin da nake tun farko kaina a duke sai murdan baki nake, zufa na dan tsiyayo min,
Daga kofa nake jin muryoyin yan gidan mu suna nuna farin cikin su da haihuwa na,
Ban san wa yakira mutanen gidan mu sai muryan Atika na tsinkayo daga waje itama tana cewa ikon Allah da zunfa Aina tashigo take ce min nan ta ke gurin Aisha suna kulla kankara, da ita, amma batace muna bata da lafiya ba,
Zarah tace itace fa tai muna girkin safe da rana gashi ma bamu ko ci ba tukun,
Nan gida ya kaure da,farin cikin samun karuwan da akayi har akaci aka sude aka gyara min daki banga Sadiya ba,
Saida Atika da Mama Saude zasu koma gida bayan sun min wanka suke tambayan halan bata nan ne tasan halin mama saude sarai sai ta dan fito daga daki fuskanta ba yabo ba fallasa a cikin shi take cewa,
Ina nan mama sannun ku da shigowa dama na bari har a gyara guri ne in ta kimtsa sai na shigo,
Haba kubar irin wanan rayuwan mana dan uwanka ya sauka lafiya ai kazo kai mashi barka dai ko,
Zarah tace ranan da kika haihu da tsohon cikin ta wallahi duk daren nan da ita ake a kan ki har safe,
Babu ruwanki don ni ra,ayinane hakan ko zaki sani dole ne,
Don Allah matsa can in kina gyara halin ki ki gyara kinji, zarah ta bata amsa da hakan,
In ban gyara ba,ai sai kizo ki gyara min kaji min yar raini senses kawai kidai iya da naki kishiyoyin tukun kafin ki shiga na,wasu,
Ke dai kika,sani mutum bai iya boye mugun halinshi ko yaushe sai ya zubar da hali kowa yagani,
Ke zarah wallahi kada ki fada min maganan banza wallahi yanzu ajimu a gidan nan
Ajimu mana wake tsoron ajiku dashi ko waye bai san halinki ba da zaki wani budawa mutane ido
Wai may ye haka kukewa mutane Hamza da yashigo gida dauke da leda da sabulu da Omo da,aka bukaci ya kawo yake magana a cikin daka tsawa,
Shiru su kayi suna kallon shi don kowa tana tsoron shi sabboda yafisu zafin rai sun sani yanzu za,ajisu in basuyi shiru ba,

****** ********* ******
Dakina ya dauki kamshin turaren wuta lokaci daya yana bada kamshi da kuma karnin jego irin na,dankin haihuwa,
Ina zaune gefe guda can kuryan daki mamana Rahana ta,shirya baby tsab a cikin tufafin yan mata masu kyau da tazo dasu,
Mama ta,dago kai tana cewa kin koga yarinyar Aisha wallahi gata kamar hamza yai kaki,
Murmushi nayi kawai tare da dan dukar da kaina gefe daya, sai mama ta mike ta nufoni da yarinyar dake nade a cikin showel,
Miko min tayi tana cewa karbarta ki gani mana don nasan baki dauketa ba tun dazu,
Nace cikin jin kunya mama barta kawai ai zan dauke ta,
Miko min tayi batare da nai magana,ba na karbi yarinyar sai mama tafita dakin dauke da,wani robs a hannun ta,
A hankali cikin natsuwa nakai dubana ga yar jaririyar dake nade a cikin showel, na,dan bude showel din tare da,sauke ajiyan zuciya nai wa Allah godiya da baiwan wanan yarinyar da yai min,
Idanuwan ta,a rufe amma ta dan sanya yatsu a bakin ta tana tsotso na rungumay ta tsam a jikina ina karanto mata adduan neman tsari daga,sherin shedan da shedanu tare da neman tsari daga,zina sata, ko wani mugun abinki,
Mama ta dawo dakin tana cewa bari na,shiga gurin Fatima, nafito (Ummi) nace a,sanyaye tau mama,
Fitan ta yai daidai da,shigowan Hamza da yar leda a hannun shi yake sallama,
Tsayawa yayi yana kare muna kallo ni da yarinyar cikin nuna,so da kauna a tsakanin mu,
A hankali ya tako zuwa inda muke zaune yana cewa mama ta tafine nace tashiga gurin Ummi ne,
Dan tsugunawa yayi gaban mu yana cewa dabino nake son bata da ruwan zamzam,gashi kuma kamar tana barci ko
Nace ai kila zata karba tare da kokarin miko mashi yarinyar yakarbeta tare da mikewa tsaye ya nufi gurin kujera ya zauna,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login