Showing 207001 words to 210000 words out of 299981 words
Kiran Sallah yafara mata a kunne sanan ya dauki dan lokaci yana mata addu,a tare da dan daga gefen ta na,dama yai mata adddua yadawo gefen hagu yai mata sai naga ya bude gurin al,auranta yai addua sai ya tauna dabino ya hada bakin shi da nata ya bata tare da,diga mata ruwam zamzam din sai kuwa yarinya ta dan shiga lashe baki cikin yamutse fuska,
Ya sauke numfashi tare da dago kanshi yana kallon na yake cewa Allah ya raya muna ita tafarkin addinin musulunci,
A sanyaye cikin kunya da murya mai taushi na amsa da amin a hankali batare da,wani yaji may nace ba,
Yana mika min ita yake cewa lafiya dai kike ko na amsa still a sanyaye da lafiya ta kalau yace masha Allah,
Umma ranan har dakina take tana min barka da,arziki tare da daukan baby zuwa wani dan lokaci tabar dakin, fuskan ta dauke da annuri,
Bayan komai ya lafane zuwa dare yan barka,suka,fara shigowa kamar yadda al,ada yake a kasar hausa,
Washegari baby ta jawo min yan uwan mahaifinta a dakina don zarah da yan uwanta a dakina suka tare don nuna kaunar su ga diyan dan uwan su,
Sai hira ake ana,dariya cikin raha da,daga murya yi suke don su karawa Sadiya da ta kunkumay a daki haushi,
Rana yayi amma ba alamar Sadiya gurin dora girki har saida rana yakai take ba tafito ba
Hamza ya,shigo gidan gani ba a,dora girki ba sai ya,samay ta a,daki yake cewa, lafiya bazakiwa yar uwar ki dafuwa bane ko yaya,
Wani irin kallon ta watso mai daga inda take kwance tace wacece yar uwa na,
Wacece abokiyar zaman ki da kika haihu tai maki girki ta dora maki ruwan zafi da sauran su,
Ai ban sata ba ba inda zan fita da jegona a jiki na halaka kaina don gudun bacin ran ku kai da ita,
Oho ashe hakane ita da tsohon cikin ta take maki aiki har kikai karfe haka yau yazo akanta shine zaki nuna halinku na yan duniya ko,?
Cikin wani tsiwa da nuna isa da gadara tace bazan yi banace ko za,a sani yi dole ne,
Da kai ya,fara amsa mata yana cewa Ok yayi ba damuwa
Ya juya zaibar dakin take cewa haka kawai da jegona zakace wai nawani dafawa wata matar ka can abinci kada taci abinci don Allah,
Murmushi yayi gami da cewa Ok yayi hakan ba matsala ai sai ya fita daga dakin a kofa ya tsaya yana kiran Asmau,
Asmau tafito tana kokatin daura dankwali a kanta yace mata ku fito kuyi muna girkin da za,aci,
Mama dake daga gurin girkin namu tana dora ruwa take cewa kubarshi kawai gashi zan dora ai,
Daga ranan mama hafsi ce mai mai muna girki da dora ruwan zafin wankana ni da baby,
Sadiya,sai wani isa da toroko takeyi akan bazatai girki ba aci don itama jego takeyi,
Da yamma ta shiga gyaran dakin ta tare da yin sauri tai wanka ta saka tufafi masu kyau a jikin ta,
****** ********* ******
Ina zaune da abinci a gabana ina ci duk da bakina bana jin dadin shi don jego yafara aikin shi saboda yadda nake jin jikina gabobina sun fara tsami don wahalar haihuwa da mace keyi,
Mama Hafsi tashigo dakin dauke da,wani kwanon silver mai marfi ta girke a gabana tana fadin na bude na diba naci sai na koshi, don ki na girkashi,
Ta samu guri a,saman kujera ta zauna tare da daukan baby dake kwance a,saman gado tana dan dubata a hankali,
Take ce min sai masu barka sun dauke kafa zan dauraye ta,don rage mata kasala saboda ku samu barci issashe da,dare,
Idan ba hakaba sai kafa ya,dauke kiga yaro yaki barci saboda tsamin jiki shiyasa ba,a son yawan daukan nan da,akewa jariri da rana,saboda jikin su ba karfi yana,basu reaction sosai,
Kawai daga dakina da muke da mama muna hira mukaji muryan Sadiya tana fadin wallahi baka isa,
Sai dai yau ayi duk abinda za,ayi a gidan nan amma dole ne ka kwana a dakina, don nima dana haihu ai a,dakinta kake kwana,
Hamza yace kin manta may kikacd ne dazun akan girki cewa fa kikayi jego kikeyi bazaki girkawa kowa abinci ba da jegon ki a jikin ki,
Shine nikuma kike son yaudarata na,shiga dakin mai jego na kwana na,sabawa Allah da,al,ada ko,
Shiru tayi tare da cewa Owoo tanan kake ganin kafito min ko don nace bazan yiwa matar ka,girki taci ba ko?
Macuci aidama,akan wanan figagar matar taka ka saba cin amana ta,
Ni zaka gwadawa an haifa ma,diya mace ko kuwa ni ban haifi da namiji a gidan bane kafin mace,?
Ya juyo da karfi ranshi a bace idanuwan shi sun kada a lokaci guda sunyi jawur ya nunata da hannu yace ina da namijin naki yake ?
Ni a gurina da namiji da mace duk daya suke a gareni fatana Allah yasawa yata albaka yasa rayayyiya ce dazamu more mata,
Ni zakaiwa gorin dana yamutu yace anyi maki wayakashe yaron bake ba saboda bakin halin ki,
Sai kawai tasa ihu da kuka tana shatar majina tana cewa wai yai mata cin mutunci dagori akan dan ta ya mutu,
Umma tafito daga dakinta tana cewa kai haba yaran nan wai may nene haka don Allah,
Kullun kuke nan a gidan nan ba,ajin alherin ku sai da sheri ni wanan hali naku ya isheni wallahi,
Amma Umma kina jin abinda yake fada min don kawai naki yin girki da jegona a jiki zaizo yana fada min bakar magana da gori akan yaro bai tsaya,ba,
Juyawa gurin hamza Umma tayi tana cewa, yanzu kai akan diyar da aka haifa maka har kake gayawa matarka bakar magana da gori,
Umma don Allah ki fitar da bakinki akan wanan zancen don wanan karon bazan dauki rainin hankalin da,Sadiya take min ba kina gani kice wai nayi hakkuri da ita ,
Daga haka yabar gidan fuuu Umma tana kiran shi ya,fice daga gidan,
Gurin danake zaune nayi shiru ina,sauraren abindake wakana dagani har ita takece min kada wanan zancen ya bata maki rai kedai rugumi diyar ki da macen da na miji duk Allah ke badasu, a inda yaso kuma shi yasan dalilin baka irin jinsim daya keson ka dashi,
Murmushi nai mata, tare da,cewa, mama ni kan Alhamdullahi nagode da baiwar da yai min,
Sai da mamata tabbatar da,cewa ban sa, zancen Sadiya araina ba tabar dakin don zuwa ta kimtso dakin ta saboda tare muke kwana da ita a,dakina,
Itace ta ce yan uwana su huta don zatai min duk abinda yadace aiwa yaro sai dai kawai azo ai min wanka inda,bukatar hakan,
****** ********* ******
Ga Dare ya raba amma sam na kasa barci don ma babu ko alamar barcin a idona duk da yin barcin ake bukata,agareni don samun hutu,
Ajiyan zuciya na,sauke tare da dan lalabo yar diyata da take kwance a kusa dani,
Idanuwana na rutse tare da tuno kalaman Sadiya akan yar baby na,dana haifa,
Ba,Sadiya ba harda Umma sai yanzu na,fahinci rashin kara shigowar ta,gurin mu don diba lafiyan mu,
Ashe wanan dalilin nace na haifi diya mace kecin zuciyar Umma taki kulani da yar dana haifa
Maynene illar haihuwar diya,mace da,suke gani da macen da na miji ai duk Allah ke bada su yadda yaso,
Shekara kusan hudu da aure ban samu haihuwa, ba,anata min gori da,shagube akan rashi haihuea,
Yanzu gashi Allah ya tausaya min ya bani mai makon a tayani farin ciki samun karuwan da nayi
Shine kuma don hassada aka kirkiro min wani sabon sheri wai diya mace na,haifa,
Nikan gaskiya,alhamdullahi nagodewa,Allah don ina jin so yata har cikin kasan raina,
Tsoro na daya shine kada Umma ta cusawa uban ta kin ta a,ranshi don tana diya mace,
Idanuwana a runtse suke ina mai sauke numfashi a hankali, na furta,a hankali Allah ka taimake ni,
Sai naji muryan mama tana amsa min da cewa Amin Aisha,
Tsayin lokaci babu wanda yai magana a cikin ni da ita sai zuwa can take cewa,
Kin sa zancen wanan shu,umar yarinyar a ranki ko wanan dakike gani minshon ce bat da musulmi,,
Yanayin maganar mama ya,nuna min a cikin bacin rai tai min magana,
Tace kada ki fara ta fahinci maganar ta yayi tasiri a ranki don dama haka take son gani duk ta yamutsa maku farincikin ku,
Kukan da yar jaririyar ta tsalane yasa mu katse maganar mu inda mama ta mike zaune ta kama yarinyar tabata ruwa take ce min na mike na bata nono a zaune kada na yarda na bata nono a kwance don haka yana da illa wanda iyayye basu ganewa sai yaro ya girma illar yake baiyyana masa,
Namike kamar yadda mama ta umurceni nayi din nabawa yarinyar nono sai dai bata iya kamawa ba, tadan ja kadan sai ta sake taci gaba,da barcin ta,,
Tsam na kankamay diya na a cikin jikina ina mai kura mata ido yarinyar tana barcin ta hankali a kwance, cikin koshin lafiya, na,sauke ajiyan zuciya ina maijin kunar zuciya da irin halin rayuwar da,ake shirin bullo min dashi a gidan,
Jin munyi shiru mama,da dan barci yafara daukata ta farka take cewa idan tayi barcine miko ta nan ki kwanta ki huta kin ji,
Naji dadin yadda mama take min kamar uwata da ta,haifeni
Bayan na kwanta kafin barci ya daukeni nake cewa a raina may yasa wai Umma take son kuntatamin a,rayuwanta
May nai mata har take son kawo kiyayyan da take min ga yar jikanta jinin ta, yarinyar da kwatakwata kwanan ta biyu a duniya,
Wanan ai zaluncine kawai irin na Umma data saba yi na ba gaira ba dalilin a cikin iyalin ta,.
A hankali naji hawaye ya soma dan zubomin a fuska nasa hannuna na toshe bakina don gudun kada mama taji sheshekar kukana,
Washe gari bayan nai wanka na kimtsa cikin dan kwalliya kamar yadda ko wata maijego take dan,dandassa kwaliya saboda ta kara burge mutane,
Hindatu ce tazo da yan uwanta tare da manyan ledoji a hannun su,
Ba komai acikin sa sai abubuwan amfani irin na maven da ta haihu daga na ci da sha har namfanin jiki nawa dana baby,
Nan yan uwanta suka barmu don mu dan tatauna da ita kamar yadda muka saba,
Ganin yadda nai shiru cikin damuwa bayan tafiyan yan uwan ta yasa ta dan rage murya tana cewa,
Aisha akwai matsala don yanayin fuskanki ya nuna min da,akwai damuwa tare dake,
Murmushi na dan kakaro a fuskana don kada ta fahinci komai a,tare dani,
Tace look Aisha ban tsanmani zaki iya,boye min sirin ki ba amma tunda bakya,son in sani shike nan,
Idanuwana na watso mata sun kara girma saboda hanlin da nake ciki sun koma kamar hasken kwai, saboda basu saba canza launi ba,
Nace ni Anty ban san may na kashe wa Umma ba aduniyan nan ,
Ko auren dan ta danayi ne bata so ba,tun farko bata kauna hada zuria dani,
Kuka nafara inda cikin kukan nake labarta mata zancen da Hamza su kayi da Sadiya da kuma amsar da Umma ta bashi,
Yadda zancen Umma yake nufin cewa yana kokarin wullakanta matar da take mai haihuwan diya maza akan mai haihuwar diya mata,
Shiru tayi har na kare magana ta tana saurare da nazarin abinda nake fada mata,
Al,ajabi da mamaki ne suka hanata magana har ta kasa furta komai,
Hmm tace tare da jan tsaki tana cewa amma wanan matar babban jahilace wallahi,
Yanzu saboda tsabar kiyayya har take son ta saka yar jikan ta a ciki,
Wallahi zanga hamza yaudin nan naja masa kunne tare da kara cusa mai son yar shi a rai tun kafin munafukar uwar nan nashi ta umurce shi kan dole sai ya,aiwatar da,abinda ba,daidai ba,
Wallahi Aisha,sai yanzu nafara fahintar duk itace mai tillasta shi yin wasu abubuwa yake mata don biyayya,
Don ma wanan wagarar kishiyar taki batada kimtsi aida abin yafi nan sai reshe ya juye da mujiya ko ita bata bari ba,
Haka kawai mata mara mutunci kiyi kokarin tozarta kyautar Allah kan son zuciya,
Wallahi intace tai haka,sai Allah ya tambaye ta don Allah baya jin kan wanda baya jinkan mutane,
Shiru nayi ina,saurarenta tana cewa yau din nan da dare zan sa man ya kira hamza muyi mashi bayanin komai yadda zai fahinta wallahi ko,
Duk tsiyanta sai ta barshi da yarshi wallahi muguwar mata kawai ni wallahi dama bani son ta don rashin kaunar ki da batayi don banga abinda kika tsare mata ba,
In ba,aure ikon Allah ba ai ke ba matar hamza bace wallahi don shima yasan kifi karfin shi sa,a dai Allah ya bashi,
Amma mu zuba da ita tagani tasan tayi da maihi wallahi,
Da irin wanan maganganun taci gaba da kwantar min da hankali tana bani baki har naji kwarin gwiwa komai ya fita min a zuciya irin kuncin da nake ji da farko,
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEEENABUIDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,
Alhsmdullahi don yanzu na,warware saboda shawaran hindu yai tasiri a zuciya ta sosai,
Na kuma fahinci kamar yadda tace min zasu yiwa hamza nasiha din sunyi don gaba daya,wani irin nuna kulawan shi a,kaina da yar jaririya yake yi,
Wanan abin a zahiri ya tayar wa,Sadiya da Umma dake kokarin boye halinta rai,
Hindatu da mijin ts duk sune silan dadin ran da nake a ciki don sunyi namijin kokari gurin gurin fahintar da Hamza yadda zai dinga kawar da,kai ga,wasu miyagun shawara da,Umma ke dora,shi akai,
Don a yadda ya,fada masu wasu abubuwan dole yake sashi yin su don ya,samu su rabu lafiya da ita,
Mansir yake ce mai kada kayi gigin da ka bari yarinyar nan Aisha ta subbuce a hannunka don irin su Aisha abin alfa,arine zama dasu nan gaba kai zaki kowa farinci kansan,cewar ka da ita,
Duk shirin da Hamza yakeyi na suna idon Umma da Sadiya yana a kai sai yazama min na samu kishiyoyi guda biyu lokaci daya, agida da guda,
Basu fahinci duk wani shirin da yakeyi ba,saboda sabon takon da ya,dauko masu a gidan Mansur ake shirin komai,
Saura kwana biyu suna iyayyena suka zo daga burkusuma, da abin arzikin su a gidan mamana Rahana suka sauka su biyar mata maza biyu,
Ganin sun shigo inda nake hannu salin alin Umma ta fara sake magana,bayan fitan su wai dama fashi bakauye bai san kunya ba,
An kwaso jiki anzo wa mutane haka akara masu nauyi da wahala ita bazata yarda a sa danta cikin wahala,ba don ko abincin da za,a basu ai aikine a gurin su,
Mamace ta katse tada cewa sun fada maki anan zasu sauka dakike irin wanan magana haka bakon kafa annabinka,
Karuwa kika,samu suka samu suma sunzo taya yar,su farin cikine ne fa saboda nisa kikaga sunzo da guri haka,
Don Allah yaya ki kama bakikin don irin wanan magana,bai kamata,ace anajin shi a gurinki ba,
Zarah dake zaune gefe tana ba,dan ta nono tace ni wallahi ban san sanda umma ta koma haka ba
Haba ace matar danka ta zama abin takaicin ka itace abin yiwa shagube shiyasa mutane suka barki da diyan ki ai kowa yazo neman su sai ace baki da dadi gurin sarakai,
Haba aikuwa Umma tai kanta da fitina da zagi wai ta raina ta,shine har take fada mata magana son ran ta,
Umma ni gaskiya nake fada maki don haka baidace ba saida ibirahim yashigo yanaji shima yace,
Kai haba haba Umma wallahi ni wanan halin yasa sam yanzu ban son zama gida, shiya kashe maganan,
Maganan har Hamza saida yaji ta,amma saboda halin shi bai nuna a,fili ranshi ya baci ba yai shiru kawai,
Ranan suna yarinya taci suna Hauwa,u sunan gwagon su Hamza wace ta rasu uwar su daya da mahaifin su,
Ta rasu bayan rasuwan mahaifin su itama tana da zumunci sosai da hamza yake yaro ance tai kokari dashi sosai,
Umma tai masifan saka sunan yar uwar mahaifin shi dayayi take cewa don baisan zafinta ba yasa shi saka,sunan wata ga,ta,a,gida,
Yace Umma idan na,saka sunan ki duk wanda ya kirata da,sunan ki zan dinga jin zafi a,raina ne shiya,sa amma kiyi hakkuri ai yanzu akafara,
Da,sauri tace may ne akafara yanzu haihuwan diya matan ko may fa ?
Yace da macen da namiji duk shiryuwan Allah muke nema a,gare su
Shiru tayi cikin jin haushi da takaicin shi don tana ganin bai san ciwon kan shi bane,
Da,safe na,saka,wani dinkin atamfa corde voire mai ruwan makuba, a jikina,
Ina zaune dakina ni kadai ce a cikin dakin kafin yan uwana,su shigo sai ga mama tashigo daukan kwanonin da nai amfani dasu da dare,
Cikin murmushi da nuna jin dadin ta take ce min kai "ya ta,wallahi kinyi kyau don jego ya karbe ki sosai ,
Ba kamar kishiyar ki da masifa da raki ya hanata tsayawa tasha ruwan zafi yadda ya kamata,
Dama ai shi jego na kwana hudune idan ka kuskure wanka kwana hudu zuwa biyar da haihuwa duk sai kika mace ta