Showing 21001 words to 24000 words out of 299981 words
gani ,
Inda yake cewa yai hakane don ya gwadawa Saude da yar ta cewa idan har bai da iko da isa akan yar cikin shi,
To ga diyan bayin Allah sunyi mashi biyayya yadda ya kamata,
Sun yake zancen cewa zasu ba uwar Aisha dan lokaci yadda zasu yi dan shiri a tsakanin su,
Hamza wanda abin duniya ya kaiwa,ko ina, a rayuwan shi yarasa yadda zai yi da,rashi,
Aisha yar karamar yarinya kuma kazama dabata ko san yadda mata,suke gyara,ba,ahine wai yau take a matsayin matar shi,
Ya dan gyara juyawa daga saman yar mokaddan katifar da yake a,kwance sama yana mai nazarin siffan Aishan yarinyar da koda yaushe a cikin hijjab take a dunkule baka taba gane kalar surar ta,
Washe gari yan abokan shi da suke zama a,shago suka,dasa mashi sheri da,wasa irin ta angwanne,
Umma Rabi ce sukai ta tausan shi har ya hakkura da zancen auren Aishan don gudun kada ya budawa malam Mudi kasa a ido,
Bayan sati, guda da,daurin auren su ya na zaune a bakin shagon shi suke jin ana yekuwar cewa mai gari yana neman duk wani wanda yasan cewa shi manomi ne don akwai bayani akan gagarumin wasan gwajin amfanin gona da za,ayi, a garin,
Wanda manya mayan baki zasu shigo daga sassan kasan nan ta ko ina don kallon wanan amfanin gonan na manoman kasar,,
Jin wanan shelan yasa mutane tururuwan zuwa kofan gida sarki don jin karin bayani daga bakin shi,
Abinda yai sanadin jefa zukatan mutane da dama a cikin nazarin shiga wanan gasar ,
Daga ciki harda Hamza cikin masu nazari yadda zasu kokarta,su kawo nasu amfanin gonan a,wajen gwajin mai taken suna AGRIC SHOW,
Daga dangin Hatsi, kayan labbu, dabbobi kayan ruwa da,sauran su,
A lokaci guda duk gari ya rude kowani gida zance a buguda akeyi kawai,
A wanan lokacin kuma uwa da diya a gidan malam Mudi suna a cikin matsi da,tsangwaman matan gidan,
Duk da,su suka nuna,basu son auren Hamza din da kansu amma,suna ta,sake magana a tsakar gida,
Har da,atika wace take bayan Saude da,yar ta,don muna funci kawai don son halin kishi,
Hakan yasa,a koda yaushe mutum ya shigo gidan zai samu Fatima daki da,yaran ta,suna yar hiran su ,
Aisha wace zuwa yanzu abin duniya ya kaiwa ko ina tana,mamakin irin yadda tai wanan subul da,baka har tace wa Baba ayi wanan hadin auren da ita,
Alokacin tausayin Baba ya,raja,a a kan ta har yakaita ga furta,wanan zancen a gaban shi,
Umma Rabi ta,umarci Hamza da ya hada yan abubuwan bukatan rayuwa,a,kaiwa, Aisha a gidan su,
Hamza wanda har yanzu ganin zancen yake kaman a mafarki don har yanzu ya kasa gaskanta al,amarin cewa wai Aisha a matsayin matar shi take,
Sabulun wanka Sabulun wanki omo manshafawa dasauran
Sune aka hada a cikin wani leda akabawa Halima sister din Hamza din takaiwa Ummi Fatima, kayan ace inji Hamza din,
Tun shigowar yarinya gidan da kaya su Atika da mama Saude suka shiga ya da,magana a tsakar gida, da cewa,
Iyakar ke nan tsiya tsiya ankawo wa Amarya kayan tausa, ,
Wanan gayar tsiyar akai shi can gurin mubukata irin sa,amma ba nan ba dai,
Atika tace ai adaiyi mugani uwa,kwance diya zaune, duk a kare a tagumay,
Daga cikin daki Kubura ta,dago labule don taga abinda ake zance akai yayin da,tai arba da kaunar Hamza na kokarin shiga,dakin Ummi Fatima da dan leda yellow mai layi layin baki, dan kayan da baikai rabin leda ba a cikin sa,
Tace tsiyatsiya ke nan dama a can ya,dace da akai ba nan ba,
Ni kan ai nagodewa Allah da ya raba ni da gayar tsiya,
Fatima ta tari yarinyar da mutunci tare da godiya,akai akai da haba haba da ganin ta a cikin mutunci inda tabawa yarinyar naira,Ashirin tace tukwaici ne,
Kaf zance abin da ya,faru a gidan malam Mudi ba abinda Halima ta rage a bakin ta,
Gaba daya ta tsiyayewa Umma Rabi shi a kunnuwan ta kaf,
Abinda yai matukar bata mata rai sosai yadda ake cewa wai suna yi,
Saukin ta,guda,shine yadda, Ummi Fatima ya karbi yarinyar a,cikin mutuntawa,
Hamza yana,tsaye daga bayan Umma har yarinyar ta,gama bada labarin irin cin fuskan da akai masu a gidan,,
Muryan shi Umma taji daga bayan ta ya fadin Umma kada ki damu da zancen su don su sai kiji fiye da haka daga gare su, ma, ai,
Yafita zuciyar shi na mai kuna yadda yake jin zafin irin wanan gorin da Saude da,yar ta,har ma,da,abokiyar zaman ta dayan,
****** ********** ******
Duk abinda Aisha ke yi hankali ta yanzu ya koma ga zancen Baba, da yake mata a ranan daurin auren ta,
Ta dan gyara kwanciyar ta a hankali tare da dan lumshe idanuwan ta tana mai dan hade miyau masu daci,
Ta dan kara gyara lumshe idanuwan ta tana mai sauke ajiyar zuciya a hankali,
Ki kwantar da hankalinki Aisha wanan aure naki Allah yai mashi albarka Allah yasa muce gwamma da akayi,
Saudayawa alheri kancin ma,bawan shi ta hanyar da bai zata ba, arayuwan shi,
In har Umma Rabi da danta zasu rike min ke amna Aisha sai ince zaman ki a,gidan su yafi min zama a gidan nan,
Zaman da kike a gidan nan a cikin wahala, tsangwama da shagube,
Sun manta da cewa Allah ne bai nufi ki fito daga cikin tsatson su ba kika fito a can wani gurin na daban,
Wanan hattaran da tsangwaman da suke maki a gidan nan kiris ya rage hawan jini ya kamani a kan hakan,
A hankali Aisha tafara dan kuka a hankali don kada mutanen gida suji muryan ta,
Washe gari sun tashi da,safe ba fashi daga duk wani aikin da Aisha din ta,saba yi a gidan da,safe,
Da ita akai komai amma sai Umma saude taki saka,wa Aisha dan kunun kokon da take saka ma ko wani yaro a gidan da,dan kosai din su kwara biyu a matsayin abin karyawan su,
Yau Saude ta hana wa Aisha wanan kosai din haka abincin rana ma again,
Malam Ummi ta sama da zancen take tambayan shi ko shine ya hana a sakawa Aisha abin karyawa a gidan shi,
Kafin ya ba da amsa buty suka ga mama Saude wace take kamar a jirace a bayan su ta,shigo tana cewa,
Nice nan na hana mata ba wai wani yasani yin hakan ba,
Ai aure take yanzu don haka sai taje can gidan mijin nata a saka mata shida keda alhakin ciyar da ita yanzu, don duk wani nauyi nata ya rataya a kanshi yanzu,
Malam Mudi wanda kr reacting kamar wani shanyaye sai cewa yayi ai zata tafi gidan mijin nata kowa ma ya huta ,
Ummi bata samu bakin magana ba,sai kallon yadda Mama Saude ke faman budan baki tana vin mutunci wa mijin nasu,
Ummi ce ta katse su da cewa Aisha zata koma gurin mamanta Rahana har zuwa lokacin da zata tare a gidan mijin ta tunda abinci da ake bani ni kaina ba isa na yakeyi ba balle nace zan dinga ci da ita,
Daga fadar haka tabar daki inda ta samu yar ta Aisha take fada mata cewa ta,shirya zuwa gidan maman ta Rahans,
Da sauri Aisha ta dago kai tana kallon mahaifiyar nata don son tagano ko anyi wani abu a tsakani,
Amma sai bata iya hango komai ba a fuskan uwar nata,don haka ta dan mike daga zaune ga yunwa,da ya damay ta a,rayuwanta,,
Yan tsunmakaranta ta hada a cikin wani bakin leda bag mai giwa,
Ta,dawo daga kofan daki ta zauna a rakube tana kallon yadda yau zata tafi tabar Ummin ta, a cikin wanan yanayin zaman hakuri da tsangwama da take gani daga kishiyoyin ta ga,goyon tagwaye a,tare da ita ga,wahalhalun duniya iri iri a gidan,
Bayan Ummi ta goya hassan ta umurci Aisha da tagoya hussai din taku ma umurce ta da ta je suyi sallama da su mama saude da,Atika,
Ba,wani amsan da ta samu sai dan tabar bakin da,suke suna cewa umma ta gaida Aissha yau kan zamu sha iskan rahama gida ba yar agola a cikin sa, yar gola kiwon Allah ya isa,
Sai suka tafa tare da,shewa suna masu rangada guda,
Akarata can inda talauci ya yanke cibi mugani,
Tafiya suke duk zukatan su a,cakushe saboda bacin rai don har Ummi din, yau ji take tankar tabar gidan malam Mudi din gaba daya,
Suna jin shewan mutanen gidan a lokacin da suka fita suba cewa yau yar agwai an tafi,
Atika tace yau kin muna maganin wanan shigiyar yarinyan mai kama da mayya kawai,
Duk Ummi tana jin su amma ta kyalesu kawai suka,sa kai zuwa gidan Mama Rahana yar uwar ta,
****** ********** ******
Anty Rahaba ta gama komai na yinin ranan ta na,zaune daki ita da,yaran gidan suna kallo Ummi ta,shigo da,sallama,
Mamakin ganin ta su keyi a lokacin saboda ba,al,adanta,bane fitowa uguwa da,dare, irin haka,
Daya bayan daya yaran suka watse daga don bawa yan uwan guri saboda su sirint a tsakanin su,
Bayan gaisuwar da,su kayi a tsakanin sai yar shiru ya biyo baya nan mama Rahana take tambayan ko may kuma ya faru,
Ummi Fatima tana kuka tana bawa yar uwar ta labarin abinda ke faruwa a gidan su yadda matan gidan yanzu suka dauki kahon zuka suka saka mata ita,da yar ta,a gidan da kuma hana mata abincin da akeyi a gidan,
Ummi ta karasa acikin wani irin kuka mai ban tausayi, atake rayuwan yar uwar nata zuciyar ta ya, baci sosai take, magana a hasale da cewa ni wanan al,amari nagidan ku yana,daure min kai wallahi,
Yanzu ace har a hana ma wani abinci a cikin gidan ka kuma shi maigidan bai dauki mataki ba a kai
Nan suka yanke shawaran cewa Aisha ta zauna a gurin Rahana har zuwa lokacin da za,a kaita gidan mijin ta,
****** ********** ******
Zancen duniya baya boyuwa don haka,barin gidan Aisha da,kwana biyu labari ya fara kewaye uguwa cewa saboda auren da malam Mudi ya daura da Aisha ,
Su mama Saude sunyi sanadin da yarinyar tabar gidan da zama zuwa wani gidan irin tsangwaman da ake mata a gidan,
Haka zancen yai ta,yawo abinda ba,ayi aka dinga fafin cewa shi akayi a gidan har maganan yazo kunne Umma Rabi,
Hakankinta ya tashi don ji irin wullakancin da akaiwa yar mutane saboda dan ta,da ta aura don ba,a bari yai kunya ba,
Umma Rabi tasa,a,fara gyara daya daga cikin dakunan gidan inda yaran zasu zauna,
Tsohon part din mahaifin Hamza din wanda yake ciki da falo ne sai dai ba masu girma bane sosai haka sune ake tawa dan gyara don su zauna a ciki,
Dakin ya tsufa sosai amma dole haka zasu zauna din a ciki ,tunda basu da wani,
Yanzu rayuwar Kubura ko ba,a fada wa mutum ba yasan cewa ta zama wata yar birni sosai saboda irin yadda idanuwan ta suka,bude,
Shigar ta kawai zai nuna,wa mutum cewa ta sake fiye da tsanmanin mutum,
Yau suna da wani dan liyafa da su yi wanda zai hada matasa masu yi da zamani da a gurin,
Tayi kitson attachment ya mayar da ita kamar diyar yare,
An mata gyara fuska wanda ya,sauya yanayin ta daga na diyan musulmai zuwa na diyan kabilu,
Wani dogon riga ta,saka a jikin ta ya dane mata jiki sharp din jikin ta y fito tsab,
Sai faman kiran ta ake a,waya cewa tazo an fara taruwa agurin sha,anin nasu,
Uwar ta,sai murna,da farin ciki take ganin irin yadda diyar ta yanzu ta koma one in town,
Sai washe baki take yayinda,Atika mishon batta da musulmi take faman koda yarinyar agaban uwar ta,
Wani daga cikin diyan Atika ne yashigo yake fada masu cewa ga Baba nan zai shigo gida,
Da sauri shige daki ta zuro wani katon hijjab a kanta, ta boye takalmanta a cikin jikin ta,
A,a yau sai ina haka tace Baba littafin da muke hadda dashine zan karbi a gurin wata yar uwar karatuna tunda Aisha bata,nan,
Tasako zance Aisha ne aciki don Baba din ya ya ji dadi ya barta ta fita, zuwa inda zata,
Yashige part din shi inda ta,waigo tana,wa uwar ta dan bye bye din samun nasara ta fice abinta,
Gurin part din ya hadu sai kida ke tashi samaru da yan mata masu karamin kwakwalwa suna ta sha,anin su gungu gungu a gurin,
Kubura tana daga cikin masu gudanar party din haka zirga zirganta yai dan yawa a gurin,
Daga inda yake tsaye yana iya hango wanan yawan sintirin da take a guri,
Turawa yayi wani dan duniya yakira mashi ita kamar bazata zo ba can ta taso a cikin ragwada tana tako daidai har ta karaso gaban,
A dan tsiwace take cewa malam kai ke kirana tana wani taunar chewing gun
Yace a cikin kasaita da mu samu dan guri inda babu hayaniya da yawa,
Motar big show suka shiga wace ke daga gedaya a Parker wanan shine mafarin haduwan ta da Nura wanda yaxo mata da kudi irin wanda take bukata da mafarkin samu,,,,
ZAINAB IDRIS MAKAWA,,,
👑 SARAUTAR MATA 👑
0⃣9⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
ALLAHUMA AJINIR MINAL NARRR,,,
Wanan novel din kada ku manta amanace tsakani na daku Allah yasa muci gaba da rikewa Allah yasa mu dace yan uwa
Hakannan naci gaba da zama a gidan mama Rahana, inda nake zaune ba wani tsangwama komai,
Ina gudanar da,al,amurana cikin natsuwa da kwanciyar hankali,
Saboda gidan mama Rahana kowa yana nuna min so da kaunz a fili tare da yaba min hankali,
Sai nake ji a raina dama ace tun farko a nan din nake zaune ina rayuwana,
Matsalata guda shine kewar yan uwana da ke damuna tunda ban taba tafiya na barsu ba,
Yanzu duk wani mugun hali a,Ummi suke nuwa shi tare da hattaran ta da yan diyan ta,
A wani yanmaci lokacin ina da sati uku a gidan mama Rahana sai ga mahaifiyata tashigo da zancen wai zan tare a gidan mijina,
Zance da yadaga min hankali kenan gabadaya wanda itama mahaifiyar tawa hankalin ta duk a tashe yake, ita,ma,
Ummi tazowa da yar uwar korafin cewa bata aje komai ba akan zancen aure na yanzu gashi zance ya tashi,
Mama Rahana ta kwantar wa da Ummi hankali da cewa shi aure ai alheri ne daga Allah dazaran ka dasashi sai kaga hanyoyin Allah suna budewa ta inda mutum bai tsan mana ba,
Da irin maganganun haka har Ummina ta kwantar da hankalinta ta zurawa sarautar Allah ido
Yan sayaya akai min duk da bangani ba amma inajin yadda su mama da Ummi ke shawara a,dakin akan zance na,
A can gidan baba Mudi matan gida sai gori da habaici suke sakewa wai rana bata karya saidai uwar diya tai kunya,
Yau gashi aure ya taso ummi bata aje komai da zatai min aure dashi ba ga shi malam Mudi ba dama ya taimaka min don sun kai karan shi a gurin yan uwan shi cewa yana maida hankalin shi ga yar agolan gidan shi fiye da,diyan su sosai,
A tsayar da magana cewa a gidan mama Rahana za a guda nar da duk wani abinda za,ayi sai a kaini daki na,
Raban da,za,a kaini a,ranan ne aka,sakani a lalai don ba wasu tarin kawaye ke gareni ba ni,
Ranan na yi kuka kuka irin mai tsuma zuciyar mai sauraren ta ,
Don za,a kaini aure ba gado da shimfida irin ta,al,ada sai tabarmi da yan sauran tarkace kawai,
Zokaga murna a gurin masu son gqnin bayan don sai shewa da raha suke suna yadda magana a gaban kowa,
Cikin ikon Allah sai ga dangin mahaifina tare da na mahaifiya suka iso tare da mota fam da yan kayan su sai dai irin na kauyawa ne,
Isowar su yasa guri yadan rude sai kama baki ake ana mamakin abinda,su kazo dashi, anan sabon gulma ya fara tashi kuma
Da yamman fari yan uwa suka tasani a gaba wai naje muyi sallama da mahaifiyata da kishiyoyinta da,suka tayar dani,
Mun shiga gidan da,sallama banyi tsanmanin sun karba muna ba,sai dai naji muryan Ummina,
Mun shiga dakin ta tana zaune tare da,wasu baki mata mutum biyu yan uguwar mune da,take shiri dasu,
Can daga kuryan dakinta kadan na,samu guri na,durkusa a kafana,
Kaina ya,sade a kasa yayin da take gaisawa da matan da muka shigo tare, dasu,
Daya daga cikin matance take cewa tau fadima ga Aisha nan mun kawo ta tayi maku sallama keda abokan zaman ki,
Nan da nan naji idanuwana sun ciko min da hawaye kaina yana sadde a kasa nace cikin kuka Ummi ki yafe min don Allah,
Shiru kamar ba zatai magana ba,sai can naji tace nikan Aisha may kikai min a,duniyan nan,
Kece dai zance ki yafe min nida a,sanadina rayuwanki ya zamto irin haka,
Wani kukane yazo min maiban tausayi da