Showing 216001 words to 219000 words out of 299981 words

Chapter 73 - Sarautar Mata By Makawa

04 Dec 2025

17629

kada yajin maki ciwo a banza,
Uwarta ce tashigo gidan rai a bace tundaga nesa take fadin wai may ye haka may ya kawo hakane wai,
Tana tambaya cikin bacin rai idanuwan ta,sun nuna mugun bacin rai tace wa Sadiya da ke kuka tashi mu shiga daga ciki, an taru ana kallon zai kashe ki kowa ya kyale ku haka yana dukan ki kamar ya samu jaka,
Umma tace haba Sa,a kin san halin Sadiya in tafara abinta bata jin bari wallahi tun abinan baiyi nisa ake mata magana taki bari,
Agaban ki fa Rabi danki yai mata wanan itin dukan tsiya na,wullakanci kuna kallo wallahi in "ya ta ta samu matsala bazan kyaleku ba sai nayi karan ku, gaba,daya tun da ba jaka nahaifar maku ba,
Yau naga masifa a,filin Allah, uwa jidali diya jidali ga mutane sun cika muna gida, suna kallo da saurare,
Daki na koma na gyara goyon yarinta da ke motsiniya a bayana cikin tashin hankali wai ana fada akan yar wanan tatsitsiyar yarinya,
Baba ya,samu Hamza yafita gidan cikin takaici da kunar rai ya samay shi a kofan gida yai mashi fada kancewa duk yadda ranshi ya baci ya baci ya bar dukan mace hakana don in ya saba da hakan haka zaici gaba dayiwa matan shi nan gaba,
Baba yace kayi kokari kaba yarinyar nan kudin ta don a zauna lafiya kadai ga halin ta ba yar rufin asiri bane,.
Baba kudin nan da take zance fa nawane ni nake bata tace zata sai fridge dashi shine
Da ta tayar min da hankali shine nace sai dai na bata a hanakali har ya kai rabi sai ta cika ta,sai fridge din dashi,
Dana samu matsalar nan shine nace ta aramin din na bawa emeka kudi shi a lokacin,
Murmushi Baba yayi kadan yace ai tunda ka bata ya zama nata don haka idan ka samu ka bata abinta a zauna lafiya bashi ke nan ba idan ka biya wani kudi kuma zata kara maka tonon asiri a kan shi haka,
Insha Allahu zan bata kudin ta ba kamar yadda kace din,
Baba yace abune babu shawara in bashi ba ai wanan zurian ba zurian auren ka bane hamza yarinyar da take tashin mace,
Ai babu tarbiya wadattace a gurin irin wa yan nan mata,sai tarin dana,sani kawai dan dadin zama da irin su kadan ne bacin rai yafi yawa,
Wallahi hakane Baba duk Umma ce takaini ga,wanan bala,in don ba yadda ban kurce mata akan wanan hadin babamma fir taki yarda tace ala dole sai nai auren nan tama dauki fushi dani dole nayi shi badon naso ba,
Yanzu ai gashi harda ita basu raga mata ba suci min mutunci suci mata suci ma yan uwa na ina macen zama haka baba ?
Babu komai kadai yi kokari ka biyata kudin a zauna lafiya kawai,

Nan ya zauna waje yana tunanen akan dubu goma sha biyu Sadiya take mai wanan balain haka insha Allahu zaiyi kokari ya,biyata sai ya dauki mataki
Ashe Aisha ba karamin hakkuri ke gareta ba don da kudin ta dayai sana,a Allah ya albarkaci sanan dasu yai auren Sadiya din,
Amma bata taba yi mai magana a kan su duk da ganin yana,wa Sadiya din spending da Umma tace yadinga sawo mata saboda shigan cikin da take dashi a lokacin,
Aisha batai magana ba amma karshe Umma din ce kuma abin ya fita a tsakanin su kowa na kallon su,
Uwar sadiya da ta fito tana masifa ita bazata yarda akan dan magana kadan aita bugar mata yarinya ba,
Har ta,wuce bai ce mata kallal lahu ba don matar duk ta fita mashi a,rai saboda basu da mutunci ita da yar ta,

****** ********* ******
Bayan komai ya lafa ina zaune a,daki ni kadai na kurawa rigunan dake yashe a,saman gadona ido, rigunan da suka hada fada yau a gidan,rigunan da basu kai ko dubu uku ba,don irin masu saukin kudin nan ne, bonanzar hanya ya,sayo,
Wai shine a kan su Sadiya ta sha,wanan uban dukan kamar wata jaka can,
Yanzu ashe ba,dama ya sayawa Jidda komai a gidan nan kenan sai tare da Sadiya don itace a kuma ta,koma kishiyar ta,.
Akan kin rufawa mijinki asiri da,dan magana ya hadaku sai ki shiga mashi gori da tonon asiri har ki tara mashi jama,a wanan wani irin rayuwane haka mai tonon asiri da cin mutunci,
Gaskiya halin Sadiya sai ita akan dan abin da baikai ya kawo ba sai kaji muryan ta yana tashi kamar wani babban magana,
Ga Umma tsoron cin mutuncin Sadiya take ji kamar zata dake ta,sai kiga tana wani dan sune kai tana tausa murya haba dai Sadiya ki bar yin haka mana da,sauran su,
Dan kudin hannu zan zage damtse na fara business na debewa kaina da yar diya,ta takaici tunda na fahinci so ake aga walle na,agidan kawai
Kiyayya harda yar yarinyar dake goye abaya,a hada da ita,gurin kishi,
Ashe haka kishi yake kowa da irin nata sallon kishi ba,a raina abin yiwa kishi ko kadan,
Kai jama,a Allah yasa mufi karfin zuciyar mu jama,a kishi bala,ine akan rigar yarinya tasha dukan banza abanza babu mai rama mata,



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABUIDDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,


Duk da,an kashe magana Hamza zai biya Sadiya kudin ta, har zuwa yanzu sama sama suke don yaki sake mata fuska,
Zaman yar tsama sukewa junan su duk da ita Sadiyan ta dan sake dama haka halinta yake cin mutunci da zaran tayi shi ke nan zance ya tafi a gurin ta sai wani kuma,

Mun cika kwana arba,in cif nasha gyara ta ko ina daga dakina har jikina don a dakina na canza kujeru da ledan kasa,
Haka ma jikina yasha,gyara don abubuwa da dama mama Rahana tasa ai min don na kara daraja a gurin miji kamar yadda ko wace mace take kokarin gyara idan zata koma gurin maigida,
Nai kitso har da kumshi ba wanda ya fahinci hakan sai mama hafsi ita hankalinta yana a kaina ko yaushe,
Duk wanan gyare gyaran da nakeyi Umma da,Sadiya wai basu fahinci cewa na kusa arba in ba a gidan,
Sai da safe da suka ga mama hafsi tana aikawa da masan da,Mama Rahana ta,aiko muna dashi, na sadakan arbain,
Yan uwa wanan al,adan sadakan arbain bawai jahilci bane don yin haka yana da amfani domin sadaka alheri ga,wanda akaiwa amma gaba daya yanzu mun daina mun marya dashi cikin bidi,a
Bidia din ne don annabi bai ce ayi ba amma kuma ance muyi sadaka don haka ya kamata mu dinga yin sadaka wa yayan mu don kariya ce babba akan su

Wani leshi nasaka a jikina sabo mai ruwan dark blue,sai farin zare da akai mashi aiki dashi as a flower takalma jakka har hijjab dina duk sabo ne,
Na goya Jidda da showel fari a bayana tana barcin ta na jawo kofa na nufi dakin Umma ina mata sallama,
Zan fita karo na farko bayan haihuwana kenan don tunda na haihu van fita zuwa ko ina ba ina gida ina jego kamar yadda ya dace mace ta zauna guri daya ta samu hutu ta mayar da jinin ta da ta zubar, a baya gurin haihuwa,
Koda ba,hali gariku ba zaman ki guri daya kina ci kina sha kina,samun hutu zai saukar da ni ima a jikin ki,
Karar takon takalmana shi yasa hankalin su Umma har da sadiya data dan leko ta kafan labulen dakin ta,din gani ko wacece ke tafiya,da takalma yana kwas,kwas,
Daga kofa na tsaya ina fadin Umma zan shiga gida gurin su Ummi na gaishe su,
Au injin yau anyi arbain ko ?
Muna gayar dasu adawo lafiya nace amin Umma daga bakin kofan Sadiya na tsaya ina cewa Sadiya zamu fita sai mun dawo ke nan
Ku dawo lafiya yan arzikin suna kusa an karba min yau ba a kyaleni ba,
Ina fita tamike zaune tafara sake sake a ranta sai daga karshe ta samo mafita don haka sai ta kutta kawai, ta,koma ta zauna saman kujeran ta,
Nikan farkon fitana gidan mu na fara shiga na samu Baba a gida bai fita,ba muka gaisa dashi cikin jin dadi da farincikin ganin na da yayi,
Daki daki na,shiga na gayar da,abokan zaman Ummina, sun nuna jin dadin gani a fili sai da abaya idan na,daga ai muna dariya, wai na nakasa,
Atika ce taso zolayana da cewa ina yar fitinan gidan ku kai Sadiya babu dadi wallahi,
Murmushi nayi ba tare dana bata amsan komai balle tace taji wani abu a bakina akan Sadiya,
A dakin Ummi na nacire hijjab dina already, Jidda na barta a gurin Baba Mudi tun shigowana gidan,
Na zauna ina cewa ina su yan biyun Ummi su ke ban gan su ba sai take cewa sun tafi sayo mata kayan miya,yanzu zasu dawo,
Gaisawa muka kara yi da Ummina irin na da da mahaifi take tambaya mutanen gida na amsa da lafiya kalau,
Ina maman ki nai murmushi nace, ta tafi, cikin gari gurin karban kudin ta don yau bata,samu fita,saboda sadakan da ta,tsaya yi na arbain din mu,
Akwai ta dai da kokari wallahi tana kokarin ta da ku a gidan nan amma ita,sarakuwar taki kan halin ta,sai ita,
Mijin naku yaba matar tashi kudin ta ko, ?
Wallahi Ummi ni ban san tsakanin su ba,saboda ban son saka kaina a cikin zancen su,
Ni ko su na abinsu koda ta,sa suban ban biye mata sai dai tayi haukan ta ta,kare shike bata haushi dani wai sai na dinga mayar da ita mahaukaci,
Kada kiyarda kuna sa,in sa da ita don yana kawo raini da wullakanci abinda akeson a fada maka na,sheri gurin irin wanan fadan na kishi ake ma mutun kake akan abinda bashi ace shine yayi ko wani mugun tarihi wa iyayyen mutum da,sauran su,
Shine dalilin da yasa ba,a son fitinan kishi don babu komai a cikin shi sai sheri da kissa ke ko nasan ko dan kissan matan baki iya ba, tafa cikin zolaya na,
Nace a,a Ummi ni wanan ba a gabana yake ba taje taitayi ai sunyi daidai da mijin nata tunda shima yanzu ya iya, ai,
Ina dai horon ki kada ki yarda ajiki dashi akan abin duniya don baki san irin ranan da,shima zai maki ba,watarana,
Zama dama cudeni na cudeka ne kataimaka lokacin bukata indan kana da hali kaima watarana sai Allah yasa maishi ya taimake ka,
Don haka don kin bashi ba,wai ance ki saka mai ido akan duk takon shi ba hakan sai yakai wata rana kin mashi gori baki sani ba,
Ummi nifa ban taba bashi abu na sa ido ko na kara waigen abin ba bashi kawai nake don rufin asirin mu,
Tace ashe kin gane kin wa kanki kuma dubara duk tsiyan mutum watarana dole yasan kayi mashi rana ta wani gurin,
Mun dayi hira nace zan tafi don har gidan Anty Hindatu da Mamana Rahana zan shiga da yan sauran guraren da ya dace,
Sai nadawo kafin na,shiga gida zan shigo na kara ganin ku,,

Gidan mama na nafara zuwa mun dauki lokaci da ita muna hira ta na bani shawara da,abubuwan da ya dace na rayuwa,
Sai gidan Hindatu dana shiga zuwa karfe biyu a can nai azahar har la,asar muna hira da ita,
Nafito na,shiga gidan iyayyen ta na gaidasu sai gidan su kibura da yan uwan ta duk sai da na biya a tsatsaye muka gaisa dasu nai masu bangajiyan buki da,suka zo min,
Ranan nasha zumunci sosai don nasada zumunci a gurin yan uwa da,abokan arziki,
A gurin Ummi na,dawo akaiwa jidda wanka don dare yayi lokacin sai da,akafito sallah magariba nashiga gida a lokacin cikina yai dam da abinci na koshi a gurin Ummina,
Nadawo gida na,samu kowa a gida gayar dasu nayi na,bude kofa na nashiga, suna tayi min ba,a wai na samu fita yau sai jnda kafana ya tsinke na tsaya,
Sadiya bata samun abinci ba nima haka ban damu da na tambaya ba don a koshe nake,
Ganin nadawo ba,a bani abinci ba yasa Mama tambayan ina abincin Aisha , ne ?
Ni walle ban sa mata ba don gida naga ta tai, shinas sa ban samata ba,
Tsit gurin yayi don jin may Sadiya,ta fada a gadarance kai tsaye,
Sai Ibrahim ne yace amma dai ke ina ganin baki da hankali mace da,jego tana shayarwa ki hana mata abinci ke ta taba maki haka ta hana maki abinci a gidan nan,
Kai walleh karka damay ni ra,ayinane hakan don may zaka matsa mini ne wai kaji min kai,
Umma tace Sadiya wai mi da baki son gaskiya shin ke taba ganin ko dabba anyi horo nai da yunwa,
Abinci dai yau gashi an sayo wadatattce kowa yaci ya koshi har abin cikin miyan duk Alhamdullahi,
Ai basai ta ci ba dama ai ba don Alkah ya sayo ba don yaga tai arbain azaton shi Aisha ce zatai girki shine ya sayo mai yawa haka,
Shiyasa ni kuma na juye duk na rabawa kowa ita da taje gidan su sai taci a can,
Yau kan kamar na tanka sai na tuna yanzu fa Ummi ta ga yi min nasiha akan rayuwan Sadiya cewa irin su ba,wai auren ya damay su bane zasu iya cewa namiji goma ba uba goma bane ai
Su basu zauna ba kai kuma da aka,sa.u ba,a barka ka zauna dakinka ba su koreka ko su tsaya idan kina da diya,su dinga azabantar da diyanki na wani dan lokaci su gudu, subar yara kamar marayu,
Mafiyawan aure yanzu haka yake wallahi, sai kiga an samu mace da mijin ta a,tayar mata da hankali ita da diyan ta karshe ma,akore ta gidan ita kuma amaryan tace bata zama tayi bautan diyan wata,
Maza basu da tunane yanzu sai wanda Allah ya sa yagane gaskiya za,a shigo mai gida da iyayi yasa ma,amarya waigi bazai dauki rainin hankali da tazo dashi ba,
Amma masu dauka yanzu sunyi yawa don sauyin yanayi zuciyan mazaje yafi karkata ga amarya sai na,Allah ke tsayawa yayi adalci don haka idan kin tsuci kanki a,wanan yanayi kiyi hakkuri ki kawar da idon ki ga irin kaidin da ta,shigo dashi kada kice zaki tsaya wai ku kwata ance mai laya kiyayi mai zamani,
A karkashi kasa zaki gasa mata kwakwa a hannu batare da an fahinci naki halin ba,
Don haka sai na daure kawai nai shiru batare da na bata amsar duk maganan da takeyi akaina ba cikin gadara wanda duk wanda ke kusa zai dauka cewa tsoron masifan Sadiya nake ji da yawa, hakan,
Daya bayan daya suka fara,watsewa,a,gurin Hamza da yafita tun fara zancen sai gashi dauke da leda a hannun shi,
Idanuwan su gaba daya yana akan shi dakina ya,shiga da ledan ina tsaye a bakin gado zan yiwa Jidda shimfida,
Jin shigowan shi dakin yasani juyowa dan naga may yashigo yi sanin da nayi cewa baya shigowa a wanan lokacin idan har Sadiya ce da girki,
Ledan hannun shi yake kokarin miko min yana cewa gashi ki ci kafin ki kwanta kada ki kwana da yunwa,
Namika hannu ina cewa nagode amma ban ma da yunwa don naci abinci a gurin Ummina kafin nazo,
Ki dai karba kici ko da,zuwa dare don kada ki kwana da yunwa a cikin ki ,
Sai na mika hannu na karbi ledan yake cewa gwagona tana barci ke nan eh kawai na,bashi amsa a takaice kawai,
Har yakai bakin kofa yake ce min ki cire ledan tea a ciki don kada ya yoye maki naga ba ruwan zafi tasa nace a hado maki a can,
Nagode na kara furtawa cikin ladabi tare da juyawa inda jug na dauko ledan na fara juye tea, sai wani kumshin da na gani ashe, nama ne gassashe mai yawa,a cikin takarda sai bread longi guda ,
Ban tsaya ta kan kayan ba na fara zuwa don nayi sallah kafin na kwanta,don na kwaso gajiya a tare dani,
Murya kasa kasa naji Sadiya a dakin su tafara halinta ta,na cewa wanan ma zance ne don ba zan yarda,ba ko ka,sayo min nawa ko kuma na,shiga dakin ta na kwaso abin da ka,sayo mata mu raba,
Muryan shi naji yace au ashe ba,dadi ke da kika kwashe wanda na,sayo kowa yaci a gida kika hana mata,
Aiko yau akwaita, a gidan nan wallahi don bazan yarda da,wanan cin amana ba a filin Allah,
Ke jinan yace a cikin wani kakausar murya muddin kikai min balai a cikin daren nan yau wallahi za,ayita a kare don nagaji da fitinar ki wallahi,
Daga nan na karasa alwala, na nashige daki abina tare da rufo kofana har na rufe sai na tuna da mama hafsi na diban mata bread da naman nakai mata na,samay ta tana sallah don haka, na aje mata,kawai na tafi,
Har na,shige ina jin suna rikicin su yana cewa ai nace idan kin isa, ki je ki dauko,
Murmushi kawai nayi, na,shige dakina ina mamakin halin iri na,Sadiya da,son yawan masifa,
Ni dai har na idar da sallah na zauna

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login