Showing 249001 words to 252000 words out of 299981 words
yafara tuki yake cewa kai Umma akwai rigima daga shigar mu ta tayar wa kowa da hankali nima na dauka ko wani zance ne can nadaban wallahi,
Ranan haka na wuni sukuku dani ina kullawa ina kwancewa sai faman tunane nakeyi ni kadai a gida,
Sai dare ya dawo cikin anna shuwar shi ban nuna mashi komai ba kuma ban ta da zancen ba don ban mason ayi shi,
Dadare bayan mun gama komai sai barcin shi yake hankali kwance niko na kasa runtsawa sai tunanen abinda Umma tai min yau nakeyi,
Umma shike nan tai min wanan sanadin ta kishiya a daidai lokacin da muke zaman mu na dadi ni da mijina
Amma yanzu zata sa a kawo min wata a cikin gidan nan ta zauna a matsyin kishi a gare ni, Umma bata bukatar zamana a gidan dan ta ko kadan,
Yadda na saba zama ni daya yanzu idan ankawo wata na tabbatar da duk farinciki na zai rushe ne kamar yadda Umma take bukatar gani na,
A haka muka zauna cikin wani bakon yanayi ina lura da tafiyan shi ko zanji wani abu ya taso akan zancen kishiya sai da har zuwa tsawon lokaci ba abinda ya faru shi kake ji,
****** ********* ******
Watarana ya,shigo gida da takardun shi na karba kamar kullun zan shiga mashi dasu daga ciki sai yake ce no dakata ai takardun nakune na tafiyan ku, saudiya,
Ban san lokacin dana juyo ba cikin murna nakai mashi ruguma tare da subantar shi ina cewa kai yayana aiko naji dadi nagode, wallahi, sai faman murmshi yakeyi yana jin dadin yadda nake ta faman yabawa,
Nasake shi ina cewa amma ni dawa keda wanan sa,an rana haka yaya ?
Keda suwa kike son tafiya dama bada sisters dina ba tare na,samo maku sai mama,
Naso ibrahim yabiku kada kuyi tafiya babu namiji a tare daku amma kuma har yanzu ba,a samu kujera ba,
Nakara rugumay shi nace wayyao yaya ka gama min komai don kafitar dani daga zargi wallahi,
Nace wai ashe saudiya na da kwasan manyan bako bana gaskiya yaya ban san irin godiyan da ma zan maka ba,wallahi,
Yace in baki sani ba,aini na sani bari anjima kiga irin godiyan zan gwada maki ai,.
Dariya kawai nayi tare da kara kankamay shi ina murna da farin ciki sai sambatu nakeyi ina Allah nagode maka Allah yakara daukaka da budi na alheri yaya,
Kafin kwana biyu zancen tafiyan mu kowa yaji sai murna ake muna da fatan aje lafiya a dawo lafiya,
Su Zarah har ni saida sukaiwa godiya sina cewa sun san nice silar hakan don basu zaci ma zai kaisu ba,a lokaci daya haka,,
Muna ta Allah ,Allah lokacin tafiyan mu yayi don an samo wa yaya Ibrahim nashi,
Yai tafiyan shi zuwa lagos ya dawo mun tare shi da murna da farin ciki kamar kullun sbai fita ba sai washe gari ya tafi zuwa gaida Umma,
Ban bishi ba dontun lokacin da tai muna kuka nan ban kara zuwa gidan ba har yau din nan, tai korafin hakan ta barni,
Yasamu nagama girki ya zauna yaci yana wa madina ba,a wai itace tai girkin shiyasa yaji dadin shi,
Ina daga zaune gefen shi sai murmushi nake masu don yana kula min da al,amarin yarinyar sosai kamar shiya haife ta, har makarantan boko ya saka min ita na kudi ita da Jidda suke zuwa,
Sai da yakare na kawar da kayan nadawo na zauna daga gefen shi remote din tv dake aiki ya dauka ya rage karan tare da juyowa inda nake,
Hakan yasa na fahinci magana ce ta musanman yake son yi dani,
Yace cikin kura min ido tun kwanaki naso muyi wata magana dake Humaira sai dai ban samu lokaci bane don tafiyan da nayi,
Na zuba mashi ido ina kallon shi tare da sauraren shi, yace nasan zaki dauki maganan tawa da wani manufa ta daban,
Amma idan kin fahince ni sai kiga maganan ba,wata abin tayar da hankali bane,
Ya dan yi shiru tare da numfasawa yasake kura,min ido cikin natsuwa yace bawani abu bane illa zancen auren da nake son in kara kwanan nan,
Abinda naji azuciyata yafi karfi akirashi da faduwar gaba sai dai a fili na dake ina sauraren shi batare da,na nuna damuwaba a fili,
Nasan ni dake akwai fahintar juna Humaira kan mi a hade yake bamu da,wata matsala a ko wani bangare,
Itama wace zata shigo din ba wai karamar yarinya bace nasan tasan takan duniya sosai, shiyasa na yarda da shigowan ta a cikin mu,
Don haka ban son kiyi wani tunanen ko ban son ki ne nace zan kara aure ko kuma ki dauki wani abu da tsanani har ki bata tsakanin mu,
Kuma ban son kiyi tunanen ko wanine yasani yin wanan auren ban tashi yi ba, kinnsani tun farko ni mutum ne mai ra,ayin hakan,
Banyi bane abaya don ina son in maki adalci sai kin samu natsuwa da kwanciyan hankali, a gidana,
Hmmm yaya ke nan adalcin may kai min ko kuma kwanciyar hankalin may nasamu in akwai shi a gare ni nuna min in gani,
Shiru yayi tare da,dukar da kan shi kasa sai kuma yadago kai yana kallona kara jin haushin shi naji a raina har ban iya boyewa
Namike a zafafe nafara tafiya ina cewa nayi dana sani da auren ka Hamza a rayuwana wallahi,
Ya maimaita kslman Hamza da nace yace Hamza yau Humaira, nace eh Hamza ko ba sunan ka ke nan ba,
Bukatar Umma ya biya ai ban san ta isa ba da tasaka cika mata,burin da tace sai yau tasa ka sakeni saki uku ta zuba ruwa kasa tasha,
Mikewa yayi a lokaci daya ran shi a bace ya nuna ni da yar yatsa yana cewa kada ki fara ki zagar min uwa wallahi yanzu ranki zai baci a gidan nan,
Naga kina son kawo maganan da zata lalata tsakanin mu don ba zan kyaleki ba idan kika zagar min uwa Humaira,
Ki bari mu fahinci al,amarin yadda muka saba saboda kada mutane suyi maki dariya,
Ya kalleshi kasa da sama nace mutane ai sun dade da min dariya tunda ba yau kafara watsa min kasa a ido ba,
Yau ne aure ka ake min dariya a gida da,waje tunda kai ba dan goyon baya bane wallahi nayi tir da zama acikin ku mutanen da ba,su san arziki ba,
Ai kin san bamu da arziki tun farko kika,aure Aisha ,?
Nadauka a lokacin ko ku yan mutnci ne ai sai yanzu na fahinci ko ku suwaye,
Na tako har gaban shi nace ka,sake kawai ka huta da,wahalana da,akecewa na shanye ka,
Yace baki shaye ni din bane Humaira wana ke gani da mutunci in bake ba yafada cikin murmushin takaici,
Ya zo ya gwautani ya wuce nasha gaban shi nace wallahi sai ka,sake ni don ba zan zauna akara kawo wace zata sani agaba da,tashi hankali ba,
Hankade ni yayi ya fita daga gidan yabarni nan na tsuguna a gurin tare da rushewa da wani irin kuka bai ban tausayi,
Bai, madina tazo ta dafani idon ta taf da hawaye tana cewa kiyi hakkuru Anty ki kyale shi don Allah,
Rugumota nayi ajikina muka shiga rusa kukan a tare ba mai ba,wani hakkuri sai nice ma nagaji na kyale gudun karnajawa yar mutane ciwo,
Bai kara kula harkata,ba nima ban kara bi takan shi basai zaman doya da,manja muka shiga yi,
Bai saba ba don haka yahe ya fadawa mama hafsi a,asirce tazo tai min magana ita da anty hindatu,
Lokaci guda sukazo lokacin kwana hudu daya fada min zancen auren nashi,
Ina ganin su nasan sun san da zancen zaune nake a,falo dagani sai rigar barcin dake a jikina tun safe da zani,
Tun shigowan Hindatu tafara cewa may ye haka Aisha may ye kika mayar da kanki haka kamar wata bakauya can,
A take idanuwa suka ciki da hawaye nace muryana na,shirin kuka Anty may naiwa Hamza da Umma,arayuwan su suke min wanan azaban haka may ne masu anty,
Dafani tati tace kinga idan kina son muyi magana mai kyau tau share hawayen ki ki saurare ni,
Don wannan kishi naki yafi kama da irin kishin jahilan mata ba matan da,sukan kan su da addini ba,
Ita fa kaddara ai yarda da ita shine sharadi na cikan imanin bawa don komai da kikaga bawa yayi mukadddarine a gare shi, mai kyau da mara kyau sai ka,rugumay ta idan tazo maka,
Aisha mayye acikin wanan zance bafa wanan karon bane farkon kishiyar ki, may zai hana ki natsu ki nazarin wacan artabun da kuka sha wancan karon ki san ta ida zaki bullo mashi,
Amma kinzo kina wanan irin ta da hankali haka kamar wace bata da,wayo,
Don Allah Aisha ki natsu ki kwantar da hankalinki ki fahinci mijin ki ku zauna lafiya kada wace za,a kawo tazo ta samu kuna fitina har ta samu kafar da zata rainaki,
Mamahafsi dake gefen mu ta ce ni Aisha na,rasa ina hankalinki da,wayon ki, ya shiga ne wai,,
Da har kika rufe ido kinawa mijin ki wanan tujaran cikin nuna,rashi ladabi da tarbiya,
Shiru nayi don zancen su ya fara,ratsa,min zuciya nan suka sani gaba da fada da nasiha har saida nasauko,
A,karshe suke ce min na yi hakkuri na kara tausar zuciyata sun san hakan akwai zafi amma idan nai hakkuri komai zai wuce
Gashi duk mijin ki ya tayar da hankalin shi don kin ki kwantar da hankalin ki ga buki na karasowa saura Sati daya da yan kwanaki,
Da sauri na dago kaina nace satifa kikace mama, mama tace eh sati mana bakin ki kwantar da hankalin ki ku fahinci juna da shi ba,
Kin ba yan uwan shi da uwar shi dama sun shige maki gaba tare dasu yake aiwatar da shirye shiryen shi an barkina nan kina ta haukan ki ke kadai,
Ni don ansan ina,tare dake komai ba,ayi dani Aisha ina dai jin wanda yazo min a kunne na,
Mama yanzu ashe har auren yazo ban sani ba mama wallahi hamza ya cuceni yaci amanata wallahi,
Don Allah kibar wanan haukan Aisha ki natsu inji hindatu yanzu ki saurari maganan karshe da zaman maki,
Idan yadawo tunda ya nemo mii muzo gareki ki kwantar da hankalinki ki fahinci ina ya dosa ta yadda zaki mayar da komai da yan uwan shi keyi a ba,tare da keba,ki nuna masu ke din kin kai komai yaddawo a hannun ki ki wanke kanki,
Nan ta fada min duk yadda zanyi har suka tafi bai dawo gidan ba sai dare yadawo,
Lokacin muna zaune falo da yarana ina cikin kwaliyan material pink color da,golding,
Yarana,munci kwalliya dasu sai wasan su sukeyi a sanyaye yashigo gidan don yasan ba sannu zai samu ba gare ni dan dama a gurin madina in tana falon
Amma ga mamakin shi sai yaji ina mashi sannu da zuwa, hakan yadan bashi mamaki maimakon ya shige yadda ya saba sai yadawo falon ya zauna yana wasa da yaran shi,
A sanyaye cikin murya mara sanyi nake cewa abinci fa yaya yace cikin murmushi in Rangida tabani zanci mana tunda kun barnimaraya dake da yaran ki
Ban bashi amsa ba na shige kitchen na hado mashi, abinci nakawo mashi yana ci ina zaune daga gefen shi yana satar kallona a hankali,
Sai da naga yai rabin abincin nake cewa yaushe ne auren naka za,ayi,
Dagatar da cibin da zaikai baki yayi yana cewa kin sauko ke nan daga fushin naki, dan gutun murmushi nayi iya fuska kawai,
Yace koke fa Humaira yaushe rabon da nagan ki haka duk kin wani hargitsamu ga baki daya kin hanamu shakat a gida nida yara baki dayan,
Yau da kikasake koke bakiga gidan naki ya dawo normal ba kamar baya humaira ban son ki tayar da hankaliki akan wanan zancen kamar yadda kikayi,
Kin barni a maraya banda abikin shawara dole naje gurin su zarah na nemi shawaran su,
Saida na hade yawun takaici tukun nakakaro murmushi ina cewa ai yanzu komai ya wuce sai muyi yadda kace,
Sannu a hankali nake tambayan shi yana fada min abubuwan da akeciki ni kuma ina kafa nawa dokar ina rushe nasu,
Washegari da safe zaifita inajin zarah ta bugo mai waya sai ya bata ansa dacewa tazo ta samu humaira asan yadda za,ayi,
Komay tace mashi sai naji kawai yai murmushi yace nadai ce kuzo gurin ta bashike nan ba,zata baku komai da za,a bukata,
Ya juyo inda nake zaune yake cewa Zarah ce zasu zo su samay ki sai ku tsara yadda za,ayi,
Nai mashi adawo lafiya har ya kai kofa sai kuma ya dawo inda nake zaune ya dawo ya tsuguna daidai tsawona yana fadin a dai kara hakkuri please,
Ban son naganki a damuwa ko kadan idan har kinga nayi ba daidai ba ki nuna min kuskure na nace naji kawai yamike yafita,
****** ********* ******
Sun shigo gidan suna wani hura hanci sai nafito ina ce masu, a sannun ku da zuwa ashe kuna,tafe,
Sai wani bina da kallo sukeyi suna yatsunar fuskan su cikin yan harare harare,
Saida suka zauna muka gaisa sama sama dasu zarah tace gamu mun zo ance dole sai mun ganki tunda kece shi,
Murmushi nayi nace zarah aiko kin ji dadi tunda,kaunar ki ta zama yadda kike so,
Wani harara ta bakado min na wasa tace aini wallahi yanzun kifi karfina Aisha nadan rugomo tanace sai anty na,
Nan muka wasance naciki na ciki ga kowan dole ba don sun soba muka tsara yadda za,ai komai, a tare,
Sai yamma nya,dawo sai dai naga wasu a bayan shi suna shigowa da akwatina har kala biyu ko wani saiti sai kyali yakeyi yi,
Ya,sallami yaran yana mazu godiya tare da basu kudi, ya zauna yana cewa yauwa wallahi tun safe muna,sokoto ni da mansur sai yanzu muka dawo komai banci ba tun safe wallahi ina can ina wahala a kanku,
Idona akan akwatinan da ya shigo dasu nace nakawo maka abincine yace eh amma yanzu da zan samu abu mai dan ruwa zaifi min nace na hafo maka tea ke nan ko yacd ok abani,
Nakawo mai tea din yasha batare da bread ba sai da ya shanye cup din tas,
Wanka yashiga yafito akwatinan suna gurin da aka aje su har yanzu yafito saye da,far jallabiya a jikin shi ina dan lalashi mimi dake kuka wai kafanta yana kaikayi,
Daga inda yake tsaye a bayan kujera yake cewa Humaira nadago kai da kafan yarinyar a hannu tare da waigowa inda yake yana cewa,
Kalli akwatinan nan ki gani ki zabi guda daga ciki guda kuma gobe su Zarah zasu zo su dauka, su tafi dashi ki dauki naki ki sa a dakin kii yanzu,
Kamar banji shiba na dauki yarinyata na goya a bayana ta lafe tai shiru a bayan nawa sai barci sai da na sauke ta na shimfide a kujera,
Yace min bakiji may nace maki bane Humaira na dago ido kamar zanyi kuka nace naji mana yace tau kiyi hakkuri ki dauki guda daga ciki,
Gaban akwatinan na isa na dan kura masu ido na wani dan lokaci naji muryan shi yana cewa duk abugudane aciki kalar akwatinan ne kawai aka banban ta sai na duka na jawo dan kit din mai ruwan milk din dake a gabana a hankali,
Yana tsaye yana kallona nafara jan akwatinan a hankali zuwa dakina daga inda yake a tsaye ya dan girgiza kan shi yabini da murmushi har na shige dakina da akwatin ya sauke ajiyar zuciya a hankali,
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABUIDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON HAKA CIN AMANA NE,,,,,
Sosai akai shagalin buki wanda har lokacin ban ma tsaya tambayan ko wacece Amaryan ba sai daren buki nake jin wai wanan Biban ne da ya nema tun farko,
Tayi karatu a college of education na Argungu kuma itace tafarko a gurin uwar ta, amma su goma ne a gurin mahaifinta uwar tace mace ta biyu a gidan su,
Yan uwan Hamza sai faman rawan kai sukeyi suna zakewa har da cewa yanzu kan an auro masu wayayya don Biba yar gaye ce,
Zancen su yana sani cikin tashin hankali amma sai nake dakewa kawai na basar idan kin gan ni zakice ban damu ba don sai shiga nake ina fita,
Duk da sabon kayane a dakina amma sai da mama tasa Hamza ya kara gyara min guri,
Sabbin set ya sayo min a sokoto masu ruwan fari da purple, set din suna da matukar kyau sosai wallahi,
Abin gaba ya kaini don na kwashi nawa nakaiwa Ummi na sai kuma hakan ya jawo wani fitina Umma take cewa wai don may ita ba,a kawo mata ba zaice na kwashe naba uwana,
Yace haba Umma don naba mahaifiyar Aisha abu mai nayi idan har kinyi la,akari da irin halarcin da sukai min su,