Showing 252001 words to 255000 words out of 299981 words
Kudin sune fa nai amfani dashi na nai jarin da ya kaini haka har yau mutanen nan basu yi zancen kudin su da ke kaina ba,
Maganan da ya fadi yasa tai shiru don tasan gaskiya ya fada mata ita kuma Ummi taba mama Rahana tsohon wanda na bata da zan dawo sabon gidan mu,
A gidan su Ummi ma sai kananan magana akeyi wai na samu guri na mallake Hamza sai abinda nace in bashi nakaya sabbi haka za,ace wai sai ancanza su don kawai na yaudare shi na kawo wa uwata itama tasa ai yana da uwa shi ma mai yasa bai kai mata ba,
Kane, kanen da nayi a harkan ba karamin taimaka min yayi ba don duk wanda ya ganni zai dauka ban kishi komai, sai dai na kasa na kasa, don zuciya ta a,tashe yake,
Ko da za,ai auren Sadiya ban ji irin yadda nake ji a yanzu ba ko dan na kara girma ne, duk da maigidan yana iya kokarin shi gurin ganin bai kuntata min ba a harkan auren nashi,
Duk abinda nace sai dai yace min tau kawai ya bayar ayi koda baiyi niyayya ba,
Hakan yasa kowa na yabawa da hanakalina amma duk da haka ban ganin farin shi kai kishi dai kumallon mata ne kawai, sai hakkuri,
Yan kawo amarya suka shigo da gudan su, sai shewa sukeyi Allah yasa ina cikin kawaye da yan uwa da abokan arziki har makwabata dan nayi sabbin abokai matan abokan shi sun cika min daki,
Muna zaune tab a dakina ina cikin wani irin rantsatse lace da hindatu ta sa aka kawo min daga lagos, mai ruwan purple da stones farare sai shinning nakeyi zakace ko nice amaryan ,
Abinda ya daure min kai shine duk wace ta ga amarya sai ta dawo dakina tana fadin kai namiji dai kabarshi kawai wallahi, ni dai ban san abinda suka gani ba,
Sai da aka kawo ta dakina wai an kawo ta ai muna fada irin na al,ada da akasaba yi idan an kawo amarya,
Matar dake magana tace tau Aisha yau ga Habiba nan mun kawo ta zama a cikin ku, ance zomu zauna zo mu saba sai kuyi hakkuri da junan ku kujewa zagar makiya,
Babba ya rike girman shi karami kuma ya tsaya a matsayin shi, sai a zauna lafiya,
Sai bin dakina suke da kallo da ajiyan zuciya don sin san na zarce mata matar take cewa ina uwargidan take ne wai Hindatu tace ga tana tare da dan tabani duk sukayo idanuwan su a kaina caaaa,
Sai matar tace Ummm lalai to kuyi hakkuri kinji ga amanar ya ta nan mun baki keda mijin ki,
A,a mama iniji hindatu idan kunbata amana to ita Aisha a,wa za a bar amanan ta a dai bawa juna amanan su azauna lafiya shike nan,
Suka fita zuwa dakin su tun a kofana suke cewa lalai akwai magana wanan ce uwargidan ai kamar ma Biba ta girmay ta nake gani shine akace har diyan ta biyu,
Wasu kuma suna cewa wai yar inace halan don basu sanni ba a garin sai akace masu yar sokoto ce o lalai kuwa,
A daki na kuma su Hindatu da sauran abokai cewa sukayi kiyi hakkuri Aisha wanan matar da kike gani a tsaye take dubi ko mayafi bata yafa ba a kai kamar amarya, wai ita wayayya ki yi hakkuri ki hidimar ki kawai, ,
Shi kuma mijinki ki kara mutunta shi fiye da da don ki karawa kan ki girma a idon shi ki kula da yan yaran ki,
Muna jin suna cewa Habiba badi war haka muzo bukin yan biyu maza masu kama da uban su,
Daya bayan daya mutane suka fara watsewa a gida har aka bar mu saura i mu kadai a gidan amarya tana dakin ta nima ina nawa da yara na da madina,
Madina kamar wata babba tun fitar jama,a ta gyara min daki yakara komawa tsab dashi tasa muna kamshi,
Sai zuwa sha daya da wani abu ya shigo gidan da alamar gajiya a jikin shi ya na dauke da leda guda biyu a hannun shi muna mashi sannu da zuwa dagani har madina,
Madina ya mikawa dayan ledan da ya,shigo dashi, sai ya dan duka ya na taba mimi dake barci ya dago yana ce min ya gajiya Rangida,
Lafiya kawai nace mashi tare da dukar da kaina muryan shi naji yana cewa ni zan kwanta sai da safe ke nan Allah bamu Alheri nace mai,
Ya juya yana tafiya a hankali yabar dakin nacewa madina rufe muna kofan mu kinji, nace mata bayan ta rufe kofan bude kuci abinda ke ciki sai kun koshi,
Tashi nayi na fara cire kayan dake a jikina a zuciya ta ina tunanen yadda zai yi idan ya shiga dakin,
Yaran suna hiran su da dariya suna cin naman su da juice niko sai tunane nake yanzun haka kilama Hamza ya gama afkawa amarya ko don nasan shi kamar zaki yake a gurin mace,
Har yaran sukai barci ni ina zaune sai faman tunane nake nikadai ina juyi cikin bacin rai sai tsakar dare barci ya dan kwashe ni,
Washe gari tun da safe na farka na hada break fast mai lafiya basu fito ba har wani lokaci kofan ta yana a rufe,
Har na koma daki na shirya jikina na dan kwanta don nahuta ga kuma bashin barci a kaina,
Barci yadan fara daukana naji shigowan shi dakin sai kamshi yake yai kwaliya da shadda mai ruwan makuba,
Daga inda nake kwance na dan bude idanuwa na na kalleshi duk da shigar tashi tai min kyau amma sai naga yai min wani baki a idona,
Har inda nake kwance ya tako ya dan manna goshin shi da nawa yana cewa antashi lafiya ina dan kaucewa nake cewa Alhamdullahi,
Yace abinci fa naga kin aje a dinning kifito muci mana nadan bata fuskana ina cewa ni a koshe nake bazan ci ba,
Mikewa yayi yana cewa may kikaci halan ki taso muci ina son muyi magana da ku ne,
Shi yafara fita alokacin Biba tana tsaye daga kofa tana kallon kofan dakina don taga ya dade aciki a ran ta,
Bai wani jima da fita ba nafito daga dakin ina saye da Arabian gown baki daga gefen kafadun shi an mashi adon light blue color da stones, na daura dan kwalin shi a kaina gashina dana tufke yafito taba da ribon din da na daure kaina,
Sun zauna ko da nafito sai dai ina fitowa naji shi yana ce mata zauna daga can ya nuna mata dayan kujeran da ke daga gefen shi,
Nima da nazo a dayan dake fuskantar ta na zauna muka sa shi a tsakiya,
Banyi nauyi ba gurin fara bude kulan abincin dake a saman tebur din pepper soup ne na kayan cikin rago sai dankalin turawa da kwai sai kayan shayi a tsakiya,
Na dan dago ina ce masu bissimillah ko tana duke da kanta tana jagular wayan ta dake hannun ta fuskan ta a,daure yake tamau,
Shike fadin a,a zuba min mana tunda ban saba zubawa ksina ba da can, nace cikin murmushi amarya ki fara aikin ki ki zubawa maigida abinci yaci,
Ta wani dago kai kamar mai fada tace bake yace ki zuba mai ba, dan kallon shi nayi sai naga yai murmushi yace zuba min kawai Humaira,
Umurnin shi nabi na zuba mai abincin ba bata lokaci ya fara cin abincin hankali a kwance har lokacin Biba kanta na akan wayar ta kamar bazataci ba dan kadan na zuba a plate nima na faraci a hankali ,
Ko may tagani tagani ta jawo plate tazuba itama tafara ci zan iya cew duk tafi mu cin abincin tun a lokaci na fahinci tana da ci sosai tsab nai mata kallon kyau baka ce wuluk da ita,doguwa mai dogon fuska da pinpurs,
Duk da tayi makeup a fuskan ta bai hana kurajen fuskan ta fitowa ba a lokacin,
Sai da yagama ya goge bakinshi tsab har lokacin Biba cin abinci takeyi ya dan yi gyaran murya abinda yasa kowan mu natsuwa ke nan,
Yace am da,farko dai zance na godewa,Allah da,ya hada rayuwan a gurin guda don kasancewan mu a tare,
Don haka ina son ku saurare ni da kyau kuji may zan fada maku, Humaira,
Sai nadago kai na,kalleshi yace ke ce babba zan ce zamu baki hakkuri akan ku zauna lafiya, a gidan nan da bakuwar ki,
Ki sani ke ma,Biba ki sani, cewa bawai ban son mata na bace ko tai min wani laifi ko gazawa na auro ki,
A,a ra,ayinane kawai na son zama da mata biyu a gidana don haka ina fatan zan samu zaman lafiya a gurin ku kamar yadda nake fatan samu,
Don zaman lafiyan ku a gidan nan shine kwanciyan hankali da cigaban rayuwa ta,
Amma in kuna fitina a tsakanin ku gaskiya daukan mataki akan duk wacce takawo min tashi hankali a gida,
Don haka ina fatan zaku kasance masu biyayya a junan ku ku kawar da,duk wani kishi ko tsegumi kuyi zaman lafiya don kun sani ni ba mazauni gida,bane,
Sai zancen kwana ina son ku raba a tsakanin ku duk yadda kuka raba is ok for me,
Dafatan zan samu yadda nake so a gurin ku a zauna lafiya,
Gaba dayan mu shiru mukayi ba wacce tace uffan daga cikin mu sai shine yakawar dashirun da cewa umhumm ina sauren ku ne fa don fita zanyi, zuwa kauye yanzu duban wani gona na,
Biba ce tace why not muyi kwana bibiyu kamar yadda akeyi juyawa yayi inda nake yana cewa madam hakan yai maki ko ?
Nace ba matsala,Allah ya sa mu dace, yace amin sai ga mimi ta shigo tanufi gurin shi nan hankalin shi ya,dauke akan yarinyar, sai biyewa shirmay ta yake suna hira tana dan tataba mashi jiki,
Biba tace cikin wata murya shike nan zan iya tafiya, ko?
Yace fuska a daure ki tafi mana angama ai da fatan zaku kiyayye dokana ,
Naji kawai tace tamike zuwa dakin ta nabita da kallo doguwa ce ta sosai bata da baya don zan iya cewa da gaban ta da,baya duk dayane,
Ajiyan zuciya na,sauke koda na dago kai yana kallona yace yaya dai na iya zabe ko,
Murmushi nayi nace kwarai kuwa yace nasan itace zatai daidai da,ke shiyasa na zabe ta
Baki na tabe nace zaku daiyi daidai kai da,take matar ka nikan may ye nawa a,ciki,
Yar dariya yayi yace Rangida ke nan bazaki fahince ni ba ke nace kwarai kuwa,
Mikewa nayi don na hada kayan dake gabana sai naji kida ya fara tashi a dakin Biba, a,raina nace wata sabuwa kuma sai mimi dake gefen shi tafara rawa nace matsala Allah ya,cece ni da,yara na wanan sabon akidar,
Wasu yan matane suka,shigo gida sama sama muka,gai sa dasu suka,shige dakin Biba sai shewa mukaji suna tafawa kitchen na tafi donkai kayan da mukaci abinci dasu,
Shima dakin shi da aka,gyara ya shiga ina fitowa muka hade daidai lokacin da sukai wani shewa da,tafawa suna cewa, sai ke ta Hamza yaro, guda daya,ba bari ba aci gaba da gashi kawai muna kallo,
Kallon juna mukayi dashi don mun fahinci zance sukai akan kwanan ta,da Hamza,
Shigewa,nayi ina cewa sai ka,dawo ban tsanmanin ya,amsa ba don banji ba,
Da rana ma nice na girka muna abincin rana ga baki yan ganin amarya suna,tashigowa gidan,
Da,dare ma,a gajiye nake don girkin da nai muna na tuwon shinkafa da miyar agushi da naman shanu,
Sai farfesun da,na,sake hadawa nai mai hadi sosai don dai amarya da,ango suci
Bai dawo da,wuri ba, don haka,na zauna yarana mukaci muka koshi ina dan hira dasu don na,ragewa kaina damuwa,
Anan yasamay mu a kasan kafet mun zube muna kwasan girkin mu hankali kwace ina cikin kwalliyan atamfa super,
Yazauna gab damu yana cewa wassh Allah na sanu mukai mashi mukaci gaba da cin abincin mu yana bina da kallon shaawa nai kamar ban san yanayi ba,
Nawa abincin fa naga kina ci da yanki ke nace bari amaryan ka tafito ta,zuba ma kada,na kara laifi,
Sai gata,tafito cikin wani dogon riga baka kamar karan dawa, tsololo da ita a cikin rigar,
Tsayawa tayi tana kallon mu kwaliyar da nayi ne ya,tsone mata ido ita da,take amarya ya dace tayi amma sai gani ni na tsala kwalliya na tsab,
Hamza ya daga kai ya kalleta yana cewa zubo min abinci naci,
Tace mai anan zakaci ko yaya,?
Yace a ina zanci dama,?
Zuwa,tayi saman table ta,debo mashi ta kawo mai tagirke a gaban shi tajuya ta,debo nata zauna sai da,ta cinye plate din ta sha ferfesup din, tai kat,
Na,kwashe kayan da mukaci abinci nashiga dasu nabar su nan falo zuwa wani dan lokaci suka shige daki,
Da safe ban fito ba don na,tanadarwa yaran abinda zasu tafi dashi makaran ta dasafe dama,
Barci nayi sosai ni da mimi sai wani lokaci na,farka,nai mata wanka nima,nayi na,shirya,na fito waje, don mu samu abinda zamu ci,
Samu nayi kayan da akaci abin dare ma ba a,wanke su ba sai da na,dora girkin abinda zamu ci na,wanke kayan,
Muna falo mun karyawa nida mimi sai ga Biba tafito tana wani yatsune fuska take cewa Aisha baki girka muna abin kari bane yau har My yafita bai karya,
Na dago kaina ce Allah ?
Wake da hakkin bashi abinci bake ba don may baki fito kika girka mai ba ?
Au kishin naki ashe har yakai ki fara yi min rowan abincin gidan naki dakike cewa gidan ki ne,
Murmushi kawai nai mata nace aiko gidanane don gidan mijina ne nan,
Jinan bakin ki ya,saba da fadin mijin mu don yanzu ko baki so dole muyi sharing din shi ni dake a gidan nan don haka sunan gidan naki da kike fadi ta,saba da fadin gidan mu,
Kuma bari kiji wanan bakin kwalliyan da kikeyi don satan hankalin shi, gara ma ki daina don da yana da amfani a,gare ki da baije gurina ba ya dauko,
Murmushi nayi nace ya,dauko ki ko kin matsa mai a,rayuwa ba,dare ba,rana kina rokon shi ya aureki,
Kadafa kiga kamar kin shigo kiyi tunanen wai daya,muke dake a gidan nan na girgiza kaina nace har abada,ba daya muke ba biba don sawun giwa yafi gaban na kurawa,
Amma,bazaki gane ba sai in mun zuba ni dake a gidan nan zaki fahince ni, don haka,duk abinda kike takamar kin shigo dashi daidai nake dake a,gidan nan don ni kujera ce daidai da na mai hawan shi,
Hakakikace tafadi a hasale ke har mace ce Aisha nafasan komai don Umma ta,fadamin ke din bashi akayi ,
Niko shi yaganni yace yana so na nace a haka,din yace yana,son ki tace a haka din kuwa,
Nace to yanzu sai agani da yar sadaka da matar zabe ko wa zataiyi winning a gidan nan,
A tunda kin iya bin bokaye da malamai ki raba shi da,uwarshi da yan uwan shi haka zakice to ni nan ban shigo gareki ba,sai dana,shirya maki sosai ,
Na ce ashe kin san wacce zaki sama din duk da yar sadakace sai anshirya ma,shigan ta,
Muzuba dake banza kawai stupid ,,,
Nace ashe baturiya,ce aka dauko ban sani ba zamu sha turanci ke nan,
Ta kada hannayen ta tace ni ba kamar waccan garar kishiyar taki da kika fitar bane da makircin ki Aisha ki dubeni da,kyau ki gani nafi karfin ki,
Nace damay fa da, shigar samudawa ko da,shigar fatalli,
Zaki gane kuren ki wallahi don kina ganin Hamza zaki barshi dani a gidan nan nace tau ai saukin abin Allah yafiki, ko,
Tashige kitchen don neman abinda zataci tanata jinini da zage zage har tagama tafito,
Tun ranan muka,fara zaman kwari a gidan da ita ko sati daya,batayi ba,dashigowa,
****** ********* ******
Tana da kwana hudu da shigowa yace daren yace mu shirya muje gaida Umma gidan ta,
Gabadayan mu minyi kwalliya nida yarana,sai kamshi mukeyi koda muka fito ta kalleni sai ta tsargi kan ta, da sauri naga ta fita zuwa, waje yana bayan ta dauke da mimi,
Gaban mota tabude tashige nafito ina tako daidaya har na iso gurin motan rike da hannun jidda madina tana bayana,
Yana ganin ta a gaban motan yace cikin daure fuskan shi, yace, ke fito ki ba Humaira guri ta zauna nan dago kai tayi tana kallon shi kamar zatai magana sai kuma tai shiru ta bude motar tafita,
Maimakon ta,shiga baya sai naga kawai ta juya ta shige gida, shiko hankalin shi naga mimi da yake ajewa a saman sit,
Sai da,yajuya,don yaga yadda,suka zauna sai yaga bata cikin motan fita yayi a,fusace ya bi bayan ta,
Ya,samu ta cire gyalen ta ta,kwanta yake cewa may kike nufi Biba ?
Ta dago fuska a murtuke tana cewa kai dai zance may kake nufi kana nufin zaka fifita matarkane a kaina,
Kai har kana da matar da zakace wai na fita a gaban mota na bata guri har i a matar take