Showing 255001 words to 258000 words out of 299981 words

Chapter 86 - Sarautar Mata By Makawa

04 Dec 2025

17630

mace kamar babyn roba,
Oh shine kikazo dashi ashe na fifitaki a kan ta kiji dadi don kina yar son kai ko,?
To bari kiji kin dai san sharadin da nai maki kafin na,aure ki, wallahi inkizo ne don ki jagula min zaman lafiyan gida na,ashirye nake da na dauki mataki yanzun nan don bazan lamunci rainin hankali a mace ba ,
Ke yanzu din baki da hankali sai nasa ki a gaban mota Humaira tana baya akan kina yar gwal ko may,
Kuma bari kiji wallahi har in baki fito muka tafi ba yanzu sai dai yau ki kwana a gidan ku,
Yajuya fita dakin a fusace alokacin har nai shawaran nafito kawai na koma ciki nima don har na hau zuciya,
Sai naganshi yafito da saurin shi itama gani nayi ta biyo shi, a baya a raina nace Allah kadai yasan irin lalashi da,yai mata tafito,
Har muka kai gidan Umma ba wanda yai magana a cikin mu sai da mukafita muka shiga gidan,
Suna dakunan su muka fara shiga gurin Umma tana ganin mu tafara washe baki tana cewa maraba da Biba yar albarka harkin fara fitowa ashe,
Hankalin ya gaba daya yana a,gurin biba sai sabari takeyi da farin cikin ganin ta, tana faman gyara mata inda zata zauna,
Nice nace Umma ina wuni daga gefen da naiwa kaina mazauni, cikin dan murya ta amsa min,
Tajuya gurin shi tana cewa kokai fa Baba na bagashi gida ya cika ba yanzu injin kuna lafiya dai ba wani izza ko ikon da,ake gwada maki,
Murmushi tayi tace lafiya muke Umma mun samay ku lafiya cikin murmushi tace lafiya lau yar albarka sanni kinji,
Shima maigidan gaisheta yayi tare da tambayan lafiyan su suka dan fara hira a tsakanin su ,
Mikewa nayi ina cewa bari na,gaida mama dakin ta inda Biba take ya kalla yace tashi kuje mana,
Ta mike tabiyo ni simi simi a,takure mun samu mama tana kidayan kudi tana ganin mu taji dadi duk ta rasa inda zata samu,
Mun gaida ita ko minti uku Biba batayi ba tafito nikan na zauna saman katifan mama dake yashe a,kasa muka fara hira da ita,
Take tambayana babu dai matsalar komai ko nai yar dariya nace babu komai mama tace wajen ita kisharya taki fa,don nagan ta a,tsatsaye,
Nace ita tasani na kwshe yadda mukayi da ita da zamu fito na fada mata mamatace,
Shiyasa nace ki kwantar da hankaliki kibi mijinki da kina,nan kina bori da yanzu ta samu kafar rainaki yadda taso don wanan da kike gani akwai aki saikin jajirce mata sosai za,a zauna lafiya,
Sai da ya dauki lokaci yashigo dakin mama yasamay mu a nan lokacin har yaran sun fara barci,
A dakin Umma kuma Umma ke tambayan Biba in ban mata wani abin take cewa ba komai sai dai shi dake nuna fifici a kaina,
Umma tace tayi hakkuri zatai mashi magana zai daina kuma kada ki fara ki dagawa Aisha kafa don ba karamar makira bace,
Biba tace ai nagani Umma don ko yanzu saida muka kwasa nice da,girki amma wai sai itace zata zauna a gaban mota, tace wanan ma fadine wallahi bari yazo dashi da ita zanci masu mutunci yanzu kuwa,
Min fito zamu wuce muka,shiga sallaman Umma sai cewa tayi babana wallahi kaji tsoron Allah kada ka kama cin zalun yar mutane akan wanan makirar matar taka,.
Umma may akayi kuma yake tambayan ta tare da duban Biba dake zaune a gefe idon ta da alamar tayi kuka,
Ban sani ba tace ban sani ba don may yarinya itace da girki zakace sai wata ta zauna a gaban mota tabarta,
Umma wallahi wallahi bazan wa Humaira wulakanci akan wata ba don nayi sabon aure,
Idan ma,takawo karanane tasani bazata,sa na,wulakanta matata akan ta ba,dama,dashi tazo
Da take son shigowa inane bata tafi ba tana rokon na aure ta kece fa kika,tursasa min nai wanan auren,
Kai ya isa haka don naga kazama,wani zarare akan matar ka zamu hadu,
Ko banza naji abinda,ban sani ba akan Biba dake cewa ni bashi akayi sadaka ashe itama sai da kamun kafa tashigo gidan,




ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABUIDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON HAKA CIN AMANA NE,,,,,,,,


Kamar yadda muka tafi da farko haka muka dawo bai mai magana a motan sai yaran ke dan magana jefi jefi,
Yatsaya bakin shago yai muna sayayya muna zaune cikin mota ba wace tai magana daga cikin mu,
Wallahi yarinya dani kike wasa in har kince baki bari na more mijina yadda nake so nikuma nai alkawarin hanaku zaman lafiya,
Murmushi nayi nace gyara dai kalamin ki kice mijin mu don kin san yana da iyali kika shigo don haka kin makara da kina son more miji sai kije ki auri mara mata ki more ke kadai yadda kike so amma anan ba daman hakan,
Kuma,baki so more miji ba don hanyan da kika dauko wa kanki ba mai dorewa bane gareki,
Tace cikin kuta haka kikace nace kwarai da gaske kuwa don, bai kaiki ko ko ina a hakan,
Shiya shigo motan daidai tana kutawa a she yafada a kunnen shi juyowa yayi da sauri yana kallonta a bayan motan,
A hasale ya ganta ya juya inda nake fuskana da mirmushi kawai yadda ya fisgi motan yasani gane a cikin fushi yake,
Mun shiga gida Madina ta kwaso ledojin a hannun ta na nufi dakina sai naji yana fadi Madina aje karamin ledan kikaiwa antyn ki babban ledan dakin ku,
Da,shiga na dakin nafara cire kwaliya na zuciyata tana tukakin abin da Umma tai muna sai dai yaya zanyi haka Allah ya nufe ni da gani,
Muryan Biba na dinga ji gata dai siririyace amma muryan ta tankar na ganga tana cewa wallahi ni bazan yarda ba ko yau she ka dinga fifita matar ka a kaina ni may kake nufi dani ne wai a gidan nan,
Kaimin wullakanci da zamu fita yanzu ma kuma bai ishe ka ba sai ka nuna mata fifiko kace wai akai mata,babban leda a,dakin ta,
Yace nakai mata daya kuke halan yara nawa ke gareta adakin dazakice dole komai abaku iri guda,
Kai dai kawai kace macucine kai baka iya adalci a tsakanin mu sai ka nuna banbanci,
Yace wallahi Biba tun ranan da kika shigo nai bakin ciki da,auren ki may nagane akan auren ki banza kawai don kin samu nasawa zuciyata hakkuri a kanki har kinga,wurin zagina a macuci,
Akwai macuciyar da ta,wuce ki sai da kika gama watsar da kanki a titi kuka yaudareni ke da dan uwanki na kwaso ki ashe honko kike ban sani ba,
Shiru tayi da taji ya fadi hakan yace, wallahi Biba ki shiga hankalinki ki barni da abinda nake ji a,raina, don kika kara kai karana gurin mahaifiyana ko wani zaki barmin gidana,
Don dama hakkuri nayi na,taushe zuciya ta akanki matata budurwa na,aure ta kamar ki amma ke ashe bazawarar boye ce ban sani ba,
Gidana muna da siri ysakani da matata ba mai sanin may muke ciki amma ke duk kwana hudu da,shigowan ki kin fara tarwatsa min farincikina,
Har ya gama zancen shi banji muryan Biba ba kuma sai sbirun da naji yayi bai kara magana ba,
Karan rufe kofofin su naji hakan yasani cewa Madina rufe muna kofa kinji kaunata,

Washe gari na tashi naiwa yara breakfast na hado nawa dana mimi na shiga dashi daki na saya kofana muka koma muka kwanta abin mu,
Cikin barci naji muryan shi yana cewa bakuyi abin karyawa bane agidan nan,
Na bude idanuwana da sukai min nauyi dakyat ina cewa, cikin fuska mara walwala,
Ina kwana yaya,
Yace lafiya kalau ya kwanan yaran nace Alhamdullahi, sun tafi makaranta,
Yakara cewa nace babu abin karyawa ne a gidan ina son in fita ne don akwai inda zani,
Ka manta cewa matarka ce keda alhakin hakan a kanka bani ba,
Ki fito ki bani abin karyawa na fita zani daji ne, maimakon na tashi sai na mike zaune ina cewa haba yaya, yaya kake son nayi ne wai matar nan taka fa,batazo da zanan lafiya a gidan nan ba,
Yaya zan fita na girka ma abinci bayan itace da alhakin ba ka na girka kuma ta kirani da azzaluma,
Ni wallahi wanan abin ya isheni ya isheni wallahi sai na,sa mashi kuka cikin dan kukan da nakeyi nace ko ina ba dadi ga matsalar Umma ga nata,dawani kake son naji a raina,
Kuka nake mai tsanani saboda bakin cikin da ua isheni a,raina yace kiyi hakkuri Humaira nima wanan abin ya koma min ciki yanzu,
Biyaygan Ummace da suka sakani a gaba kan sai na kara aure kuma na auri Biba wacce ko yaushe tana gurin Umma ita da yan uwan ta,
Yace Humaira ban fayi maki komaiba Humaira ban kuma zalunce ki ba akan auren nan bakuma zan zalunce kiba,
Saboda banyi aure don na gundura dake ba ko kin isheni ni ba nayine kawai don ina son hakan da kuma biyayya, don shi yin aure ai ba laifi bane a gurin Allah,
Ina da halin da zan kar aure a rayuwana don godewa ni,imar da Allah yai min,
Don Allah na roki alfarman ki kada ki biyewa wanan yarinyar kucutar dani a rayuwana, kada kiyi min abinda kika san can da bakiyi min,
Karki bi ta nata ki azaban tani ni da diyana akan zancen ta zan hakkura da komai amma banda wanan hanyan hanani samun natsuwa a gurin ki,
Ki dan yi hakkuri dani kadan nayi maki alkawarin zanyi mai yawa akan ki,
Idan kika dan kawar min da kai kikayi man kawaici na miki alkawarin zanji kunyarki in kuma yita girmamaki a gaban kowa saboda dama ke din maigirma ce da,daraja a gurina,
Yace don haka tashi muje ki bani abinci naci na fita kada na makara ,
Nace idan na baka zai zama matsala a tsakanin mu don bani ce ya dace nabaka ba din,
Hummm yanzu kina ganin idan kun azabantar dani da yunwa akwai wani riba a hakan ke nan yadda kika fara bani abin karaya da,farko kici gaba da yi muna har,sati matsayin ina,gidan,
Ya kamata ki yarda cewa kin fi Biba daraja a gurina son kin san darajana da zafina fiye da kowa a duniyan nan,
Duk da nina ajeku gaba dayan ku nasan halin kowan ku yanzu kuma kin san ina gudun bacin ranki don ina tsoro naga fushiki saboda fushi ki gareni don matsalane fushiki a gareni,
Ina yin komai ko barin komai, don neman zaman lafiya dake Humaira don haka na rokeki karkiyi amfani da damar da Allah ya baki a kaina ki kuntatawa rayuwa na, ki hanani more halal di na akan ki,
Kalamun shi, sun sani samun natsuwa namike a hankali daga kan gadon na dauki kayan break din dana hadamuna ni da mimi nakai mashi falo na aje na,dawo dakina na kara kwantawa, rai a bace ,
Sai da ya shirya ya shiga dakin Biba dake kwance tayi dai dai bisa gado kafa a,ware tana kwasan barcin ta hankali a kwance kanta babu komai, gashi jefi jefi tsaki yayi yace ke ni zan fita ta dago tana wani mika
Yai tsaki ya juya yafita har ta kai kofa take cewa ina son zuwa gida fa yau don na,dubo su kina ko da hankali Biba ko fa sati bakiyi ba a gidan nan,
To shine may ba gidan mu zan tafi ba yace lokacin da ya fara tafiya ban yarda,ba don ni ban son mace mai yawo a rayuwana,
Sai zuwa yamma ya,dawo yake fadin shi zaiyi tafiya ne a yaudin ina jin suna fitina akan wai ko sati batayi ba zaice zai tafi tafiya,
Yace idan na zauna banyi tafiya ba ke zamuci ko kuwa may kike so nayi tunfarko kin san ni ba mai zama bane a gida don haka yanzun ma baki isa ki hanani ba, don haka kada ko fara,ki fita bada izini na ba agidan nan, kuma har inkin fita zan ji a gurin makwabtana don nasa security akan gida na, idan ban nan ko ban gari nasan shige da ficen kowa a gidan nan,
Da zai tafi nake ce mai ina son ranan sati naje gaida su Ummi yace min sai kin dawo amma a kira Ibrahim ya kaiki don ban son hawa masshi kin sani,
Yaba ko wacen mu dan abinda zata rika a hannun ta kafin ya dawo ya kuma,bani na zuwa school din yara,


****** ********* ******
Na shirya ranan Sati na tafi gidan mu wanda nakai kusan wata daya rabon da naje na gaishe su da zan tafi kowacen su saida na daukar mata dan tsaraban da zan kai mata da dan kudi a jakata,
Nasamay su zaune suna cin dumamayn tuwo a guri daya sun tare ni da fara,an su kamar babu hassada a ran su,
Sunyi murna da gani na nashiga dakin Ummi na cire hijjab dina nafito kayan wanke wanken da na samu a gurin wanke wanke nafara tattara na wanke sai albarka suke saka min ,
Sai da na gama na shiga dakin Ummi na dauko masu tsaraban da nazo masu dashi nakaiwa kowa dakin ta nan suka shiga godiya da samin albarka,
Gidan Mama Rahana na,shirya na tafi inda tai min nasiha akan na zauna lafiya da kowa a duniya don duniyan gaba daya ba komai bane a gurin Allah,
Da zamu dawone naga Sa,adatu muka gaisa amma ban shiga ba tashiga tana cewa Umma ina nan cikin uguwar taga na shigo,
Umma ta zaci zan shigo yadda na saba ta shirya abinda zata fada min sai taji shiru har wani lokaci ban shigo
Da yamma nayi sallah la,asar naji muryan Baba ya shigo na tafi na gaida shi yaji dadin ganin mu yake cewa tafiya dai ya kusa ko nace insha Allahu Baba yace ikon Allah,
Sai ki kara hakkuri akan wanda kikeyi Aisha don shi rayuwan duniya nan babu komai a cikin shi sai rikici amma idan ka dauke ta da sauki sai abin yazo maka a cikin sauki,
Da kin bi ta uwar mijiki da ta sakaki a gaba kinyi fushin zuciya kince ki bar gidan da yanzu kin yi hasaran wanan makkan taki koda yake shi bawa ba,a gama halittanshi ba sai ranan da ya mutu,
Kullun shi nake lurar da yaran nan amma sunki fahinta na sai busar duniya suke suna shakar ta,
Nan yai min nasiha nai ta godiya da zan bar gurin shi na kawo kudi dubu goma na,bashi sai samun albarka yake yi,
Na dawo dakin Ummi na nasamu tagyara daki kai Ummina har yanzu dai wanan tsabtar taki tana nan a she,
Tace to haka kawai mutum da lafiyan shi yai ta zama a cikin kazanta hakane kawai zan yi na godewa Allah na,
Tace Aisha dama ina son ganin ki sai dai hakan bai samu ba saboda ba halin naje gurin a lokacin da ake shirin maki kishiya,
Jikina a sanyaye na dago kai ina kallon ta cikin natsuwa da sauraren ta,
Tace ta ya kuke a gidan an kuma,watse lafiya ko ?
Nace Alhamdullahi Ummi komai lafiya kalau, kuma duk lafiya,muke tace Allah yai maki Albarka Aisha, Allah ya saka maki da,alherin sa,
Ya kuma baki hakkuri da juriya rike girman da ya baki nace amin Ummi tace ina nan ina ta fargaban kada ki kasa dauriya akan zarabawan da Allah yakawo maki,
Nace Ummo kamar kin sani don wanan fitinar ta kamar ma zai shaye na sadiya wallahi don tun tana da kwana biyu aka soma,
Ummi tace fita ba tun ta,kima harkokin ki kada ma ki sata a ranki mayar da ita,bakima san tana gidan ba ki kawar da idon ki ga duk a kan al,amarin su,
Idan kiyi haka,sai kiga kamar yanzu komai ya suce anzama daya a gidan
Ke dai kada ki rika kokarin shiga tsakanin su babu ruwan ki da sha,anin su kiyi kokarin kare mutunci ki kawai a,gare su baki daya,
Don haka yafi a ce kin damu da matsalar su kedai kawai taki dashi ne kawai zai hada ku,
Shiru Ummi tayi sai kuma tanisa tace kishi zafi gare shi Aisha in baka,kai zuciya nisa ba sai ka gudu kabar ladan ka a banza wata ta kwashe,
Nace wallahi Ummi hakane don har na fara,biyewa son zuciyana da farko amma da na zauna nai la,akari sai naga kawai naba kaina hakkuri,
Tace ki godewa Allah da ya yakince maki shedan a zuciyar ki inkiyi haka ubangiji zai doraki a kan ta ,
Nan Ummi ta zauna ta dinga bani shawara irin na wanda yafika sanin duniya da mutanen cikin ta
Shawaran Ummi sun min dadi a rai don dama har yanzu bakin Hamza nake gani a zuciyata don kwata kwata,yafita min azuciya ta dama dakewa kawai nake dashi a gidan,
Ummi tai dariya tace kai Aisha may yai maki haka har ya sure maki baki daya yayan naki keda dan uwan ki don hamza tankar dan uwa yake a

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login