Showing 258001 words to 261000 words out of 299981 words

Chapter 87 - Sarautar Mata By Makawa

04 Dec 2025

17647

gurin ki ba miji kawai ba,
Nace ni fa Ummi ko da yake cewa wai harda biyayya yasa shi yin wanan auren ban fa yarda ba don nasan da ra,ayin shi,
Shiyasa ma har na yanke shawaran na kama kaina dashi kawai na fita batun shi nabar shi da amaeyan shi sukarata can,
Hmmm aiko dakinyi haka da baki mashi adalci ba wallahi har da muma na tare dake nace Ummi harda kefa kikace tace kwarai kuwa,
Kina ganin inkiyi haka akwai wani sauran zaman lafiya ke nan a tsakanin ku, kwanciyar hankalin ki fa Aisha shine nawa, da "ya"yan ki,
Nina san babu macen da Hamza zai auro a gidan shi yafita batun ki don ko da yanayi da tun akan auren Sadiya yayi maki,
Nan taita kawo min irin mutuncin da nace yai min tace kina ganin da,watace zai iya cewa yarinyar tafita a gaban mota tabaki guri ki zauna a gaba tare dashi,
Allah kadai yasan namijin kokarin da yayi gurin yi maki wanan yakin ga kuma uwar ku iri n yadda yai mata saboda taso aci maki mutunci tun farko,
Mun yini a gida sai da magariba na koma gida nazo wa yara da abinci don nasan ba lalai bane mu samu abinci a gida,
Mun shigo muna sallama amma,batafito ba duk da,dazan tafi saida nai mata sallama cewa, mu zamu gida mu, mu gaida su,,,
A haka mukai ta zama ni da ita a gida kowa yana sha,anin shi ba ruwan wani da wani kowa harkan gaban shi kawai yake yi,
Ya bugo min waya,kaman yadda ya saba cewan yana tafe banda gobe don haka nasan nice zan karbeshi sai na hau shirin tariyar shi,
Ban ga tana wani shiri yadda muka saba ba sai al,amarin shirmayn tara kawaye da takeyi ai ta ihu da sowa a dakin,
Nai girki na gyara gida tsab don itama irin Sadiyace bata aikin komai a tsakar gida Madina ce mai gyaran main falo din gida duk yamma, da sauran part din gidan,
Shigowan dare yai muna ina zaune falo da yara mukaji ana,shigowa da kaya bai samu shigowa,ba yana waje na tura Madina ta fada mata maigidan yadawo,
Madina na,shiga dakin tace ke may yakawo ki dakina ko kin zo zuba min barbadin maganin da kuka saba yi ne,
Madina tace Antyna tace nazo na fada maki cewa wai baban Jidda ya dawo,
Tace yadawo cikin mamaki to tafi naji tace wa yarinyar tafito tana ce min wai taji tace,
Ya shigo yana saye da yan kanan kaya ta maza a jikin shi tieshirt fara da bakar wando sai kamshi yakeyi ya koma kaman saurayin da bai taba yin aure ba,
Sai faman sannu da zuwa muke mashi tafito daga daki ganin irin kwalliyan da nasha sai faman sheki nakeyi da,annuri, taja tai turus,
Wani irin kishina ya,turnuke zuciyan Biba a,sanyaye tace mashi sannu da,dawowa sai na nufi inda yake na karbi jakar dake sabale a kafadan shi,
Bina tayi da kallon irin tafiyan da nake kamar wata,tarwada, a kasa, cikin dan rusunnawa nakarbi jakar daga hannun shi,
Na nufi dakin shi dashi dakata Aisha inji Biba ta tako inda nake tsaye na juyo ina kallon ta,
Amma dai kin san a,dakina yake ko naga kina son shiga hakina ban yi magana ba illa murmushin da nai mata kawai,
Yace kamar ya a dakinki nake kwanan na tafi kwana nawa ake a dakin budurwa tace da sauri sati guda nace yau kwanan ki nawa a gidan nan,
Tace goma,sha, daya yace tau hakakikayi ne ko may ke damun ki da,zakice wai kece da girki ita Aisha ke nan ba mace bane,.
So dai kake ku cuceni kaida ita,amma ya kamata a ce nayi kwanakina a gidan nan na kare satina daya daya dan,na biyyo ka bashin kwana biyu a,baya katafi,
You are very stupid Biba are you out of your sense, ? or you have gone crazy ?
Ya juyo inda nake yace shige min da kayana,ciki wanan batazo da zaman lafiya a gidan nan ba,
Amma zan yi maganin ki very soon tace mu dai yi maganin juna ni da kai don nagane ku macutane dakai har ita,
Ya ce tau mu zuba mu gani tunda baki da kunya,wallahi sai na,gwada maki Hamza nake ina fadi kina fadi ,
Saida na hada mai ruwan wanka nafito daga dakin nazo na,shirya mai kayan abinci, a table,
Dakina na,shiga kafin yafito na kara gyara kwalliya na da kyau yafito yana kamshin turaren da ya,sa THE,,,
A falo yai sallah duk muna zaune daga ni har ita tana cika tana batsewa, taki shiga ne ina gani don kayan tsaraban dake ajiye tsakar falon a cikin ledoji,
Sai da yai sallah ya fara cin abinci ya dan yi nisa yaran na kusa dashi suna mashi hira yace Humaira bude ledan nan ki basu tsaraban su,
Haka yake idan yai tafiya da wuya ya,dawo bai sawo wa yaran tsaraban wani abuba wanda haka ke kara jawo mashi kauna ga yaran shi haka kuma in ya,fita komai dare sai ya,sayo masu wani abinda zasu ci,
Takalmomi ne na,yara, harda Madina ta samu sai kayan wasa irin su jirgin kasa da mota suka shiga murna da ihu kowa ya dauki nashi abu gudane bai sawo masu shine abu mai siffan halittan abu mairai don Jidda ta damay shi ya,sayo mata babyn roba yace a,a gwagona malaikun rahama basu shiga gidan dake da abu mai siffan gunki don haka kiyi hakkuri,
Sauran kayan cine da,sha a cikin shi yace wannan na amfanin gidane kowa ya ci,
Biba tai farat tace to a,raba,mana kowa ya,dauki na shi, ba,wanda yai magana, kamar ba,zai tanka mata ba,sai yace Ok, kasa su kashi bakwai kashi kashi daya abawa maigadi kuda yara ku kwashi kashi guda guda sauran kashi daya ku sa min a,dakina,
Tace harda yaran da,maigadi za a kasa daidai dasu yace wani yafi wani baki ne a cikin mu,
Shiru naga tayi yace taso ki kasa mana kowa ya kwashe nasa rabon bashi ke nan ba,
Kamar bazata tashi ba sai ta mike jiki ba kwari ta,shiga rabawa a hankali shiko ya tsure ta da idanuwan shi har ta gama yace ke Madina dauko abu ki kwashewa maigadi kikai mashi a,waje,
An fitawa maigadi dashi yace min tashi ki kwashe naki na zabi kashin gabana yace ta dauki nata ta dauka yace Madina kwashinaki dana yaran ki ta hada nata dana yaran nace zoki hada da nawa kikai muna store din mu,
Sai gashi nawa yai yawa kamar duk kayan da ya,shigo muna dasu ne gidan murmushi mugunta nayi nace ance in zaka gina ramin mugun ta kagina shi ya zam gajere,
Simi simi ta mike tana kwashe nata tana cewa ashe a kwaita kuwa don bazan yarda da haka ba wallahi, yaja tsuki naga ya jawo wayan shi yana magana,

Nakai yara daki nace dare yayi duk da goma saura nace kada su makara zuwa school da safe, sai da suka kwanta,naga barci yafara kwasan su na fito,
Tunda ya,gyara dakin shi yaune rana na farko da zan kwana a dakin tare dashi, tsab nagyara jikina yadda ya kamata,
Babu kowa a falon na kashe duk wasu na,ororin wuta dake falo da tsakar gida,
Nashige dakin maigida da sallama na,ashe duk abinda nake tana tsaye bayan labulen ta tana kallo na tace shegiya mai suffan yan ruwa, tasake labulen waya ta,dauka da,daren nan takira uwarta tana kuka tana sheda mata karya da gaskiya,
Uwar tace wallahi habiba ki bi a sannu komai asannu ake aiwatar dashi har yaushe kika shiga gidan da zakice dole sai dokanki za,a bi,
Wallahi ki rufa min asiri kin dai san irin wahalan da nasha kafin ki shiga gidan nan,
Shine yanzu mun samu kike son ki ja min gori a gurin kishiyoyi da makiya nawaje in kin kashe auren ai sai kizo ki zauna ga dakin nan mu dinga gwada tsawo dake a ciki,
Tace amma mama ,,,,, rufe min baki wawuya,mara,hankali haka nace maki kiyi idan kin tafi ko kuwa,?
Bataji dadi ba ko kadan a,wurin uwarta dake ganin samu da,rashi a lokaci guda yarta na son ta ja mata hasara ,

****** ********* ******
Yana zaune a bakin gado da yar computer shi yana duba nashigo dakin ina tafiya,kamar wata queen of ocean,
Abinda yakeyi ya bari ya kura min idanuwan shi har na,iso gare shi yace Rangida har kusa binki wallahi na zaci bazaki shigo bane ai,
Nace kabini sai kace nice amaryan taka wanan muka min ai sai amare, ke dashi,
Tsuki yayi tare da mika min hannun shi alamar inzo gareshi yace nidai zonan ki zauna na shaki kamshiki da nai missing for long,
A zuciya na nace wani sabon sallon yaudara ke nan irin ta maza wanda ya kwana nawa da,wata matar daban zai min wanan dadin bakin,
Nazauna gab dashi yarufe system din shi yana cewa ai ba,wata amaryan da zata yi irin amarcin da kikayi a guri na Humaira,
Kece fa kika fara bude abinki ga leda kika koyar dani duk wani zumar dake cikin diya mace tun kina kuka har kika saba da,kwazabana,
Yanzu wace mace zan samu kamar yadda na samay ki Humaira bayan kece matar da tasan dadina da,wuyana, a,duniya
Ni har gobe a gurina ina iya nunawa duniya ba wata bayan ke wallahi agaban kowa kuwa,
Ki sani Humaira wallahi zan iya barin kowa a saboda ke sai dai kawai kunata tamu irin na mazane zanje vurin wata amma badon na gamsu da abinda kika saba min dashi ba,
A ko ina a gaban kowa ina fadin kice farin cikin rayuwana don har yau babu wanda zaice yaji a tsakanin mu,
Haka yai min dadin bakin maza har ya kara,karyan min da zuciya na bashi kai bori ya hau yai yadda yake so dani a cikin gidan,

Zancen tafiyan mu ya taso sai don haka banda sahran zama a gida sai sintirin shirin tafiya,mukeyi,
Umma tazo gidan tana zaune a falo nazo na gaisheta take cewa ashe ina da mutuncin da za,a gaishe ni shine kwanaki kika tafi uguwar mu kika ki shigowa gaida mu ai idan baki shigo ba ki turo min jikokina na gaidasu tunda ba jikokin Fatima bane ita kadai,
Murmushi nayi kawai sai Hamza ne ke cewa haka akayi Himaira Umma tace ai gata zan mata karya ne,
Nace ba haka bane Umma bance mashi zan shiga gurin ki bane iya gidan mu na roka zan tafi,
Eyyeh su biyayya manya ashe zuwa gauda mu din ma sai an bada umurni ake zuwa,
Wai ina yar tawa take ne banga giccin ta ba tun da na,shigo gidan ko bata nan ne wai,
Nace wa Umma tana ciki bari na fada mata kida na tashi kamar kullun a dakin, na shiga da,sallamana,
Nacce amarya Umma ce ke gaishe ki a falo tashigo yanzu,
Waye Umma tace cikin yatsune fuskan ta, nace Umman dai da kika sani ta maigida, najuya nakai kofa naji taja tsaki nace a raina kunfi kusa,
Bata fito ba yadda nai tsanmani sai zuwa wani lokaci tafito fuska,babu walwala ban san may yasaba duk ranan da tai girki haka take wuni rai a bace a gidan,
Nakawo wa Umma ruwa da dan abin tabawa sai ga Biba tafito daga dakinta fuska a daure, cikin malalaciyar murya tace, Umma kece ina wuni a,tsaye kerere,
Hakan baisa Umma fushi ba,sai washe baki takeyi tana cewa ,a,a,a Habiba, kuna lafiya yanzu har nake batun na shiga dakin ki ai mu gaisa,
Kitchen na,shiga naci gaba da aikina koda nafito Umma ce ita kadai a zaune a falo sai tv dake aiki,
Nace sannu da zama Umma, tace yyawa kawai na,shige daki abina don yara suna islamiya a lokacin,
Yadda Biba ta shige nima haka na,shige nawa daki muka barta nan zaune a falo,
Shiru shiru ba,wanda yafito daga cikin mu sai zuwa ajima kadan nafito tana gyangyadi jin motsina datayi tabude idanuwan ta,da,sauri,
Nace a Umma kina nan zaune na ai nazaci kin shiga gurin Biba ne don naji kina cewa zaki shiga,
Tace a,a ina nan Habiban ma naga tafito kaman ranta a bace yake bari dai na,shiga naji abinda ya faru,
Tamike tashiga dakin Biba da sallaman ta take cewa ashe kin kwanta ne biba tace mata eh batare da ta mike zauna ba Umma tai wa kanta mazauni a dakin tana cewa ,
An maki wani abin ne Habiba nagan ki wata iri yau,
Biba tace may kikagani lafiyata kalau ba komai yasa tace haka ba sai gargadin da Hamza yai mata akan Umma din,
Shiru dakin si Umma tace injin wanan makiran batai maki halinta nasu na makiran mata don wanan yarinyar da kike gani sai kinyi da gaske a kanta zaya barki ki zauna gidan nan lafiya da mijin ki,
Biba tace wa wai Aisha daga inda take kwance tace ni banda matsala da ita don ba ita ta ajeni ba a gidan,
To ai shi nagani haka kuma nake so wayan da aka bugo mata ta dauka ta,share Umma nan a zaune ,
Ganin bata samu yadda take so ba sai tafito daga dakin ta na kada kai kawai,
Nan falo ta,wuni ita kuma Habiban bata fito ba tana ciki abinta yana dawowa take cewa ya,kaita gida,,
Daga kofan kitchen na leko ina mata sai anjima a hanya take cewa wai ko Hamza amaryan taka kanta daya kuwa
Dariya yayi sosai yace Umma may kika gani ne ko tai maki wani abin ne tace a,a gani nayi dai kamar bata da kunya yarinyar,
Murmushi kawai yayi bai mata magana ba har cikin gida ya rakata acikin gida takecewa itama Aishan yau sai naga tana min wani gani gani a idon ta ,,
Yace Umma aiko hakan ba halin Aisha bane don kin san halinta ai,

Washe gari su Zarah suka shivo gidan tana jin su taki fitowa sai sune suka shiga inda take suka gaisa Asmau ke cewa kinajin mu Biba kin ki fitowa mu gaisa tace yanzu ba gaku kun shigo mun gaisa ba ina kun san dakina,
Suna falo muna hira da dariya tafito ta dauki ruwa a fridge Zarah tace ke baki ko zuwa ayi hira, dake,
Tace in nazo goya ku zanyi komay banda lokacin fitowa ne shiyasa don ban son damuwa tashige dakin ta
Ido suka bita dashi suna mata kallon mamaki sai dai basuyi magana ba,
Asmau tace ashe akwai aiki samun gurin har ya fara aiki ashe bamu da labari,
Ranan laraba muka kwasa sai hajji cam muyi sallama da kowa a gari yan uwa da abokan arziki Biba taki fitowa sai zuwa can ana ina take ina take sai ta leko tana cewa zaku tafi kenan Allah kai lafiya ta juya ta shige dakin ta,
Nikan nasan halin sune dai abin yazama wani banbarakwai don ba haka suka saba gani ba a gidan,
Angama komai mun daga zuwa kasa mai tsarki nabar yarana da madina zasu zauna a gurin mama Hafsi da zata dawo gidan gurin su har in dawo,
Hamza ya rasa zaune ya rasa tsaye da zamu wuce damuwa karara a fuskan shi,
Mun dan kebe yake cewa wallahi sai yanzu nake da na sani na rufe ido mu tafi nace ai babu komai ga yaya Ibrahim dasu zarah yai murmushi yace baki ganewa ne Humaira nace ka kula min da kan ka da yara a gida,

****** ********* ******
Nayi gaskiya gurin zaben mama ta zauna a gida ta kula da yara har in dawo don nasan zasuyi daidai da Biba fiye da kowa,
Aiko tafiyan mu da kwana biyu sai tafara batun takurawa Madina wai ta,dora masu girki tayi shara ga aike,
Sai mama ranan tace ke bazatayi ba yarinya karama haka duk kin takurawa rayuwan ta keda kike matar gidan idan bazakiyi ba sai ki bari bata kara komai a gidan nan dan dama aike ko shi ba nisa ba,
Nan ta zage tana son yiwa mama rashin kunya mama tace ke wallahi nafiki zama yar barki idan ma danbe sai ki fito muyi shi mu cashe yar iska mara kunya ni ban neman komai a gurin ki don ba don ki nake a gidan nan ba,
Abincin ma idan bazaki girka damu ba ki barshi zan iya muna nidasu, basai kin bamu ba,
Da ya,dawo ta,sashi a gaba wai mama ta sata,agaba ya samu mama yana tambayan ta may yafaru nan mama ta,fada mashi yadda sukayi da kuma yadda tafara hattaran yaran,
Yace look Biba gaskiyan mama don koni bazan yarda,da,wanan akidar taki ba,ashe da gurin su nabarki bazaki iya rike min su ba,
Tace akan may ma zan rike su tunda suna da kaka kaisu gurin kakar su mana, su zauna,
Mama tace ashe baki da kunyane haka ni dama nasan ko yanzu tsugune bata kare ba yadda na gan ki da gani baki samu tarbiya ba tun a gida,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login