Showing 261001 words to 264000 words out of 299981 words

Chapter 88 - Sarautar Mata By Makawa

04 Dec 2025

17690

Wallahi nikan kada a zagar min iyayye don bazan yarda ba gaskiya tunda iyayye basu fi iyayye ba,
Biba ki shiga hankalinki wallahi don zanyi matukar saba maki yanzun nan ranki zai matukar baci,
Taje bakin ta tai shiru don ta hango masifa idanuwan shi tasan yanzu da ta muda zai iya bata mata rai yadda yace din
Tamike tawuce dakin ta tana guna guni ya juya gurin mama yana cewa mamakin ga kuma abinda na kwaso wanan karo,
Mama tai dariya tace duk cikin jarabtan bawane da sannu zata gyaru tunda baka daga mata kafa idan tayi,
Matsalar har yanzu a gurin yaya yake don naga har yanzu bata fahinci halin yarinyar ba ina gudun a maimata abinda ya faru a baya,
Bayan kwana biyu ya shirya yai tafiya saida yabarwa Umma abida zai ishe su a hannun ta don yasan halin kayan shi,
Nan sukai ta gogawa da mama a gidan ba sanya ko kadan a gurin mama tai girkin ta iya cikin ta mama tayi ita da yara tun da madina ta nuna mata yadda ake amfani da gas,
Bai dawo ba sai bayan sati biyu yana can ya ketara kasashen ketare yana harkokin shi,
Biba tacika tacika ta batse sai waya take mashi nacin mutunci wai don yaga matar shi bata kasan shiyasa ya tafi ya barta ita kadai a gida,
Har ya kai ya daina daukan wayan ta,sai in shi yaga damar kiranta don kan shi,ya kirata din,
Ranan da ya dawo tai girki ta sawa su mama takira madina wai ta dauka takaiwa mama can sai ga mama tafito da kullan a hannun ta tace bar abinciki Habiba don yau yana gari zaki bamu abinci,
Mama kin fara kulla min sherin ki ke nan ko don kinga shi ya dauka da gaske ne,
Fayauuuu ya kwashe ta da mari saida ta dafe goshin ta sai kuka tace kin kai ga yadda kike so dama an hada baki dake ne ki zauna don kiga bayan aure na,
Nabar maki gidan ki zauna ya aureki idan natafi,
Ta shige daki tana dauko gyalen ta tana kuka tabar gidan ko minti arbain batayi ba akadawo da ita uwarta da kanta ta taso tagaba tun kowa bai sani ba ta dawo da ita ta bashi hakkuri,
Sai uwar kece wa mama babba dai yasan ya girma tunda yaro zamani sai da hakkuri,
Yace mama idan kizo fitinane ki kwashi yarki ku tafi uwar na,fita gurin Umma ta tafi nan Umma ta hau ta zauna tun safe tashigovta samu mama da jidalin masifa
Saida mama,ta,gwadawa Umma bata tsoron ta Biba tagane mama,fa,ba kanwar lasa bace bari ta sauko a zauna lafiya tun lokacin ta rage iskancin ta a kan mama,




ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABUIDAN BAKI BIYABA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON HAKA CIN AMANA NE,,,,,


Haka muka zauna da da Asmau da dadi da,wuya duk na hade su na shanye a raina nake nuna ba komai a fili,
Sai dai shi ya fahinci ina fama da hakkuri daga Biba har Asmau din daurewa kawai nake ban gwadawa kowa don a zauna lafiya,
Biba yanzu tana ganin ta kai ai gidan mijin tane sai abinda taga dama tayi ba takura ankawo tane an kawo ni nima, don haka,ba maima wani ikon don duk bori guda mukewa tsafi ni da ita,
Sai ta dauko yi min abu gaba gadi ,gidan komai a,wullakance takeyi shi,
Hakama yarn,tasaka,su a gaba,sai zagi da,duka tin ina,sharewa har takai na kasa hakkuri da dukan da,takewa yarna ko agabn uban waye haka,zata,doke,su kota,daka masu tasa sai sun gigice don masifa zafin dukan da take masu,
Ranan gaba daya,muna zaune falo sai Jidda ta dauko ruwa a cup taje ta,wuce tafadi ruwan ya zube ji kake tas,da mari takuma kara aza mata rankwashi a ka,
Nace haba Amarya wannan dukan aiyai ma Jidda yawa ga mari ga,rankwashi,
Ko zaki rama matane don dama ance idan an doke su fada kike yi kamar zaki cinye mutum danye,
Nace ai ban san da gaiyya kika,doke taba tun farko tacd da kin rama mata ke nan ko,
Sai naga yanzun ma baki makara ba zaki iya rama mata in kina,so,
Tausan zuciya na nayi don irin yadda take mi magana a cikin gatse da,rainin hankali,
Nace ba wanan karon ba amma tunda na fahinci da,gaiyya kike dukan su muje zuwa gobe ma rana ne,
Nan tafara zuba magana yawanci abubuwan da akayi lokacin bata gidan sai nai mamaki ke nan komai an fada mata a kaina harda karya da,gaskiya,
Tamike tana cewa inda ma ba diya mata bane har kikewa mutane wanan salon a kan su nace nagodewa Allah daya,bani su ke ai sai kizo ki shiga haifa mashi tagwaye agani ni kuma na rike yan matana,
Daidai lokacin Asmau dake barci taji yayan yai yawa tafito taji komai sai take cewa haba Aisha may yakawo hakane wai ki daina shiga harkan wanan matar don ita ba zaman lafiya yakawo taba gidan nn don bata da gwani da kowa yin fadan takeyi,
Sai ga Biba ta kara lekowa tana cewa, mace dai ta iya bakinta don in kin isa ki koma gidan mijin ki mana ki samu daidai dake a can,
Har ya kai sai da maigidan ya,dawo Asmau ta kwashe komai ta fada mashi ya kira mu gaba dayan mu har Asmau a falon
Saye nake cikin wani dogon rigar material green color, na dan yafa dan kwalinshi har wuyana
Ita ko Biba wasu atamfane daga cikin kayan auren da yai mun su take sakawa ni ban ko fara dinka nawa ba a lokaci
Sai Asmau dake saye da dogon riga baka dake jikinta tun safe dashi ta,wuni a jikin ta
Yai gyaran murya yace yana son yaji may ya kawo cacan baki dazun a gidan nan, gaba dayan mu shiru mukayi ba,wace tai magana sai da ya kara nanata tambayan shi shine ita,biba din tace cikin hasala,
Wai dan kawai na bugi Jidda shine uwarsu take son gaya min magana akan hakan
May tayi kika doke ta ke yatambaya yana kallon ta don son jin amsa daga gare ta,
Ruwa ta zubar a nan ta nuna mashi gurin yace da gangan tayi ko kuwa ina son in sani ,
Shiru tayi don tambayan tashi yafara kureta a lokacin jin tayi shirune yasa shi cewa tambayan ki fa nakeyi Biba,
Shiru tayi sai ji mukayi Madina tai farat tace kafan anty Biba ne ya yarda ita,
Yadago kai ya kalli biba din itama biba kallon Madina takeyi yace haba Biba sherin makircin kishin ku kuma har da yarana kuke hadawa yanzu,
O makirci ne ashe kai ma zaka goyi bayan kada nai wa yaranka fada ke nan ashe, kamar yadd ita uwarsu tayi,
Look Biba idan kuna abinku kuyi shi a tsakanin ku amma bazan lamunci duka harda mari ba ga wanan yar karamar yarinyar kamar Jidda,
Yanzun dai kawai, kace min bakin ku a hade yake kenan anzuga ka kaci min mutunci,
Wai Biba ke wata irin bahaguwar yarinya ce sai ana magana ta gaskiya ki dinga kokari juta mutane,
To tsaya kiji wallahi daga yau sai yau zagi ko duka akan yara na nakashe shi a gidan nan,
Ga Humaira nan ita tahaife su amma ban daukan mata duksn yarana don tagwada itama batasha da dadi ba,
Haihuwace dai ake min gorin shi a gidan nan nima Allah ya bani yace dayafi maki sai ko doka yadda ran shi yaso amma ita kibar dukan mata diya tai magan kuma ki mata cin mutunci, to bazan dauki hakzn ba don duk nakara ji rai zai baci wallahi,
Ta mike tana cewa ki sani kuma ki rike duk randa na haihu a gidan nan bake ba,da na wallahi,
Nace Allah ya kawo muna su yasa masu albarka ne Asmau tace ba amin ba a ha kali,
Nan ta barmu tashige tana zage zage wai duk yadda za,ayi aga tayi fada da mijin ta shi ake kokarin yi itako wallahi zasu zuba ne da kowa a gidan,
Asmau ta sauke ajiyan zuciya tace wanan si wani matsalane kuma aka jajibowa mutane don wagga mace ba matar rufin asiri bane wallahi,
Shiru yayi bai ce uffan ba sai magana yake da mimi dake a jikin shi tana surutu,

****** ********* ******
Sannu a hankali nake lurar da Asmau akan al,amarin duniy duk da nima ba wani waye wa nayi ba amma nasan nafi Asmau sanin rayuwa,
Sai dai kuma wani sabon matsalar da yake kunnu kai shine yawan fitinan da Zarah ke samu da mijin ta don yanzu baida hali irin na da ya samu kariyan arziki sosai,
Abinci ma yanzu sai da kyat suke samun shi yadda ya kamata sai tazo gida anbata gashi tana dauke da wani ciki a jikin ta,
Wanan dalili yasa Zarah ta tayarda hankalinta wai ita fita zata yi gidan bata iya zama,
Mijin yana matukar son ta amma taki kwantar da hankalin ta sai yawan fitina sukeyi dashi,
Ranan da yani wanta yana gari yazo ya samu hamz don akirata a tsawata mata,
Ranan Umma tai fada sosai tace may yake nufi haka zata zauna da yunwa ga ciki a jikin ta da may zataji,
Hamza yace ,a,a Umma mutumin nan fa bai cancanci wanan sakaiyar daga gare ku ba gaskiy don lokacin da yake dashi ya taimaka maku sosai,
Umma tace makka ya kaini ko gida ya gina min hamza yace babu ko daya amma dai kunci alherin shi sosai,
Yace gaakiya Umna kada kiyi wanan magana a gaban Zarah don kamata yayi ace an tsawata mata tunda yana son ta,
Biba dake jin su tace amma Umma gaskiya baki tunane ba kamata yayi faki karfafa mata,gwiwa ta zaun a gidan ta gawata saboda rashin hali tafito shine kuma zaki kara ba,wata damar fitowa,
Umma tace Habiba ashe kafarki har ya kama kasa ahaka kike fada min magana yadda,ranki yaso
Ke kina da halin ne da ake zaune dake ko don ya zama abinda yazama shi duk yadda kashi yake yana iya shakarshi,
Babi da tasan hhalin Umma a kan diyanta da bata,tanka masu ba datai shiru yadda nai shiru ina sauraren su,
Umma ni nafi karfin banza a wurin shi tunda nasan nafi diyanki halin kwarai wallahi,
Eh lalai ashe kuwa abinda ake fadi gaskiya ne don gashi yau yakawo gareni,
Bari kiji duk fa abinda kikeyi nasani ido kawai na,sa maki ba,wai kinfi karfi na bane,
Yaran nan ko zuwa sukayi da koken su gurin dan uwan su sai kin san yadda kikayi ki kai suka ya hana masu
Biba tace wa wai zancen Jibrin kike yi yanzu kato kamar Jibrin zaice wai sai an bashi kudi shi bai zuwa ya nemo nashi,
Indai don nace bazan fadawa yayan shi bane yaje yafada maki to na hana din,
Lokacin Hamza yafito daga dakin shi yake cewa ke wai yaya hakane may nene wai haka kuma,
Umma tace barta barta kawai ta nuna min ita kyankyasan injin ne, umma ai kyankyasan injin suna da yawa a duniya bani kadai bace,
Ke wallahi yanzu tanki zai baci waike mai yasa baki da kunya Umma ce kuma kike ,sa,in sa da ita,
Ni ba sa,in sa nayi da itaba ai magana ne kawai tafada min na fada mata sai kuma ace nai sa in sa da ita,
Asmau tafito tana fadin wallahi in kika zagar min uwa yanzu sai nai maganin ki Allah,
Gurinki tazo ko dake ake magana da zaki sawa mutane baki kin fi Aisha ne da bata tanka bakin ta ba a cikin maganan manya,
Ke ki dai ji da haushin mijin ki da ya mayar dake bazawara kawai anzo an cika wa mutane gid da kashi in aure na da dadi jeki zauna dakin ki mana kibar wa mutane gida,
Umma ta juya inda Hamza yake tsaye cikin takaici tace kana jin abinda take fadi ko yace naji ta Umma laifin wa kuma,
Aina fada maki nayi bincike akan ta tun farko kikace min Umurni kika bani yanzu ni yaya zanyi akan umurnin ki nake ai,
Biba tana shiga daki ta kunna gida sauti yana tashi da karfi ta mayar dasu banza,
Na,shige dakina na barsu nan suna ta maganganun su nace ai kun fi kusa akan Biba ba irin cin fuskan da Umma batai min a gaban ta saida tai kokarin cusa Biba a zuciyar Hamza tazama wata a ran shi,
Yanzun ko gani take daidai take da kow ba yadda za,ayi da ita sai dai kallo kawai don a ganin ta tunda mijinta yana,son ta Umma bata isa ta sa shi yai mata wani abuba,
Kun san yanzu mace idan taga,wuri sai taga kamar ba,wanda ya isa da ita a dangi kaf,
Umma ta tafi da mamaki a ranta bata taba zaton rashin mutuncin Biba yakai haka ba,sai yau da tai mata shi,

Bayan kwana biyu Hamza ya samay ni ina saye da dogon riga na dinkin kasar Dubai mayafin rigar na yafa a kaina ,
Ganin ya shigo dakin yasani fuskan tan,shi fuskan shi da yanayin shi akwai damuwa sosai a cikin sa,
Na tsura mashi ido har ya iso inda nake zaune shima zaman yayi tare da,furzu iskan damuwa daga bakin shi,
Yayana may kuka ke faruwa nagan ka a damuwa yace cikin yar murya wallahi Aish al,amarin yaran nan ne duk ya daure min kai,
Suna abinda ba daidai ba amma Umma bata bari a fadi sai ta tare da wasu hujjan ta na daban,
Yanzu dubi yadd bawan Allah nan duk ya rikice akan yadda Zarah ta tayar mai da hankali lokacin da yake dashi suna ci waji su a gatin nan ,
Amma yanzu don Allah ya jarabe shi shine zasu juya mashi baya suna batun kashe shi da ran shi,
Jiya fada dare yazo min hankali a tashe wai gata can tana fitina da uwargidan shi a kan ruwa,
Nai murmushi nace ni wallahi ban san bata da,wayyo ba,sai da haka ta kasance Alhaji Bala bai ci tai mashi wanan sakkaiyan ba gaskiya,
Nace kabari gobe insha Allahu zan tafi gidan nai mata magana ko zata ji don abin gaskiya akwai daure kai sosai,
Yace gaskiya haka ya kamata ayi don in har ta bari auren nan ya mutu sai na,saba mata fiye da tsanmanin ta,
Haka ya tashi gwiwa babu kwari ya bar dakin naw cikin tafiya kamar baida lakka,
Dakin Biba ya shiga yana mata sai yadawo tana daga kwance take cewa yaya zancen kudin da ta tambaye shi wanda zata kai gidan su ana buki sunan babban yayan su sati mai zuwa,
Yace waike baki da zance ne kullun dai na abaki kudi kudin nan fa idan bidan su na da,dadi a kashe ke ma ki tashi ki nema mana yadda yar uwar ki take yi,
Don na tambaye ka kudi shine zaka kawo min gori ita Aisha wa yabata kudin da,take sana,an bakai ba may take dashi ko gidan su may suke dashi da take tunkaho,
Don ka,rike mata kan maciji tana wasa da bindin shi ko waye bai san abinda akeyi ba agidan don na barku da Allah kawai yai min sakaiyya,
Kallon ta yayi da mamaki yace ashe kina da aiki in zarginki ke nan in ma baki sani ba yau ki sani cikin bata da komai gidan su basu da komai itace sillar samun arzikina,
Tace a wulakance ita Aisha din kuma wata sabuwa ke nan inji yan caca, busa ke nan sai a fadawa su kaji,
Bakaji zan fadawa ba ke zan fadawa don ko duk kudina naba Aisha taci taci su gaba daya don da kudin ta nai arzikin dakika zo ci,
Don nagane ba don Allah kika aureni ba don hangen abin duniya kika aure ni,
To ban maki alkawari baki kudin zuwa buki gidan ku ba idan ya taso don itama banine ke bata ba,
Bamu iya mu gane wanan kuma sirina ne koke don ki fitar da zargi na fada maki, don ki sani,
Yafita don ya san in ya tsaya kara bata mashi rai zata yi a banza kawai,
Kamar yadda nai mashi alkawari zuwa gurin zarah haka nayi don washe gari na,shirya ni da mimi sai gidan su zarah din,
Na samay ta tana wanki saidai wanan karon ban samu taron arziki yadda aka saba ba a wurin kishiyoyin ta don a tsatsaye muka gaisa dasu,
Tace a,Aiaha ce yau gidan ko batar hanya kikayi ne wai nai murmushi nace aiko baki fada min haka Anty Zarah don kin san ina zuwa gidan ki,
Tace da ke nan ba yanzu da kika zama matan manya ba kin zama hajiya matar Hamza yaro,
Nace haka dai kika ce Anty mun gaisa tare da tambayana mutanen gida nace kowa lafiya
Nace ina Alhaji Balan ki sai ta bata rai tace Alhaji balan su dai nace haba anty ke da Alhajinki hakkuri fa zakiyi, da abinki,
Tace wallahi Aisha wanan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login