Showing 264001 words to 267000 words out of 299981 words
mutumin yafita min arai ace mutum ya zauna gida bai fita ya nemo sai dai a bashi ya,soke kawai,
Haba Anty Zarah ki tuna fa da yake dashi ke da bakin ki kike fadin ko baiba kowa abu ba yana baki ,yana fa hakane don yana sonki yaga ke ce karama baki da manyan diya dashi,
Tace ai su ma yana basu din don da basu zauna ba ai a lokacin dadin bakin mazane kawai yake min,
Tau koma dai may nene kiyi hakkuri don hakan da kikeyi mashi sai kishiyoyin ki suyi maku dariya,
Tace suyi mana in naji sai muyi tsiya da mace wallahi,
Haba anty zarah in fa kin kwantar da hankalinki ko da kike ganin baida zai baki abinda Allah ya hore mashi,
Haka dai kike gani nace haka din ne ma anty don Allah kiyi hakkuri shifa talauci ba mai dorewa bane baki sani ba ko Allah ya kara azurta shi,
Aisha ke wa ke iya irin hakkurin kine wai nifa da kika gan ni nan cikin nan ne ya tauye ni wallahi in bashi ba da yanzu nabargidan nan,
Nace kije ina Anty ?
Hakuri zakiyi ku zauna lafiya dashi da abokan zaman ki don fa shi zaman gida da kike gani ba dadi gareshi ba,
Wallahi zama dakinki yafiye maki komai dadi da wuya yanzu su wa yan nan yaran yaya kike son yi dasu inkin fita kibar su kamar marayu acikin wanan gidan yawan,
Shiru tayi tana saurare na nace manya kance ayi hakkuri don zuri,a don haka don Allah kiyi hakkuri ki zauna dakin ki,
In ma wani abu kike so kiwa dan uwan ki magana yabaki kudi ki fara sana,a kina dan juyawa kina samun dan kudin kashi sai kiga kin rage wani kunci a ran ki,
Aisha kwanki fa da baki nan naje gidan ban samay kiba naiwa yaya magana ya taimaka min da kudi nasai koda dan fridge ne ina sa,na,a dashi irin yadda kikai tayi a baya amma sai yaya yace min na tafi zan ji shi,
Naiwa Biba magana da zan tafi akan ta taimaka min amma sai ce min tayi wai baida kudi taji yana cewa baida kudi tare dashi,
Nace amma shine ni baki fada min ba Anty da kin fada min ai da ansan yadda za,ayi ko,
Tace sai daga baya nake ganin wanan shegiyar matar tashi ce ma ta,zuga ki aida nake fadaw Asmau ce min tayi may yasa na fadi a gaban Biba don duk yadda zatayi ta hana shi ya baki sai tayi shi,
Yanzu Aiaha in yaya bai taimake mu ba gurin wa zamu je garin nan ya taimake mu
Tunda ana ganin dan uwan mu na,dashi amma baya taimaka muna nace kiyi hakkuri zan mashi magana insha Allahu, zai baki,
Kinga da,har da engine din nika sai ki hada kina nika don naga uguwan nan naku za,a samu nika sosai tace hakane Aisha amma ai samun kudin ne keda wuya nayin haka,
Nace babu wani wuya insha Allahu ke dai ki tayani addu,a kawai Allah yasa mu dace tace Amin Aisha,
Nace idan za, saro min kaya,sai ki bada dan kudi a sayo maki koda takalmomine ki sayar da saukin kudi yadda zasu kare da wuri akara saro maki wasu,
Murmushi kawai tai min nasan zatace ina kudin suke Aisha,
Alhaji Bala ne yashigo sai ko gashi har dakin yana ganina yace a, hajiya Aisha ashe kece a gidan namu nace eh Alhaji nazo ne na gaishe ku kwana biyu ban shigo ba,
Yace Allah sarki aiko mun gode da kika tuna da mu yace ko kinga mutumiyar ki yadda ta tsufa tai nauyi da yawa yana yi yana kallin fuskan ta yadda ta wani daure fuska,
Mundan gaisa dashi yafita yabar mu nan da ita yana fita nace wallahi Antu kiji tsoron Allah kada ya kamaki da,alhakin wanan mutumin dubi fa yana shigowa dakin ki ya nufo direct, kuma kin bi kin daure fuskan ki,
In baiji dadi agurinki ba ina kike son yashiga yaji tai dan murmushi tace baki ganewa ne Aisha iyakan shi fa ke nan dadin bakin nayarda dashi ya,samu biyan bukatan shi, ba komai,da zai iya kara mutum dashi yanzu sai wanan,
Nace LOKACI NE,,,, sunan novel dina dake tafe nan da, wasu kwanaki insha Allahu,
Da zan tafi dubu goma na bata tai ta mamaki tana godiya suma kishiyoyin ta na basu dubu biyar biyar naba yaran su dubu biyu nace su raba ban rage ko kwandala ba daga cikin abinda yabani da zan zo saima karin danayi don matan suyi matukar bani tausayi duk sun jemay gaba dayan su dagani suna cikin lokaci,
Nasha godiya don sun kasa boye farin cikin da,sukayi kan kyautan da nai masu,
Nabar gida cikin dadin rai da yarda da shawaran da naiwa zarah din,
Daga can na biya gurin Anty hindatu na,samu mijin ta a gida suka kama yi min ba,a wai na koma wata yar birni kamar matan Abuja,
Bayan fitar mansur take tambayana inda nafito da rana haka na fada mata halin da zarah take ciki da mijin ta,
Tace aidama dole haka ya kasance, ita Umma tana nufin sherin da takewa diyan wasu ba zai tambaye ta bane,
Har gobe fa ita gurinta taga kinbar gidan dan ta Allah daine yafita da yanzu taga bayan ki ko,
Amma ai kadan tagani don wanan banzan matar da tasa hamza ya aura tana nan tana fadi a gari sai ta rabashi da kow nashi ta mallake shi,
Nai murmushi nace ai gata ga gidan muna gani ina ga wanan har yanzu bata san kowaye hamza ba tace barta dai nima da ake fada min cewa nayi itawa din wacce ko ranan da ya,shigo sai da yai ma baban daddu korafi a kanta yace bata da mutunci ko kadan shi ta ishe shi wallahi,
Ya barta ne kawai har Umma ta kara koyon darasi a kan ta,
Nace nima nafahinci ba banza ya kyale taba yana da,wani manufa akan ta shiyasa nasa masu ido,
Tace sai cewa take wai ita maza zatai ta haifo maahi in tafara haihuwa fon takifar maki da gwaunatin ki don diyanki son su yake kamar diyan gwal,
Nace tunda itace Allah sai ta zabawa kanta abinda take so mu gani ai nidai nagodewa baiwan da yai min kuma har kullun ina kara gode mai in ma zai kara min mace ne shirye nake dana kara gode mai fiye da kullun,
Tace bar jahila ita batasan diya mata yanzu jari bane ga iyayyen su,
Mun kai wani lokaci da ita nai mata sallama nadawo gida na samu Asmau tai min aikin komai da nadawo da zumar yi hakan ya tabbatar min da ta canza sosai yanzu,,,
****** ********* ******
Bayan kwana biyu yadawo garin sunyi nasara sosai a,wanan tafiyan da yayi don ya samu riba fiye da tsanmanin shi,
Ranan asabar ne don haka yara suna gida muna falo dasu muna hira, sai gashi yafito ciki shigar kananan kaya, yayi matukar kyau da shigan,
Fuskan shi dauke da murmushi ya zauna yana cewa mimi tazo sai taki zuwa yace a,a a mamana ba dai fushi kike da dan naki ba ko,
Nace cikin murmushi kyale ta fitina takeyi wai sai an bata carprison takara sha bayan tasha biyu dazun,
Yace abata mana ba nasu bane zo nan kinji mamana na Madina dauko mata da yawa tasha kinji,
Nace haba yaya in mafa tasha,ba bashi yake bata ba don tafara tsuguni ke nan tana damun mutane da kashi kashi,
Yace iyakan ku kenan wanke mat kashi kawai ko don Allah kubata,tasha mana,
Tana jin haka ta nufi gurin shi ta rugumay shi mu dai kallon su mukeyi madina takawo mashi yafara budewa yana bata a baki,
Biba tana jin muryan shi tafito daga dakin ta tana kallon su ba wanda ya damu da fitowan ta don mun san haka takeyi,
Shima bai daga kai ya kalle ta ba,sai hira yake da,yar shi sai Asmau ce mai cewa dama ina son tambayan ka ina son zuwa gurin su Umma yau,
Batare da ya,dago kaiba yace idan kin shirya sai na tafi dake don dama can zan tafi ko kina zuwa mama muje gaida takwaran ki,
Sai yarinyar ta kada kai alaman tana zuwa din yace madina idan ta kare ki shiryata sai mutafi,
Muryan Biba ne take fadi ka sauke ni gida ina son zuwa na gaishe su yau,
In na yarda ko kuwa ra,ayinki ban san abinda yasa kike min abu haka ba gaba gadi kamar ke kika aje kanki Biba,
Gida fa nace zan tafi kaima ba gashi jiya kadawo ba amma kace zaka je gaida uwarka,
Yadago kai daga ba mimi lemon da yakeyi yace uwatafa kikace Biba ke ba uwarki bane ke nan ko ?
Tace ni bance ba gida kawai na ce ma zan tafi kakawo min wani sabon zance inda watace tace zata wani gurin baka cewa komai sai ni,
Amma nan naga an tafi uguwa baka nan kuma bakace komai ba da kadawo ,
Yace wai fitan da Aisha tayi kikewa wanan magana tau nina aike ta dasani na tafita,
Sai lokacin na fahinci zuwa gidan su Zarah danayi take magana kenan wanan matar kishin ta harda na hauka ke nan,
Nan take na tuna da,zancen da mu kayi da Zarah nace mai aiko ina da magana dakai ko sai kadawo ne,
Yace ko yanzu ma ashirye nake da na,saurare ki nace to muje daki kaji ko may nene zai fi don komai yana son siri ai,
Nan muka tafi muka barta tana kunkuni wai ita za,aiwa raini wayyo don an rainata,
Muna shiga dakin ya dan matsoni a jikin shi na zille ina cewa bafa nice da hakkin kaba kasani yace and so what sai akace kada na taba kayana don banda hakki a kan shi, ko may,
Nace nidai zancen Zarah ne dama yace aikuwa Alhaji bala yafada min kin mashi yaki yace nai mashi godiya kwari da gaske kin zama mai gyaran aure ke nan,
Nace ai dole na kada don bazan bari yar uwana tashiga wani hali ba sai yadan murmusa yace da zata biyo halinki ai da ba hakaba Zarah,
Nace yanzun dai ba,wanan ba taimako nake son kai muna yace akan may Aisha nace akan Anty Zarah don Allah ka taimaka ka bata jari wanda zai ishe ta ta,tallafawa rayuwan ta dana diyan ta
Yai murmushi yace wace bata saba sana,a ba,za,ace ba jari ta kashe su dai a banza ke nan,
Nace sai ka kara mata,wani tundaAllah ya hore maka balle ma ba,a banza zata kashe su ba insha Allahu zata fara juyasu ne sanni a hankali,
Shine fa samun dan uwa yan uwa,su wadatu da mutum a san nasu ya na dashi ba aga yan uwan mutum cikin matsi ba shikuma yana cikin wadata sai duniya su zagi mutum,
Kafara gwada ta ka gani in son samune ma kabasu su duka ita da,Asmau su fara juyawa a hankali,
Zaiyi magana nace don Allah ba don halin mu ba don in tana da abinyi ina ganin za,a rage yawan samun matsala tsakanin ta da mijin nata
Yace min yaji kawai zai duba yasan abinda za,a ayi amma na sa i idan takashe su ga banza sai sun hadu,,,,,
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABUIDAN BAKI BIYABA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE HAKAN CIN AMANA NE,,,,
Alhamdullahi don munyi nasaran samun dubu dari biyu wa kowar su yace su fara sana,a don su tallafawa rayuwan su,
Kamar yadda muka tsara nida Zarah hakan mu kayyi, mun sai fridge da injimin nika sauran kudi aka saro mata takalma patis din yara da underwear mata, dasu sarka da dan kunne tai matukar jin dadin sosai,
Suka zo gida gurin Umma don su gaid ita sai suka kawo zancen hiran yadda akayi yayan su ya basu kudi kowa tana fadin albarkaci bakin ta,
Umma tace ban taba sanin cewa mu wawaye bane sai yau din nan ana,dafa kifi da ruwan shi kuna cewa romo,
Tana amfani daku tana karban kudi a furin dan uwan ku tana kara kan ta da yan uwan ta,
Da sauri Zarah tace haba Umma wai sai zuwa yaushe zaki jaye akidarki akan wanan yarinyar,
Aisha fa bata cancanci wanan irin sakaiyan ba a,gurinki irin yadda ta dauke mu kamar yan uwan ta, na jiki,
Baki Umma ta tabe tace kai yaro man kaza ku may kuka sani sai hargowa kawai,
Asamu ta tare da fadin nikan wallahi koma yadda Umma ta fadine wallahi ban taba gani bakin Aisha a zuciya ma don ni na zauna dasu nasan halinta,
Kina ganin in badon tai muna wanan kokarin ba yaya zai iya bamu kudi haka bayan kullun mutum yai magana ko a kan dubu goma ne fita yazo ke nan,
Yanzu gashi da fa kokarinta,da sa hannun ta har muka,samu zaman lafiya,a tare da mu,
Dubi yadda taita kori akan taga na koma dakina ke kin san irin yadd sukai ta kwasa da Abdul ne kafin ya amince na koma gidan shi,
Bafa karamin yaki tai yi ba,saida tai mashi nasihohin dako ke da kika haife baki iya yi mai,
Zarah tace Indon ta Umma ne ai bataki duk mu dawo gida mu zauna mata,ba ,
Alhaji kullun zancen shi Allah ya karawa Aisha albarka yace iyayyen ta sun dace da haihuwa ya ta gari mijin ta kuma yai sa a da,samay ta matsayin mata a gare shi,
Ku kan duk ta,saye ku wallahi saye mu da may Umma da,halinta na alheri ba, dashi kan ta saye mu ke ma inkina ba kan ki hakkuri ki kama,sarakuwar ki ta kwarai kibar yayamay yayamay wallahi Umma ki bari,
Ganin yaranta sunyi nisa basu jin kwabo yasa taja bakin ta tai shiru ranta a bace, dasu,
Mama hafsi dai tana jin su kyalesu tayi don tasan gaskiyace a makwafin ta tafara baiyyana,
****** ********* *****
Dagani har Biba muna da shigar ciki a lokaci daya kowan mu sai faman lolayi yake, hakan yasa shi fahintar duk mun halbu,
Sai dai cikin yasha banban do ita biba nata yazo da,wahala ga amai ga miyau da,sauran kasala,
Niko kamar yadda na,saba cikina haka na yazo min sai dai yawan barci da kasala da ya,sakar min,,
Dole duk da ina fama da nawa haka nake mikewa nafito nai muna abinda zamuci a gidan shi dai maigidan ba mazauni gari bane don haka yana gurin harkokin shi wimurin ne man kudi,
Wata rana tun safe banga tafito koda neman abinda zataci bane, haka yasa na shiga don na duba ta saboda hakkin makwabtaka kawai,
Na samayta a kwance duk ta galabaice tanajin motsi shigowa na dakin ta dago kanta da kyat tana fadin,
Maman Jidda wallahi banda lafiya tun dare nake fama da zazzabi ajikina ga amai har yanzu yaki ya tsaya min,
Nace subbahanallahi sannu amarya, bari na taimaka maki ki shiga k8 dan watsa ruwa sai ki dan ci wani abu tace wallahi bazan iya cin komai ba amai zanyi nace ki dai daure ki dan sha koda tea ne tace bazan iyaba sai ga hawaye shar a idanuwan ta Madina nakira nace ta dora ruwan zafi takawo min da kayan tea,
Da taimakona ta shiga taiwanka nasa Madina ta dan gyara mata dakin ,
Bayin ta,dana shiga saida tsikan jikina ya tashi don kazanta saboda ina ganin an dade ba,a gyara shi ba, shima dakin ko ina kayane ba kyaun gani,
Tafito na hada mata tea amma tace kada na sa madara ruwan liptop kawai zata sha,
Tana sha sai zufa ya karyo mata cikin muryan tausayi tace nagode maman Jidda nace haba ba komai ai zama tare ne,
Tace min har ta danji karfin jikin ta da tasha tea din nace yanzun dai ina wayan ki bari na kira mummy cewa mahaifiyan ta yadda naji tana kiranta dashi,
Bugu daya a nabiyu uwar ta dauka tana fadin mama yanzun nake batun kiranki naji yaya jikin naki nace Mummy ba Biba bace nice Aisha don Allah ko za,a samu wanda zaizo daga gida sai mu kaita asibiti a dubata don amman yai mata yawa,
Uwar tace ai maman Jidda ce yaya kuke yaya yaran nace duk muna lafiya tace jikin nata ya matsa ke nan nace eh wallahi mummy gara aje asibiti a,dubata kada karfin ta ya kare take ce min gata nan zuwa yanzu insha Allahu,
Da mahaifiyar nata zata zo tare da,gwagon Biba din suka zo gidan ganin yadda ta koma hankalin su ya tashi sai faman godiya sukeyi,
Nakira yaya ina fada mashi halin da ake ciki da ita yace muje asibiti din aji ko maynene matsalar ta,
Ibrahim nakira na fada mashi yake ce min shifa aiki yake a shago kada,na matsa mashi nace yaya Ibrahim kayi hakkuri kazo don Allah,
Da zasu tafi ban bi su ba tunda ga yan uwan ta harda mahaifiyan ta nice naba kudi don suje suga likitan,
Gado akabata za,a kara mata ruwa, hankalin yan gidan su yai matukar tashi sosai, duk abinda za,a bukata saida na tura Madina takai masu