Sarautar Mata

Chapter 89 of 94

dan neman yaro mara hankali kawai,
Hamza yana gamawa ya mike yana cewa Ibrahim su tafi, din gidan Baba mudi su gan shi,
Sun yi sa a sin samay shi a kofan gidan shi zaifita sai dai ganin su ya sa shi tsayawa suka gaisa yace su shigo daga cikin zauren shi,
A saman tabarma suka zauna gaba dayan su inda suka kara gaishe shi a cikin ladabi,
Sai dan shiru ne ya biyo baya kadan shi Hamza din ne ya kawar da shirun yana cewa Baba dama mun zo ne akan zancen Aisha ayi hakkuri ta koma dakin ta tunda ba fada mu kayi da ita ba,
Baba yai dan murmushi yake yace ni Hamza a rayuwana ba kai min komai ba wallahi sai ma ince nagode kwarai da rikon da kaiwa Aisha,
Amma matsalar tana ga mahaifiyar ka don bazan yarda ya ta takoma gidan ka ba mahaifiyarta tana gwada mata sanan bakar tsana haka,
Yau har abin ya tashi a kan ta ita kadai ya koma ga zurian ta da kai,
Don haka don Allah ka koma kaje kayi hakkuri kayi biyayya ga mahaifiyar ka ka zauna da wace uwarka ke son gani a gidan ka,
Saboda haka kuyi hakkuri ku koma don yanzun ba abinda zan iyayi don ko uwar yarinyar naga ya hau sosai itma wanan karon don haka ayi hakkuri kawai da wanan zancen in Allah yaraya yaran sun isa yayye sai acire su a nono adawo maka dasu duk ku rike tunda badasu nabaka ita ba,
Baba don Allah ayi hakuri hakan ba zai kara faruwa ba insha Allahu inji Hamza wanda ke ji kamar ya fada a wuta don bakin ciki da tashin hankali,
Baba yace hamza na fada maka,wallahi kai bakai muna komai ba halin mahaifiyar kane dai bai muna ba gaskiya ayi hakkuri,
Shiru zauren yayi kaman babu kowa a cikin zauren saboda kowa da abinda zuciyar shi ke saka mai,
Babane ya kawar da shirun da cewa aiko mahaufita yazo ya samay ta a cikin wanan hakin zai ga ban wa yar shi adalci ba na bayar da ita inda ake gallaza mashi ya ne kawai,
Nan dai yabasu hakkuri tare da basu magana suka tafi gwiwa ba karci rai a bace,
Bai koma gida ba yace Ibrahim ya wuce dashi wani guri don yaga wani abokin shi,
Nan yabar shi yadawo gurin su Umma ya fada masu duk yadda sukayi da Baba Mudi din,
Wasa wasa karamar magana ta zama babba don Ummi ta kekashe kasa tace bani komawa gidan hamza,
Hankalin shi yai matukar tashi sosai don bai zaci abin zai kai haka ba sai ga wankin hula na son kaishi dare,
Ana wanan rikici shi kuma yana kokarin samun gida a Kaduna don yace can zai mayar da iyalin shi gaba daya, yafi mai hankali kwance,
Ga matsin da yake samu daga gurin iyayyen biba sun sashi gaba da bada hakkuri,
Shi kuma ya tsaya a bakan ba zai mayar da ita gidan shi ba yagaji tafita daga ran shi yace masu,
Nikan tun zancen yarana yana damuna arai har Ummi tagane wani dare tai min tas don haka na fitar da zancen su a raina na sake jikina,
Dafarko sai suka tsiri kawo su wai sunzo ganina amma sai Ummi tai masu kashedin kada,akara kawo su abarsu su saba da Umma,
Wanan abin ya taba ran hamza sosai don ranan da yaji har da kuka saida yayi da hawayen shi yabar gidan Umma,

****** ********* ******
Tunda Hamza yai tafiya bai dawo ba yau kusan sati uku baya garin ina gidan mu abina na kwantar da hankalina na fitar da komai a raina,
Ranan wata laraba mukaji ance wai ana wa baba sallama Atika tace baba bai nan sai ga yaron yadawo yace wai ance Fatima tana nan,
Aka ce yaron yaje yace waye ina jin haka kwance nake ina ba hassan nono, na mike zaune ina mamakin wanda zai ce a sallamo mashi Ummi,
Sai muryan yaron naji yana cewa wai ance Bello ne daga Burkusu ma,
Zubur na mike, tsaye na zari hijjab dina na zuwa waje da sauri na, wani High lender nagani bak wul a waje gidan mu sai dai ba,a ganin wanda ke cikin motar sai dai na ciki ya gan ka,
A hankali akafara bude kofar motar nacikin motar ya sako kafan shi takalman shi kawai mutum zai gani ya fahinci wanda ke cikin motan ba karamin mutum bane,
Ina tsaye na zurawa motar ido na kagara na ga ko waye a cikin motar,,,,, ,,,,,


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABUIDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON HAKA CIN AMANA NE,,,,,


Fari ne sol ya bude motar a hankali yafito ga ba daya mutanen dake uguwar hankalin su, ya dawo ga motar da mutanen cikin motan,
Ina tsaye, kinkyam.na zurawa mai fitowa daga motar ido ina mashi kallon kurullah,
Kallo daya zakai mai shi kasan cewa naira ta zaunu daram a gurin daga motar har shi kan shi zuwa suturorin shi baki daya,
Daga inda nake a tsaye mutanen shiya sun tsuro min idanuwan su, suna muna kallon mamaki da kyat na iya bude bakina nace Abbana,
Cikin murmushi ya ware hannayen shi tare da nuna ni ya cewa Aisha ko ?
Haba da sauri na nufe shi cikin wani murya nace Abbana Innalillahi wa,inna alaihim rajjiun wallahi kamar mu daya da Abbana don fari ne sol ga bakin suma a kan shi wululk, kamar bunzun kasar Niger,
Kamshin turaren shi duk ya kamsashe uguwa a lokaci guda wata irin shadda ce milk a jikin sai maiko takeyi don buguwa,
Rugumay ni Abba yayi tsab a jikin shi yana sauke numfashi a hankali cikin nuna jin dasin shi,
Yadan dago ni ya kalle sai kuma ya kara rikeni tsam a jikin shi na dan wani lokaci,
Jama,a dake gurin a lokacin sukayo kanmu suna min kallon mamaki don wasun su da yawa basu ma san ina uguwar ba a lokacin,
Nan suka fara dan rade radi kodai mahaifinta ne don kaman yai yawa sosai da mahaifina,
Kuka nake sosai don na rasa irin farin cikin da zan gwada ina ji a lokacin,
Shimmer Abbba kuka yakeyi yadan cire farin madubin idon dake makale a fuskan shi a hankali, ya dan share hawayen shi
Jaye jikina nayi daga jijin shi na juya zuwa cikin gida inda na,fito masu, da tabarma,
Nai masu iso da su shigo daga cikin zauren Baba Mudi nakawo masu ruwan leda sai bin gidan da kallo yake a tsanake,
Waya aka bugawa Baba dake kasuwa sai gashi gida ba bata lokaci,
Sun gaisa yake masu sannu da zuwa nan suka shiga hiran rayuwa da shi cikin mutinci ba nuna komai a tsakanin su,
Baba ya shiga gida yaiwa Ummi izzini da tafito su gaisa, yaba da kudi a sayo abinda za,a masu girki dashi da abokin tafiyan shi wanda ban tsanmani ya iya hausa ba,
Wani yare naji sunayi da French a bakin su hidima sosai aka shiga yi da su bayan sun gaisa da Ummi yake cewa sunyi waya da Hamza yace yana hanyan dawowa ranan,
Abbana yake tambayan ina yaran nawa suke akace mai suna gidan su gurin kakan nin su,
Duk inda nabi sai ido yake bina dashi yana kallo na don ban kara bi takan shi ba,
Sai da su kaci abinci sosai sai Baba yakawo wa Abbana zancen matsalan da nake ciki a gidan mijina,
Murmushi Abba din yayi yace hukunci yana a hannun Baba don shi ba zai sa bakin shi ba,,
Godiya sosai yaiwa Baba da ya rike mashi ni amana batare da wani matsala ba,
Yake cewa Baba ya tayashi rokona nayi hakkuri don yaga kamar ina fushi dashi saboda naki dawowa gurin shi tun dazun,
Baba yace ai ko ba halin Aisha bane fushi amma bari na kira maka ita ,
Nashigo zauren cikin hijjab dina sky color nasamu guri na tsugun nan daga gefen su sai Baba yake cewa, Aisha yau ga mahaifinki Allah ya dawo muna dashi gare mu ,
Amma kuma sai naga kamar baki wa Allah godiya ba da hakan don naga kamar kina nisanta kanki dashi kuma,
Maimakon nai magana sai wasu hawaye na sake masu zafi suka dinga silalin min nan nafara kuka mai tsuma zuciya,
Dakyat na bude bakina nace mashi, Baba may zancewa mutumin da yai watsi dani a cikin duniya tun ina yar karama na bai san cina ba bai san shana ba,
Baidamu da yana da wata ya a rayuwan shi ba ya watsar dani da dan yan shi, ya manta da kowa nashi sai sabbin abokan rayuwan da ya samu,
Haba Aisha inji Baba kowani dan adam da kika gani fa ajizi ne ga Allah don duk kaddaran da zai samu bawa a rubuce yake mai a rayuwan shi,
Wanan tafiyan da yayi kaddararen al,amari gare shi ba makawa sai yayi shi don a rubuce yake mai shi cikin littafin shi,
Ashe ba godiya ya kamata yau kiwa Allah ba da ya kadara akwai robon kara saduwa a tsakanin ku,
Don haka maza ki tarbi mahaifinki kada ki sakawa kanki tsanar shi har ki dawo kina da kin sani daga baya don haka ba halin mumuminai bane,
Bai tafi ya barki don bai kaunarki ba Aisha yatafi ne akan kaddaran Ubangijin shi,
Kukan da nakeyi harda dayan mutumin yana bani hakkuri cikin harshe da nuna hannun shi,
Fita daga zauren baba yayi ya barni zaune da mahaifina shima mutumin sai ya mike yafita zuwa gurin driver su,
Inda nake zaune Abba ya taso yazo ya zauna ya dan dafani yana cewa haba Aisha nasan cewa ban kyauta maki ba na tafi na barki a cikin wahalan rayuwa ke da mahaifiyar ki,
Sai dai ki sani hakan ba,wai yana nuna na manta da ke bane a,rayuwana ko abinci zanci sai kun fado min arai ina tunanen ko yanzu a wani irin hali kuke ciki a inda kuke ko kuma kina inane yanzu,
Sai yai shiru jin da nayi baiyi magana,ba yasani dago kaina hawayene naga suna zubo mashi daga idanuwan shi,
Hada ido mukayi yace cikin kuka Aisha ki yafe min don Allah don nasan ban kyauta,wa rayuwan ki ba don nasan kin fuskanci kalubalun rayuwa iri iri a tare dake,
Tausayi yabani nace Abba na yafe maka don nice yakamata na,roke ka don sai nake ganin laifin Ummina ne yashafeni a gareka,
Yace cikin girgiza kai ko daya ni Uwarki batai min komai ba don yar uwatace halal malal, don may zan kufule ta a raina,. Haka dai Allah ya tsaro muna rayuwan mu,
A hankali nafara fada mashi irin abubuwan da na fuskanta da bai nan da kudaden dasu Baba na yan uwan shi suka bani a bayan shi da kuma taimakon da kulawan da nasamu a gurin shi,
Yace to Alhamdullahi dama abinda na matsu naji kenan kafin na isa gare su naji wani irin kulawa kika,samu a gudin su,
Don nasan yadda zan isa gare su dalilin da yasa banje gurin su ba sai na iso inda kike naji komai daga bakin ki,
Yace Aisha na dago kai yanzu mijinki nake son gani amma kafin ya iso ina so ki fada min duk matsalokin sai na san irin taimakon da zan maki ke kuma,
Nace Abba ni banda matsalar komai don Hamza yana kokarin shi dani yace nagani kuma nasani don gashi har yakai mahaifiyarki da mijin ta saudiya sun sauke farali hakan ma kawai ya isar min da nasan yana kokari a kanki,
To amma yanzu da kika bar gidan ki ka dawo nan kina ganin hakan shine alheri a gareki don ni ban son na saka bakina a wanan zancen don malam Mudi yai min duk yadda akeyi kinga idan nazo nasa baki a matsalarki nai mashi butulci sosai,
Ban yi magana ba sai gasu Jidd mama ta kawo su don suka mahaifina suna shigowa sukayo kaina da murnan su suka fada a jikina suna cewa mama, mama mu ba zamu koma gidan batare da ke ba,
Ban yi magana ba sai nuna masu Abba da nayi inacewa a gaida babana nima, gashi,
Juyawa sukayi sina kallon shi sai Jidda ce tace wanan ai ba babanki bane Baban gona,
Yai murmushi yace masu ni ba Baban gona bane baban mama ne ni Jidda tace ba kai bane baban mama ba fa ban gona ne Baban ta,
Nan ya dan fara jan ta da dan hira a hankali har suka dan fara sake jiki dashi suna bashi amsa cikin nuna jin dadi
Sun gaisa da mama nake fada mashi yadda suke da Hamza ya kaea gaishe ta a cikin mutunci ,
Sun dan yi hira tana tambayan shi iyalinshi yake fada mata duk suna lafiya suna gaisu ma,
Sai an kwana biyune zai zo da su suga gid shi ya fara zuwa ya nemi yafiyan yan uwa tukun,.
Mutane sai zuwa suke suna gaida shi yana kuma masu abin arzki take labari ya yadu a uguwa, lokaci guda,
Mama Rahana tazo sun dauki lokaci suna hira yaushe rabo a tsakanin su,
Sai yamma kis suka bar mu yace a sokoto yake son su kwana da safe zai karasa gida gurin yan uwan shi,
Kudi masu yawa ya barmin yana cewa sai ya dawo zai ganni mu karasa maganan mu dashi,
Ya tafi cikin farin ciki a ranshi inda suka,gama ganawa da hamza ya kama hanya sai Burkusuma,

****** ********* ******
Da dare ya isa garin don haka ba kowane yasan da shigowan shi garin ba,
K9fan gidan su ya tsaya da motan shi inda yafito lokacin Baba Liman yana zaune yana karatu a zauren shi kamar kullun,
Sallaman da yaji yasa shi dago kan shi sai ido biyu yayi da dan uwan shi duk da dare ne bai hana shi gane Abban ba a lokacin, yace, BELLO kaine ko mafarki nakeyi haka ne wai,
Murmushi Abba yayi yace nine yaya ba mafarki kakeyi ba nine a gaban ka,
Rugumay Abba yayi a jikin shi yake cewa Allah na gode maka da ka nuna min wanan ranan dana dade ina jira a rayuwa na,
Jan shi yayi zuwa cikin gida yana fadin ina mutanen gidan nan ku fito yau ga BELLO ALLAH ya dawo muna dashi lafiya cikin mu,
Babba da yaro na gidan sai faman tururuwan fitowa sukeyi don ganin abinda baba Liman ke fadi in gaskiya ne,
Kuka murna da shewa shi kawai ke tashi a gidan don murna da farin ciki a zuka tan su,
Duk da dare bai hana mutane na kusa da nisa fitowa daga gida jen su ba don ganin shi duk wanda yazo tun awaje da sunga motocin Abba da security din da yazo dasu sai mamaki ya kama su, su shiga cikin gida don ganin shi ranan zakace ba dare ba ne a lokacin,
Sai da mutane suka dan tsagaita shigowa don Baba Liman yace a bari har da,safe kowa ya tafi gidan shi, don dare yayi sosai a lokacin,
Kwana raye sukayi da yan uwa yana basu labarin bayan rabuwan su inda yace, lokacin da nabar gida da farko kasar Niger na shiga na kai wata uku a damagaran sai na hadu da wasu turawan faransa da nake wa aikin kula da dawakai da rakuma,
Da zasu tafine suka taya min idan zan bisu zusa kasan su banki ba sai nai kasadan bin su can din,
Shekara na Ukku a tare dasu sai maigidan nawa ya yarda da zamana dashi,
Shike turani fatauci a nan kasa shen Afrika ina mashi business din motoci da sauran abubuwa bayan karatun da yasani na ci gaba na zamani,
Sannu Sannu har aka sanni a kasashen da nake zuwa nima idan zamu shigo sai na fara nawa san,an shigo da wayoyi da computers, da sauran kayan naororin wuta,
Ganin nawa business din yafara karbuwa sosai yasa shi bani kudi masu yawa wanda ban taba zaton zan taba samun irin su ba a duniya,
Ba adade ba Allah yai mai rasuwa shine na kwaso nadawo kasan Ivory cost da zama inda nan ne ake shigo muna da kayan mu daga waje,
Sai Allah yasa min albarka shine har ya kaini ga haka na samu nawa nakai wanan matsayin,
Nayi aure a can na auri wata yarinya da,namu yazo daya yanzun haka muna da yara biyu da ita matar tawa ,
Zan kawo su suga gida idan hankali ya kwanta dama nazo ne nafara ganin gida don Fatima da muka hadu a,saudiya ta fada min nabarku har yanzu a cikin damuwan rashin ganina da bakuyi ba,
Ina fatan zaku yafe min akan irin halun tashin hankali da damuwar da na barku a cikin shi,
Sai da,na,fara zuwa gurin su Fatima din don mijin Aisha cikin rashin sani abokin kasuwanci nane a can,
Aishan tafada min irin alherin da kulawan da kuke mata a bayana banda abinda zance sai dai na gode maku da irin wanan kokarin da kukai min a bayana don nasan koda mutuwa nayi ina da yan uwan da nabari masu halarci da alheri a rayuwan su,
Sai washe gari kofan gidan ya kara cika da jama,a yan uwa da abokan arziki sai zuwa suke suna taya shi murna,
Sai yamma lis ya koma garin sokoto don ya samu masauki da mutanen shi,

Hamza yana zuwa gidan shi yaga duk gidan ya koma mashi bakikirin bai ko jin dadin gidan gabs daya a ranshi,
Kofan dakina ya dan tsurawa idanu zuwa wani dan lokaci sai ya nisa da kyat yaja kafan shi zuwa dakin shi,
Gado ya fada ko takalman kafan shi bai cire ba sai tunane yake barkatai,
Yasan da ina gidan yadawo haka da gajiya da yanzu dani da yara muna nan muna mashi oyoyo da taro mai daraja,
Amma yau gashi shi kadai a cikin gidan ba motsin kowa a gidan sai yaji gidan ya koma mai kaman makabarta,
A hankali ya bude idanuwan shi da suke a rufe ya furzo iska mai zafi yana fadin haba Umma may nai maki haka kika yanke min farin ciki a rayuwana,
Rayuwan mu ya tuna

Download complete TXT · Novel page