Sarautar Mata

Chapter 90 of 94

da irin gwagwalmayan da akasha a lokacin da Lima ta daure shi da asirin ta,
Duk irin kokari da halarcin da Aisha tayi bata guje mashi ba amma Umma bata gani,
Yasan da itace akai wa yar ta haka da tuni ta raba wanan auren ko tuntuni,
Sadiya kuma da ta tilasta mashi ya aure ta itama tazo da nata kalan iskancin har tayi tagama ba,a ji shi da Aisha ba sai,
Zuwan Biba duk Umma batai saduda ba takara kawo mai wani sabon rikici mai muni,
Abin kunya wai ace uwar shi ce tai wanan kalaman haka akan zurian shi shi ko kadan baiga laifin iyayyen Aisha da ita ba gurin dauka mataki haka,
Amna gaskiya indai shine zaice ya saki Aisha gaskiya ba,a bakin shi ba kan sai dai in duniya zata hade ne amma bai sakin Aisha gaskiya,
Saki saki fa yace ina ai gara na mutu da ace na saki Aisha a rayuwana in na saketa na zauna dawa a gidana,
Dunkulewa yayi guri guda kaman mai jin sanyi yana tausayin kan shi da iyalin shi da Umma ta jefa a wani hali,
Yasan duk inda Aisha take itama tana can tana zaman hakkuri ne saboda yasan tana son shi da zuciya daya har cikin ran ta,,
Amma ga Umma nason ta kawo masu shamaki a tsakanin su ta raba abinda Allah ya hada a halarci,
Ya kai wani lokaci a haka kwance cijin matsanacin tunane sai dai ya kasa kai ga mafita har lokacin,
Da kyat ya tashi yai sallah shafai da wuturi yana kokarin komawa barci bayan ya dauki lokaci yana addu,a sai kuma yaji cikin shi na son cin dan wani abu,
Kitchen din gidan ya shiga komai tsab a kitchen din nawa sai dai yarasa mai zai dafa yaci komawa yayi falo ya dauki wayan shi ya kira Ibrahim din shi ,
Kira daya gana biyu ya dauki wayan yana cewa ko ka dawo ne yaya ?
Murya a kasalance ya amsa mashi da,eh don Allah ka sayo min kaza abincin kowa mai zafi sosai da drinks na kwali mai sanyi,
Ba a dauki lokaci ba Ibrahim ya shigo gidan ya samay shi zaune saman kujera yana saye da wani riga mai hannu guntu da wandon rigar tree quarter,
Kallo daya yai mashi ya gane cewa yana cikin damuwa tausayin dan uwan shi ne ya kamashi lokaci guda,
Gaisawa sukayi ya aje mashi abincin daya kawo mashi yake cewa ashe ka iso ko,
Yace eh tun kafin magariba ai ina garin nadan tsaya ne yin wani abu,
Ibrahim yace gashi kuma kun sha banban da mahaifin Aisha don yazo yau amma yatafi garin su akace,
Yai dan guntun murmushi yace ai muna tare dashi dama na tafi shigo da wasu motocine da ya turo har da na ita Aisha cikin motocin,
Ikon Allah Aisha ya sayawa mota ya tambaya cikin fara,ar shi yace don yasai mata mota may akayi bafa karamin mutum bane yadda kake tsanmani ba ita kadai ba inajin harda wasu yan uwan shi don mota biyar ya turo ashigo mai dasu sune costume suka kama su,
Sun dauki lokaci suna hira duk Ibrahim yanayi ne don ya kawar mai da damuwan shi,
Ibrahim yace amma dai kunyi magana akan zancen Aishan da shi kuwa,
Dan tsuki Hanza yaja yace ba abinda zai iya don ba a wurin shi take ba don haka bai sa kan shi a zancen ba,
Yaya zancen naka auren Hamza ya tambaye shi sai Ibrahim yace ku ake jira kuje sai a saka rana da lokaci,
Ok zanyi kokarin na shirya zuwan su Baba kafin na koma don yanzu zancen gidan da nake son sama muna a kaduna ne yake gabana,
Hamza yace amma bazaka zauna gida ba a gurin Umma dai ko don ina gudun abinda ya faru da ni yafaru a kan ka don abin na Umma a jinin ta yake,
Don sai nake rasa may Aisha taiwa Umma ne haka a,rayuwa karshe dai ban gano komai ba sai naga kamar bata son taga mace ta rabe ni ne kawai,
Don kaga ba wai da Aisha kawai Umma take adawa ba har Sadiya da Biba da na zauna dasu akwai matsala a tsakani,
Ibrahim yace ni na dade da sanin haka,wallahi yaya ina dai tsoron nai magana ne inja zagi gurin ta,
To mau yakawo wanan hakane wai don gaskiya na rasa may Aisha take mata ta tsaneta haka sai nagane don kawai taki rabuwa dani ne kawai,
To Allah ya kyauta don shine matsalar kawai, in bashi ba ni dai banga wani matsala daga gurin Aisha ba wallahi,
Sun dauki lokaci suna tataunawa har sai da dare yayi yai mashi sallama yatafi cikin tausaya mashi,,

Da labarin zuwan mahaifina ya riski Umma da farko tace karyane sai da su Sa,a suke ce mata kamana da mahaifina har kamar ta baci wallahi, don kamar an tsaga kara ne,
Nan suke bata labarin irin shigar sa da kuma motar da yazo da ita,
Bata kara gaskan tawa ba sai da taga kudin da Abbana yaba su Jidda a gurin mama yakai dubu dari sabbi dal dasu,
Ido ga kudi sai ta rude ta na cewa ikon Allah ashe kuwa ba karamin mutum bane dai don wa zai iya ba mutum kudi haka masu yawa,
Nan tafaracyan sake sake a ranta yadda itama zata kwanta a ci arziki da ita batare da wata matsala ba,
Ta so mama ta bata kudin amma sai mama tace sai Hamza yazo an gwada mashi kudin tukun ,
A ran ta tace lalai tayi sakaci sosai don da bata sake ba taja jikokinta a jikin ta da dole kudin nan a hannun ta zasu zo,
Tace na samu kudin nan haka ai sai kawai na sayowa autana kayan dakin da bamu saya ba dasu,
Amma ai sai na samu ko yayane sai kuma tafara jin haushin mama wai itace ma da shegen shishigi tsiya wallahi duk ta shigewa wanan yar Agwi din mai kama da uban ta,
Muna nan da,safe sai ga Sa,a datu wai Umma tace tazo ta dauki tagwaye tana son ganin su,
Ummina da su mama saude sukace ace suna barci baza a samu kawo su ba sai dai ayi hakkuri,
Maimakon ta fita,sai ta dan tsaya taji Atika tana cewa baza a kaisu ba ta shafa masu mugun abu su ga yara sun gi bulbul a lalata masu rayuwan su,
Tana zuwa ta samu Umma da mama sai tace masu Umma sai da nace maki ba zan tafi ba kika matsa min gashi kinji abinda suka ce,
Nan Umma ta hau fada tana cewa ko dai anki ko ansi dole ace jikokina ne su don ba,a taba raba anta da jini,
Yanzu anga ci yazo shine Atika take nuna ita ta kwarai ne ko ina nan take wanko kafan ta ta,shigo gidan nan da gulma akan Fatima da yar ta,
Yanzu tasan tana son su zanje na samay ta a yi tsiyan da take son ayi yau,
Mama tace wallahi yaya na raba ki ana kokarin ganin an shirya a tsakani kina son zuwa tayar da wani balli kuma,
Dama aikowa yasan akanki Aisha tabar gidan mijin ta bawai basu son junan su bane matsalarki ce kawai tafitar da ita daga gidan ga,
Yanzun kuma shine zaki tafi hada wani ki kara lalata zancen gaba daya kowa ya huta ko,
Jikin Umma yai sanyi ran ta yai matukar baci take cewa kai wallahi ni dai na shiga uku wallahi,
Mama tace ba uku ba yaya har tara ma wallahi kin shiga don kin bada waka an amsa maki,
Tun farko sai dana hore ki da hakan don gudu irin haka yanzu gashi an barki a cikin tsaka mai wuya ai don ko gulbi goma kika shiga baki fita sai ace kin yi din ne,
Dole ba don taso ba ta kyale zancen fan ta abace don ko magana ta kasa,
Mama tace irin ku ne iyayyen mazan da yaran zamani basu son shigowa su samu a gida, inda Aisha yar zamani ne wallahi da yanzu kun raba gari da ita ko duniya taji ku,
Ibrahim ya,shigo da murna yana fada masu wai mahaifina ya sayo min motar shiga kawai da mamaki suka ce mota fa yace wallahi har ma motar ta iso ko don jiya yaya yake fada min,
Nan su mama suka shiga murna da nuna farin cikin su Umma ko sai dariyan yake takeyi kawai,
Sun tafi gidan da Ibrahim ke neman mata,amma abinda sukaji ne ya tayar masu da hankali don iyayyen yarinyar sunce sun fasa,
Saboda sunji labarin halin mahaifiyar shi duk macen da dan ta ya,aura sai ta mayar da ita karamar bazawa tafito, don ta,
Saboda haka suje suyi hakkuri abar zancen bazasu ba da yar su ba kwana biyu a sako masu ita,
Sun dawo da wanan mumunan labarin Umma ta shiga dan koke koke wai mutane suna bin ta dasheri don kawai anki jinin ta,
Irahim yana samun labarin haka ya shiga tashin hankali sosai tsaye yai mata ranan yace wallahi shikan bazai yarda ba,
Da ya zauna bakin ciki ya kashe shi garin ma zai bari gaba daya ya shiga yawon duniya,
Tirkashi ranan Umm taga tashin hankali tai nadama sosai don Jibrin ma yace haka baban yarinyarcda yake bida yai mashi kashedi yabar zuwa gurin diyar shi kada uwar shi ta illanta mashi diyan shi,
Lokaci guda ta ramay ta zabge kamar ba ita ba ko abinci bata iyaci sai da ta sha dan hwaro hwaro a cikin ta na kunu,
Su Baba Madu da Liman sun zo gurin Baba Mudi amma yace suyi hakkuri abar zance don Aisha ta gama auren gidan Hamza,
Sunyi mamakin yadda Baba mudi ya cije akan bakarshi na,rashin yarda na koma haka duk da sunzo da kansu bashi hakkuri,
Sun dawo sun fada masu yadda sukayi da Baba mudi da kuma irin cin fuskan da na fuskan ta agidan gurin Umma da yaran ta mata tun shigowa na,
Don haka Baba Madu yace wallahi Rabi kin cuci rayuwan yaran nan yaran ga gaba dayan su basu rage ki da komai ba a duniyan nan amma kika jefa rayuwan su cikin wanan garari haka saboda ke,
Hamza ko saboda bacin rai baiko tsaya angama maganan ba ya mike yabar gidan rai a bace gashi ko wayana baya samu,
Da dare yazo gurin Baba hamza ya kara bashi hakkuri da kan shi sai dai magana guda ne a bakin Baba shine ya kawo min takardana kawai ba zan koma ba,
Dukar da kai yayi yana sauraren zancen baba da yake ji kamar ana zuba mashi garwashin wutane a zuciyar shi,
Hawaye ne masu dumi suka zubo daga fuskan shi ya bude baki da kyat yai magana yace Baba kodai nima Aishan tace nai mata wani abin ne da za,a yanke min wanan hukunci mai tsauri haka Baba,
Baba yace ko daya Hamza in bamu gode maka ba baza mu zage kaba kuma laifin uwar ka dai ne ya,shafe ka don haka aje ayi hakkuri Aisha amana take a gurina idan na yarda ta koma Rabi ba fasa halinta zatayi ba don haka duk abinda ya samu Aisha ni na ja mata shi,
Don sabodani ta aure ka don haka yanzu kuma nine zan raba,wanan auren wahala da bautar da yarinyar nan keyi ba a gani ya isa haka a hakkura kawai kowa ua samu nashi rabon,
Kuka sosai Hamza yake a gaban Baba yana rokon shi don Allah yayi hakkuri kada ya rabashi da Aisha don itace farin cikin shi baba yace na,sani hamza duk nasan da haka amma ayi hakkuri kawai shi yafi,
Yai mashi sallama yace shi zai shiga gida ya tashi ya koma kada dare yai mashi shi yagama yanke hukunci,
Har baba ya mike sai ya dan tsaya yana cewa, kayi kokari ka mayar da dayan matar ka,a dakin ta don zaman ka haka ba,alheri bane
Mutane kuma zasu iya cewa saboda Ausha ne yasa itama ka sallamay ta kaga zaka,shafa mata bakin jini bataci ba bata sha ba,
Nan ya,shige ciki yabar Hamza zaune a guri har tsawon wani lokaci ya tashi,
Yana fita yaji bai iya jan mota Ibrahim yakira ya kaishi gida,.
A hanya sai kuka yake cikin mota Ibrahim din ya kasa bashi hakkuri shima dai ran shi a bace yake daurewa kawai yayi yake jan motan ,
Ranan gidan Ibrahinm ya kwana yana ba Hamza magana da kuma yadda zasu bullowa baba mudi,,,,,



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABUIDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON HAKA CIN AMANA NE,,,


Ya samu gida kamar yadda yake bukatan samu a garin kaduna a wani sabon uguwar da matasa sukafi yawa acikin shi,
Sai dai,matsala daya yanzu shine akan zancen dawowana gidan shi don abin yafara wuce tunanen shi sosai don iyayyena sun kafe akan sai dai ya bani takarda kawai a rabu don Umma Rabi,
Ya,shiga cikin tashin hankali sosai ga mahaifin Biba yana ta faman bin shi akan yayi hakkuri ya mayar da ita dakin ta amma yaki sauraren shi,
Dare daya ya yanke shawara ya tafi can kauye gurin iyayyena na,asali ya fada masu abin da ke wakana a tsakanin mu,
Sunyi tafiyan shi da mansur da wani abokin su tun asuban farko suka bar garin zuwa kauyen mu,
Sun isa garin musalin karfe dayan rana da wani abu don nisa da ke tsakanin mu da garin Jega,
An masu taro yadda ya kamata sosai don yanzu ua zama dan gida sai da aka dama masu fura suka sha,suka koshi ban da hamza da hankalin shi ba a kwance yake ba,
Sai Baba Liman yasa ai masu iso da su shigo daga cikin zauren shi don su gana saboda ya fahinci magana ce ke tafe dasu,
Hamza bai boyewa su Baba na komai duk abinda yafaru sai da ya fada masu kaf,
Baba sahabi dayake shi dan zafin zuciya ne nan take yace shi Mudi ina ruwan shi da,zai kashe wa yarinya aure may nene hujjan shi na yanke wanan hukuncin bada sanin mu ba,
Ganin inda yake shiga ba nan yake fita ba yasa Baba Liman yadakatar da shi da cewa haba Sahabi shi fa Mudi bamu da mairaina akan shi kan zancen Aisha,
Don duk yadda akeyi yai muna saboda haka wanan zancen sai a tsaya ayi bincike akan shi, don idan baida hujja ba zai yanke danyen hukunci haka ba,
Don haka yanzu yadda za,ayi shine kai sahabi da Musa sai ku shirya ku tafi can Jega din ayi ta takare muji maganan dake nan idan kun ga za,a iya sasanta maganan sai ku sasanta ku dawo idan kuma maganan ba mai sasan tuwa bane sai abi shawaran da ya yanke ayi hakkuri,
Hamza baiso haka ba amma duk da haka yaji dadin da akace da Baba Sahabi za ai tafiyan,
Don yasan in ba wani ikon Allah zai iya yin galaba akan Baba Mudi da Ummi na,
Sai cikin dare suka shigo gatin Jega ana sallah magriba, don haka basu tsaya wani magana don gajiyan dake tare da su masaukin BLB guests,in ya sauke su tare da samo masu abinci mai kyau suka ci,
Sai washegari suka samu zuwa gidan Baba Mudi wanda yai matukar mamakin ganin su da,safe haka,
Su gaisa dashi a mutunce ya rasa inda zai sasu sai farin ciki da ganin su yakeyi,
Yace bari ya kawo masu abin karya dakatar dashi sukayi suna cewa a koshe suke sai da suka karya suka fito,
Nan Baba Musa ya isar masu da zancen Baba Liman din murmushi Baba Mudi yayi yace haka nake so dama,
Kamar yadda Hamza ya fada masu shima haka ya,mayar masu harda ma abinda Hamza ya boye a lamarin mahaifiyar shi bai fada masu ba duk Baba Mudi sai da ya fada masu kaf,
Yace bazan taba kashewa Aisha aure da hannuna ba sai dai idan abin yafi karfina to zan iya don ya zama dole amma gaskita shi mijin Aisha sam baida maraina a gare mu,
Don yaron kirkine a,gabana aka haifeshi kuma ya taso agabana nasan halin shi fiye da tsanmanin ku don haka ni banga wani aibi a kan yaron
Matsala dai itace mahaifiyar shi da tasa yar mutane a gaba har da zancen kissa don kissa mana idan ta halaka yaran wa yai hasara ba Aisha,ba don ita mace ce shiko dan ta namijine zai iya auren wasu mata su kara haifa mai wasu,
Ni bukatana da na yanke wanan humuncin mai tsauri haka shine sai sun san daranjan ta da muhin mancin ta a gare su in ba haka,ba da na mayar da ita haka kai tsaye abin ba,za,a samu saukin shi ba,
Su baba sukace wanan gaskiya don tunda ba mutunci ke gareta ba zata kara bullowa ta wani hanya ne kuma,
So nake sai dan sun kai ruwa rana da ita tazo har gidan nan da kafan ta ta roki Aisha gafara kan abubuwan da take mata, shine kawai zai kawo saukin al,amari amma ai har yanzu indai Rabi ce bata saduda ba gaskiya,
Baba Musa yace gaskiya malam Mudi kayi hikima sosai a nan don gaskiya irin wa yan nan Uwayen wuyar sha,ani ne dasu,
Yanzu abinda za,ayi shine zamu kira shi yaron nan mu bashi hakkuri yaje su sasanta da,uwar shi, idan har ta yarda ta bari to tazo nan gidan ka da kan ta,taba da hakkuri kaga haka,zai sa mu fahinci ko tayi taushi ga,al,amarin,
A haka suka tsayar da zancen suka kira shi ta,waya yazo sun mashi bayani akan duk yadda sukayi da shi,
Shiru yayi kan shi a duke can ya dago kan shi da kyat ya iya bude bakin shi yace Baba kuna ganin idan anyi haka ba wani matsala kuma,
Sukace haka din shine daidai don su zauna da Umma a fahinci juna ya sauke ajiyan zuciya yace ba matsala Baba zan je nagan ta,
Yai masu sallama yafita suka bishi da kallon tausayi kawai a ran su suna cewa baida matsala komai uwarshi ce kawai matsala ga al,amarin,

****** ********* ******
Ya shigo gidan

Download complete TXT · Novel page