Showing 267001 words to 270000 words out of 299981 words

Chapter 90 - Sarautar Mata By Makawa

04 Dec 2025

17669

shi,
Sai zuwa dare na shirya da yarana muka tafi gaida Biba a asibitin mun samu jikin nata yai sauki tana zaune tana cin alalain da tace nai mata shi take so,
Gaba daya dakin ya cika da yan gidan su sai hira sukeyi suna dariya ina shigowa suka sako min na mujiya,
Suna kallo na cikin gulma da tsegumi na nagaisa dasu ina masu yaya maijiki wanan gwagon nata ce ta amsa dasauki yaya kokari murmushi kawai nai mata na isa kusa da gadon ina mata sannu yaya jikin ta amsa min da dasauki maman Jidda gashi har ina cin abinci,
Dan jin ina tsaye rike da hannun yarana sai take cewa mimi zo kici alale sai yarinyar ta make don bata saba da ita ba,
Dan lokaci kadan nace mata,zamu koma don dare yayi ba kowa a gida saida safe sukai muna muka tafi take ce min har nafara tafiya don Allah maman Jidda dasafe ma ki kara min wanan alalen naji dadin cin shi nace Allah ya kaimu,
Ina fita daga dakin matar yayan ta tace wanan kan ai ni sai nake gani kamar buzuwa ce ko ?
Wata tace bafa wata babba bace ina ga ai Biba ma zata girmay mata ga shekaru,
Shegiya sai kyaun tsiya wallahi inbadon biba ma yar iskan kanta bace aida bata kai haka a gidan ba,
Gwagon su ce tace haba haba dai ina laifin yarinyar nan itace da takiramu da rana habiba ba lafiya takuma sa akawo ta asibiti aiko kun ga bataci zagi haka ba a gurin ku,
Kai dan Allah gwago wallahi duk makirincin kishiya ce ba don Allah tayi ba kawai don a yabetane,
Gwagon tace koma don may tayi mu dai mun gode mata da bata kula ba aida ba,a,san yadda za,ayi ba, ita kadai a cikin daki,
Biba tace balle wallahi ni yanzu na ma daina damun kaina da al,amarinta don na fahinci haka halinta yake kokai mata abin bacin rai dawuya kaga bacin ranta wallahi ko ,
Irin masu saukin kannnan ne da basarwa al,amari bata daukan abu da zafi ko kadan,
Gwagon yace wallahi in wanan ja,irar ce batai mata ko kwatan kwancin wanan da tai mata, dariya Biba din tayi tace wallahi hakane gwago don balain kishin ta nakeyi don in tana gidan nan ban taba samun kan Hamza a,rayuwana,
Gwagon tace to wallahi ki dai rage shifa zama dakike gani na kishi zaman amana ne ita tana kokarin sauke nauyinta a kanki ke ko shedan yana rudinki,
Baki rasa ciba baki rasa shaba komai a kwaishi kuma mijinku bai rage ki da komai ba na zamantakewa don may zaki dagwarawa kanki wahala ita bata ko san kina yi ba ma,
Biba tace wallahi hakane gwago matsalana yanzu guda ne zuwa biyu uwar shi da yan uwan shi sune matsalata, a gidan,
Kinga inda zaki dosa ba inda bai dace dake ba kin kwaso shegen kishin iyayyen ki kin zo dashi har gidan miji,
Ko su uwafa uwace akanta wallahi inkin matsa sai ya saba maki, tace shima fa,taishe shi don halin fitinan ta yakai mashi ko ina,
Nan dai sukai ta zance akan yadda al,amarin gidanbmu yake dasu, sai da,suka gaji suka tafi don kan su,
Tun bayan dawon ta,gida naga ta rage wasu halayanta na sheri sosai don yanzu takan fito in muna falo a zauna adan yi hira da ita, ban damu da rashin girkin da batayi ba don nasan matsala ne na lalurar ciwo,
Sai dai ranan da Hamza ya dawo sai gata ta mike tana girki da kan ta da tagama kuma ta nade zazzabi ya tashi,
Sai na fahinci bata so idan tana da girki na kama mata don tana zaton zan mata babakere a kan aikin ta, don dan canjin da,ake samu daga gurin maigida,
Har wanan lokacin Biba bata fahinci ina da ciki a jikina ba don ban sake yadda ta sake ba,
Sai faman rawan kai take mutane na zuga ta suna ce mata wai maman yan biyu,
Nan ta dauko sallon da makirici a kan cikin yau tace kaza take so gobe ma tace wancan take so,
Tun yana biye mata ranan har yakai gacewa ke nagaji bake kadai bace nafara ganin ciki a gurin ki ba Allah yaba Aisha hakkuri,
Aisha kace niba Aish bace Biba ce ni yanayin cikin ta daban nawa daban kasani ko tunda ba haka takeyi ba ko ni cikin nawa namijine shiya sa,
Yace look Biba na fada maki ban son wanan rayuwan da kike shirin dauko min a gida ni dana miji da mace duk daya,na,dauke su tace haka dai kace amma ko a gurin Allah ba daya suke ba ai don an fifita su,
Rai a bace yafita yana mamakin irin halin rayuwan Biba bata dai bukatan a zauna lafiya, a gida duk abinda zai fitina a kan shi tasan yadda zatai magana sai anyi,
Nikaina yanzu har mamakin ir8n saukin kan da Allah yabani nakeyi dafarko na kance kodai nasihan Ummina ne dana hau yai min aiki haka,
Sai kuma daga baya nakan yi tuna ne koda sauki na,sama daga gurin Allah don nayi roko sosai dana je makka akan Allah ya yaye min kishi,
Allah kuma ya dorani akan duk wata mace da Hamza zai auro yakawo gidan shi daamsunan kishiya ina,rikon Allah ya fifita ta hal8n alheri a kan su,
Kan Umma mai nakan tsaya naita add,dua kan Allah ya dorani daga duk wani mugun nufi nata ina mai neman tsari dani da zuri,a na akan ta,
Saba,an da zan fara shima saida nai dawafi akan shi tare da yiwa diyana suma dawafin neman shiryuwa a gurin Allah tare da sa masu albarka arayuwan su,,
Gashi ko da,alaman Allah ya karbs min addua,a na don duk abinds na roka naga faidan shi a rayuwa na yanzu,
Abu daya ne shine baiyyanan mahaifina da har yanzu bai dawo ba kuma ko labarin shi babu,
Abin wani lokaci yana matukar damun zuciyana sosai saidai ba yadda zanyi dole nai hakkuri nabarwa Allah,

****** ********* ******
Kamar yadda Bibs ta kwalafa rai ga zancen zuwa makka shekara mai zuwa hakan bai samu ba don cikin dake jikin ta ance gwaunati ta hana mata masu ciki zuwa saudiya bana don matsalolin da ake samu acan da su,
Ba yadda batai masifa ba tana cewa ai ance in anbada cin hanci ana bari mace taje yace to shi bazai ba kowa cin hanci ba,
Tabari in Allah yasauke ta badi sai ta tafi inda rabon zuwa, case din har gurin mahaifinta takai karan Hamza amma yace wallahi bai biya sai bata da komai
Haka ya sata ido ga bado ido ga ruwa ga makka ga ciki tarasa wanda zata zaba daga ciki da kyat uwarta ta,taushe don da tace sai dai ta zubar da cijin taje makkan ta kawai intadawo tayi cikin ai,
Ina zaune ranan banjin dadin jikina sai gashi ya,shigo gidan yana,waya duk da,waya yake sai da nai mashi sannu da dawowa yavamsa min cikin lumshe idanuwan shi yazauna gab dani kadan,
A yadda na fahinci wayan da wani ma,aikacin hukumar alhazai yake wayan nashi,
Sai da ya kare yace wassh tare da shafan kanshi a hankali yace rangida may zan samu naci wallahi duk nagaji nace ga abinci ka can saman table kanakawo ma nan ne,
Yace da kin kyauta wallahi don yau duk nagaji gashi gobe kuma tunda safe zan kama hanya don wanan karon wani dajine da ake shigo da motoci ta saukin hanya muka samu can gaba da kwatano garin yake an hada mu da,wani mutum da,zai taimaka muna,
Allah ya taimaka nace mashi tare da mikewa zuwa dauko mashi abinci Biba tafito tana wani turo ciki a gaba ta canza tafiyan ta wai ga mai ciki,
Yakalle ta yai murmushi yace maiciki ke nan nadauka kina can kina sa,na,anki ai barci tace cikin dan zubar da miyau data tara a bakinta yanzu naji kamshin turaren ka nasan ka,shigo shine nafito ko kadan zo min da wani abin kwadai na dan sa,a bakina ,
Dariya mukai mata gaba dayan mu nace wanan cikin kan kila dan Baba muka samu tunda har yana jin kamshin turaren mahaifi shi ko a ina ne,
Dan Baba ai halinshi sai shi ni duk yabi ya jagwalgwalani wallahi sai faman kwadan dayake sani gashi kuma uban shi da shegen mako,
Yace yanzu duk abinda nake sayowa kici bai ishekiba sai kin ce min wai mai mako,
Allah yaba Aisha hakkuri da har yau batace min ga abinda cikin ta ke bukata ba tace bata da shine da tace ga abinda take so itama,
Murmushi yayi don ya fahinci haukan ta ya hana taga cikina da har yafito a cikin zani na yafan turo don yafi nata girma sosai,
Kitchen ta nufa tana fadi bari dai na nemi abinda naci tashige yana cewa sauniya kawai kanta kawai ta sani ita,
Yashige ya kwanta nima natafi waje don na wanke kayan yara da suka dawo dashi school,
Ibrahim yashigo gidan yana ta,sallama ya kawo mai wasu takardu daya aike shi dasu,
Biba tafito daga dakinta zata kitchen suka hade sama sama kamar kullun suka,gaisa dashi, yace ta sallamo mashi Hamza saicewa Biba,,
Bazan tashe shi ba don ya samu barci kaje idan ya tashi sai ka dawo anjima mamaki ya kama shi yace kamar ya bazaki fada mai gani nazo ba, yafa san da zuwana ,
Nace bazan tayar dashi ba ranshi ya baci yaduba dakina bani ciki yafita ranshi a,bace,
Sai gurin Umma yaje yana fada mata abinda yafaru tace yaje yai hakkuri ,
Saida yamma da yadawo yasamu dan uwan shi a falo yake fada mashi ce bata da wayyo nan yabashi hakkuri yace ba komai amma sai tagane kuren ta,
Inajin su don ina tsaye ina gyaran falon banyi magana ba don ba abinda ya shafeni bani bane inji yan conversations din sauratan mata sun min fada na rage shishigi kada su yi fushi dani,sunce na faye rawan kai😜
Zan shige naji muryan shi yana fadin zo mana humaira,
Juyowa nayi inda suke nazo na zauna a hankali saman daya daga cikin kujerun leather cushion din dake mamaye a,falon bakake,
Yace gobe idan Allah ya kaimu kije gurin Ummi kice suyi passport ita da Baba don ina ga tare dasu ne tafiyan bana,
Da sauri nadago kai na dube shi yace ko bakiji bane nace yaya makka zasu kake nufi yace shi nake nufi mana,
Ban san lokacin da na zube kasaba nace yaya nagode nagode kwarai da ,,,,,,
Hannu yadaga min yana cewa may nene haka Humaira don zanbiya wa uwata makka shine zakiyi min godiya may yasa dana biya wa Umma baki min godiya ba sai wanannan,
Murmushi nayi cikin murna nacewa Ibrahim yaya katayani godiya don Allah,
Saiga Biba bull tafito tace may yafaru ake godiya tana kallona ina rusunne a gaban maigida, da sauri naji Hamza yace ba maganan ki bane wanan,
Kallon tuhuma tafara yi muna gaba dayan mu yace wa Ibrahim kajirani mu fita tare akwai inda zamu dama,
Yashiga dakin shi yafito tare suka tafi batare da Biba taji abinda take son ji ba sai tuhumar mu takeyi,
Suna fita tace dama ai ba yau akafara cin amana ba a gidan nan koma mayye ai ji za a yi,
Azuci nace badai yanzu ba kan na kasa fahintar dalilun dayasa yaki fada a,gaban ta da,suka fita yake cewa Ibarahim ko Umm kada ka bari taji zancen nan sai in lokaci yayi,
Nima da dare da yashigo yimin saida safe yake ce min kada ki bari kowa yaji zancen nan sai in lokaci yayi,
Mun bar zance wa iya mu na tafi gurin Ummina munyi yadda yace muyi itada Baba nakawo mashi daga gidan mama Rahama ya kwashe su zuwa birnin kebbi yin E passport,
Salin alin aka gama komai na,tafiyan su batare da surutu yabi gari ba, muna jiran lokaci,
Umma ta shigo gidan mu akan zancen auren Sa,a datu sai dai bata san cewa yasamu yin tafiya don dama ya sallamay ta yace ko gobe ko jibi zaiyi tafiyan,
Sai gata,tazo bayan ya wuce a lokacin ban gida na shiga makwabtar mu yin barka an haihu kwana hudu yau ban shiga ba,
Don haka Biba ce kawai a gida sai Tv dake aiki shikadai a falo yara suna islamiya gaba dayan su,
Jin shirun da,tayi tana ta sallama sai ta leka dakina amma a,rufe yake don ban yarda nabar gida dakina a bude kamar yadda nakeyi a can baya, don itama haka naga tazo da sallon yi,
Dakin Biba ta nufa ta daga labule tana ciki zaune tana waya ta daga kai ta kalli Umma taci gaba da wayan ta, hankali a kwance,,
Habiba bakijin ina sallama ne tun dazun nashigo ba,wanda ya amsa min ,
Biba tace najiki ina waya ne da uwata sai tai sallama da wayan ta juyo gurin Umma dake cewa, eh lalai ashe kin kai can habiba,
Jinan Umma wallahi ni ban yarda ki shigo har dakina ina fama da kaina zaki aza min masifan ki,
Ni dai danki nake aure bake ba don haka wallahi ban yarda da zancen ace uwar miji tazo tana ciwa matar dan ta mutunci don ba ita ta haifeni ba,
Don Allah ki fita min daga daki kada kuma kice nai maki wani sheri ko,
Umma tace har korana kike a dakin ki yau Habiba don wuyanki yai kauri ya isa yanka ko,
Nan tafara tafa hannayen ta Umma nace ki fita,ban son fitina haka kawai don tsegumi da bani bani baki iya zama gidan ki kullun mutum yana yawa gidan sarakai babu ko kinya ni wallahi wanan abin ya isheni a gidan nan,
Uwarki ce mai yawan gidan sarakai ai nace uwarki ce mai kwadayi nikan wallahi ba uwata ba, sai dai uwar wa ke nan,.
Tace ni dai nace ba,uwana ba,wallahi abinda naji ke nan nace subbahanallahi Biba kanki daya kuwa tace da,akayi may fa,
Jinan maman Jidda kada kisa bakin ki cikin wanan magana kinji na fada maki,
Nace Amarya kibar wanan hakin don ba halin tarbiya bane kema fa watarana haihuwa zakiyi tace na haihu mana
Ko na haihu Allah yarabani da halin wanan kullun mutum yawo gidan dan shi yana aikin saka ido haka kawai za,a fado min daki ace wai nabar waya da uwata ,
Habiba yau ni kika zaga a gidan nan ba laifinki bane don ni najawa kaina hakan,
Tace inma kince nazage ki na zaga din don dai ni ba uwata ba, sai kawai umma ta fashe da kuka tana cewa Biba tai mata cin mutinci,
Da kyat na samu Biba ta shigd dakin ta tana fada tana cewa wallahi ita batayarda a zage ta ga banza,,
Umma tana kuka tana share hawaye da habar jibba din ta tana cewa kaman ni Habiba zata kalla tai min wanan zagin haka,
Babu komai bata da laifi nasan inda matsalan nan yafito nace Umma yi hakkuri, tace ai dole Aisha, ina yaron nan yake ne nace Umma bai fada maki cewa yau zai tafi ba tun safe suka bar garin nan, ai,
Tace yasamu wuce wa yau din ke nan ko nace eh Umma su tafi ko,
Allah ya,dawo muna dasu lafiya nace amin Umma take cewa bari ta koma gida tace dama nazo kan zancen Sa,a datu,
Nace Umm idan munyi waya dashi zan fada mashi cewa kinzo baki samay shi ba ai,
Tace tau nagode ni zan tafi sai dai in yadawo din zamu ga juna dashi don gidan mazan sunce suna son su san abinda,ake ciki,
Nace gaskiyane Umma yakamata su san abinda ake ciki hakana don su san matsayar su,
Nace Umma bari a kawo maki abinci tace barshi kawai zan koma ina ni ina zama gidan ku inci abinci ace kuma gotai,gotai dani nazo gidan ku na baje ina cin abinci,
Nace haba Umma ke da gidan ki tace gidan ku dai kudai keda gidan ku yanzu tunda har ankai ga korana,
Har kofan fita na kaita nai mata sai anjima tafita tana dan maganganun ta,

Sun safi matumin da,akatura su gurin shi a can kasar Ivory cost sun kuma gamsu da bayanin shi saidai abinda ya,daure masu kai mutumin ya iya hausan su sosai kamar ba dan kasar ba,
Yagane suna mamakin shi sai yace nima mutumin Nigeria ne ai zamane yakawo ni nan na zauna,
Amma ni dan kasarku ne sunji dadin zama gidan mutumin kuma sun sha daula a gidan sosai,
Yai masu hanya yadda ya dace su samu saukin kaya haka yasa su tunanen in har suka samu shigo da,motocin su ba karamin dagawa zasu yiba wanan karon kafin su dawo sunyi phouna sosai don sunji dadi bakunta a gidan mutumin,
Ya fada masu cewa zai shiga saudiya don aikin hajji saboda haka ba lalai ne su dawo su samay shi ba a garin,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login