Showing 270001 words to 273000 words out of 299981 words
Sai shima hamza ya ce shima yana ganin in yasamu hali yana son zuwa bana saudiyan don akwai business din da yake son yafara yi a can,
Duk process din da mutumin ya tsara,masu haka suka bi cikin ikon Allah sai ga motocin su da masusukan da suka,saro sun shigo Nigeria hankali kwance ba kamar yadd in zasu shigo da kaya suke shan wahala,ba,
Yai muna tsaraba masu kyau irin na mutanen kasar yazo muna dashi, kowa har yaran duk mun samu tsaraban shi,
Abinda ya,daurewa Biba kai yanzu shine duk kayan da take dasu a cikin kayan lefen ta,sai taga nima ina dasu abin sai ya daure mata kai tare da bata haushin haka,
Watau don son da yake min ma harda lefe ya hada min irin nata kenan, ko ranan da yadawo wani lace da take kuri dashi nata blue nawa light pink nasaka ajikina,
Ta hadiyi rai har tagaji gashi bata,san hakane ba duk ta mulke nata kayan ita, niko yanzun ne ma nafara,sawa,
Sai wanan dawowan Biba taga cikin dake jikina tai matukar yin shock sai dai bata yabbatar da,zargin taba sai lokacin da,taga yadan rugumoni zuwa jikin shi yana cewa ya kuke ya kuma girma,
Murmushi nayi kawai tare da karban jakar kayan shi na,shiga dashi daga ciki,
Inda take zaune tana dariyan yake ya nufa yana ce mata tare da riko hannun ta wai duk nauyin cikin ne ya hanaki taro na yau,
Tace ai kasamu taro gurin dayar mai cikin hmmm lalai ma ashe ko akwaita gidan nan ,
Daki ta shiga tafara kiran uwar ta hankali a tashe take fadin Mummy yanzin ashe makirar matar nan cikine a jikin ta amma ta boye min,
Uwar tace ta boye maki ko suka boye maki don ai mijin yasani amma bai taba fada maki ba,
Har da kukan ta,wai wani muna funcine nake shirin kulla mata in bashi ba yaya za,ayi nai ciki amma bata sani ba sai yau da Allah ya nuna mata,
Dakyat uwar ta shawo kanta tare da bata hakkuri akan haka din, cewa tafita batuna taji da zancen cikin ta kawai ta,samu Allah ya rabasu lafiya da cikin dakd jikin ta in diya ne bagashi zata,fara haihuwa dash ba to may zai damay ki tun da likita yafada maki namiji zaki haifa,,
Kin ga ita ko diya mata take ta zubawa ko yaushe sai fa in kin so ki tayar da hankalin ki,
Bayan kwana biyu kuma sai ga zance tafiyan su Ummi na saudiya ya bullo ranan kan hauka tai mashi yana daki kwance ta samay shi da kukan ta,wai yaci amanan ta yaya zaikai iyayyena makka ita yaki koda daukan uwarta yakai,
Yace ummmwumm ashe son kaki har ya kai can sadiya to ban biya ba,sai ki kaini kara duk inda zaki kaini, don ni fitinan ki wallahi ya,ishe ni Biba,
Tafada tai zage zags takiramu da macuta azzalumai mayaudara da dai sauran su harda fata tayi Allah yasa in su Ummi sun tafi can zu mutu,kada su dawo,
Agidan su Ummi ma sai bakin ciki da takaicine ya rufe su mama saude tafara tsegumi wai kilama asiri Ummi tai mata sukaki yarda ya auri kubura don Ummi ta bashi ni
Baba yacewa mama yaukuma saude dan maysiyanta da kukace a,wancan lokacin don kinga yanzun Allah yai ikon shi a kanshi shine zaki fadi hakan,
Umma kan tayi iya nata jidalin tagaji tai shiru kuma tasa shi sai yaiwa Sa,a duk abind ta lissafa ma shi ba bata lokaci sai da yasayo komai,da,ta,lissafa maShi yasayawa, Sa, datu din,,,,,,,
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABUIDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE HAKAN CIN AMANA NE,,,,,
Umma tayi kuka bayan ta koma gida ranan har tagaji tasan cewa itace ta jawa kanta don ba abinda bata fadawa wa Biba a kan al,amarin gidan a lokacin tana ganin Biba zata mara mata,baya ta cin ma manufarta na kawar da ni a gidan,
Amma,uwar Biba taiwa yarta kashedin hakan tace duk kika yarda da hakan wallahi ke sai naki yafi muni a,tsakani ku,
Na horeki ki kiyayi wanan matar don ba alheri take kokarin shuka maki ba,
Shiya ashe Biba ta tsani Umma don uwar ta ta fahintar da ita ko waye Umma din,
Koda Hamza yadawo yaje gaida ita sai Umma take fada mai irin cin mutuncin da Biba tai mata,
Hamza bayan yagama saurare duk da,ranshi ya baci amma,sai ya daure yace, a,a Umma Biba fa yarinyar ce karama kikace nayi hakkuri da,duk abinda tai min a gidana don haka ke ma Umma don Allah kiyi hakkuri yarintar natane takawo gare ki,
Ya mike yana cewa ni zan koma dama,nashigo nan gurin Baba Mudi ne kin san bana ina son su sauke farali insha Allahu,
Da sauri ta ce wani Mudi kuma yace Baba Mudi dai mana Baban Aisha, nake nufi dashi da mahaifiyan ta gaba daya zasu tafi tare da mama da Jibrin,
Sa,a datu sai in Allah yakai mu sutafi da Biba lokacin ta yi aure,
Wai ko yaton nan kasan ciwon kanka haka kawai don kudi suna maka kaikayi zaka kwashi kudi kace kabiyawa Mudi kudin maka shida uwar matarka,
Umma kudin nawaye ina kudin yarsu ce yakaini ga haka ko abinda yafi haka zan iya masu muddin ina da halin yin su,
Yace ni zan tafi akwai inda nake son zuwa umma sai cewa take ga iyayyenka maza a gari baka kaisu sai wasu don ka,gwadawa mutane kai dan dadin buje ne ko,
Yace aiko tellan ya iya dinka bujen ke nan yafadi a zuciyar shi,
Nan yafitar yabar ta tana ta faman masifa da jidalin wai an mallake sai yadda aka,ga daman yi dashi baida fadar kan shi,
Tai tsuki tace ita wanan banzan Biban da ya dauko bata san ciwon kan ta ba ma balle na wani,
Duk da ya hasala da abinda Biba taiwa Umma sai ya ke kokarin share zancen don bai iya daukan mataki a halin da take ciki ga tsohon ciki a jikin ta,
Biba sai jira take yai mata magana don tasan cewa Umma ta fada mashi komai yadda,sukayi amma abinda tayanke zata fada mai shine Umma karya take mata da,sheri,
Tace Umma ce tazo mata da wani zance da bata yarda dashi ba haka ta kulla a ranta,
Sai dai bazaman lafiya don gani take Hamza da Aisha yaudaran ta suke suna cin amanan ta kawai,
Abin yakai su har saida iyayyen ta suka zo a wani dare ana sulhunta su a dakin ta ake zance amma zakace a tdakar gidan mu ne saboda yadda Biba ta daga muryan ta tana kuka tana magana,
Wallahi gwago bai daukeni a matsayin matar shi nake ba don banbancin da yake muna,
Komai yasamu sai Aisha da diyan ta kawai yasani sai yan uwanta gwagon nata tace a dama ke yaya kike so so kike ya,watsar da iyalin shi saboda ke,
Kinki kwantar da hankalin ki kina bin rudin shedan yaya kike son gani dama,
Kuma mu mun san yana muna duk cikin mazan yan uwan ki bamu da kamar shi wallahi,
Idan ke baki ganin abinda yake maki mu muna gani, don mun san yai muna,
Kishiyar ki kuma batai muna komai sai alheri don ba mai zuwa gidan ga yace tai mai wani keko fa kinawa nata mutunci yadda take muna,
Ni ban ma gan su ba balle inji Biba din sai dayar matar tace kingani basu ma zuwa ke nan,
Gwago duk muka tashi magana sai yace min wai shi bai iya yiwa matarshi komai don da ita yake tunkaho,
Hamza dake gefe zaune yana wasa da hannun mimi da yashiga da ita dakin yai murmushi zuciyar shi tana mashi soya,
Kin dai san yadda gidan ku yake kece uwarki tafara yiwa aure idan baki kwantar da hankalin k8 ba kika bantale auren ki dake da ita sai ai maku dariya,
Sai lokacin yai magana yace wallahi gwago tausayin mummy nake ji amma ita batasani ba don koyaushe tana kirana ta bani hakkuri,
Amma ita bata san hakan ba burin ta kawai taga tatayar muna da hankali a gida ,
Itace kullun akewa laifi ita ba taiwa mutane batasan hakkuri kowa keyi ba,
Yadda kike nufin na wullakanta mamata saboda ke na fada maki hakan bai yuyuwa don ni batai min komai tsakani da ita sai rufin asiri da zaman lafiya don wallahi tunda na,auri Aisha ba a taba shiga tsakanin mu ba,
Gwagon ta tace tau ke kinji ke ko aure ko shekara daya ba a rufe ba kin cika mashi gida da hayaniya, wallahi habiba kiwa kanki fada Allah,
Ashiru tayi sukai mata tas akarshe sukace taba mijin ta hakkuri yace ai babu komai ni dai na fada mata komai lokaci ne, idan na samu yadda nake so a gareta komai zai wuce ne,
Kwana biyu kamar ta daina a na zaman lafiya da kowa a gidan ba wani matsala kuma sai dai ance mai hali baya barin halin shi don ita kishi halin ta ne karara, take nuna shi ko a bako ne balle mu yan gida,
Tafiyan su mama yazo don haka banda zama gida sai faman zirga zirga nake ban gidan mu ban gidan su Umma, don ganin komai ya kammalu,
Sun tashi lafiya yabani kudi nakaiwa Baba yabarwa iyalin shi tare da buhuhunan abinci da zasuyi amfani dashi,
Tun ban fitaba Atika tace bata yarda ba saidai a raba aba kowa nashi kada diyan mama saude suzo su kwashe ,
Tana nufin su kubura wace yanzu mijinta komai ya kara dagule mashi tayi yaji tayi fitina ya sake amma yaki sakin ta,
Sai bakin wahala da sukeyi don sai sun nemo da kan su sunci har dashi saboda yanzu ba,a harka dashi ga sabbin matasa masu irin harkokin shi sun taso,
Dole baba yasa a raba masu kowa ta kwashi nata zuwa dakin ta dashi kudi ma,sun raba ganin haka nacewa Ummi zan tafi dasu yan biyu gidana na zauna dasu harta dawo, tunda abu ya koma haka,
Ummi tace nima tunanen da nakeyi ke nan don da gidan Anti naso na kaisu amma kuma itama tana fama da kan ta,
Ummo taje tafadawa Baba yadda mukayi yace shima haka yafi mashi kwanciyan hankali
Ban dawo gida ba ranan saida yaran da kayan su sai dai ban kwaso duka ba,
Ganin yaran ya tayarwa Biba hankali ta samu Hamza a daki tace wai na cika gida da yan uwana da diyana an mayar da ita boya,
Ya dago kai ga abinda yakeyi yace haba BIBA Biba ke na gane problem ce,
Kin zama Biba PROBLEM wallahi komai kice ke an kun tata maki to naji badai girkin bane matsala tace to kai bakaga yadda nake bane yace angama,
Da dare ya hadamu a falon shi yace abinda yasa na taraku shine ina son daga yau ku raba kitchen din ku kowa ta dinga amfani da nata nikuma zan sayo kayan abinci na ajewa kowa nata,
Ke Aisha ki girka naki da duk wani wanda yake a karkashiki har ni idan ina dakin ki kiyi dani,
Ke kuma Biba daga yau kiyi wanda zaki iyaci iya ke sai ni idan ina gurinki ina shike nan yanzu zance ya kare,
Gyaran gida kuma already madina keyi ba,wani kyashi ko jin haushi sai taci gaba dayi yadda ta saba,
Ya juya inda nake yace ki min list din komai da ake bukata na amfani gida sai nasa a kawo maku,
Biba tace ke nan nima nayo nawa ko yace akan may zakiyi naki daban nata daban kike nufi k8 bari idan an kawo sai ta cire maki naki, ina shike nan an gama zancen ba wano korafi kuma,
Najuya na kalli Biba wace ke ta wani kumba tana ya mustan fuskan ta sai na gane cewa itacdme ta samay shi da wani zance ke nan,
Kamar yadda yace haka nayi na,saya muna komai yadda ya dace ankawo muna yake cewa shima yana son yai tafiya zuwa saudiya amma ta international yake son zuwa don akwai business din da suke son zuwa can su kullah,
Ana saura kwana biyar ya tafi Biba ta tashi da nakuda ba bata lokaci yangidan su suka zo aka kaita asibiti, ,
Bayan dan lokaci kadan ta haifo yarta,mace bakakirin da ita babu inda yarinyar ta biyo hamza sai uwarta,
Tun bata sauke numfashi ba take tambayan nurse din may ta haifa sukace mata baby girl wani irin abu taji ya soki zuciyar ta,
Haka ta fito daga dakin haihuwan ranta babu dadi ita yar jaririyar sai faman tsula ihu take tana neman agaji,
Babu kowa daga gidan su Hamza kuma kowa yasan cewa za,a zo asibiti da ita a lokacin amma sunki zuwa hakan ya bata ran iyayyenta sai faman masifa sukeyi suna cewa wai lalai akwai kiyayya mai karfi a tsakanin su shi gaiyar aikin shi kadaine yatafi sai abokin shi,
Can yabar su yadawo don ance wai a bari ta dan huta saboda jinin da yake dan zuba mata,
Biba tana kwance a gadon da aka bata a,sibitin wasu yan siraran hawaye suka zubo mata ba wanda yagani sai gwagon ta ta duka kan ta kamar may rada tace,
Amma Allah waddai da halinki Habiba nafahinci hawayen ki na butulcine wa Allah akan yabaki diya mace kike wanan kukan haka,
Tace ba hakana bane gwago tace wallahi maza ki share hawayen ki tun duniya batayi dake ba, sakariyar banza kawai su diya matan da aka haifa mashi kinga yakai su jujin da akeyar da su ne,
Bashiri tafara dan kakaran dariya a fuskan ta don bata san za,a iya fahintan taba amma ina har sun fara yin rada a kan ta,
Saice mata suke dan baba yafito da dabe sai yaya kuma tace wanan ma yar baba ce ai,
Ya dawo gida yake sheda muna an haihu lafiya muka hau murna da farinci sai dai ban tambayi mai aka haifa ba,
Sai doki da murna kawai mukeyi yakalle ni cikin sha,awa da tausayi yadda nake nuna farin cikina ,
Dago kai ina cewa yau Amarya ta huta da nauyin ta saura ni kuma Allah ka saukeni lafiya kabani mai albarka,
Yace amin su Jidda sun samu kauna ya fadi cikin lumshe idanuwan shi nace a, mace Allah yabamu,?
Allah ya raya muna ita yasa mata albarka yace amin Aisha amma ai ita uwar diyar naga batai murna ba sai fushi takeyi,
Akan may natambaya yace ba ta haifo maki magajin da tace ba mana ya wuce shi takewa bakin rai,
Yanzu suna ina yake ce min tana can ance abari ta dan huta tukunna sai anga yadda ta kasance tadawo,
Nan nashiga buga waya ina fadawa mutane Amarya ta haifo ban bari su tambayeni sai na kashe wayana,
Umma tanajin an haifu cikin kaguwa tace may aka samu yace mata mace,. Shiru tayi babu ko Allah ya raya,
Dariya yayi bayan ya kashe waya yace Umma ke nan haryanzu dai tana ga akidar ta ke nan,
Sun dawo gida da yar jaririyar baka batada kama dakowa amma sai naji yan uwa Biba suna fadin wai yarinyar tana da kama da mimina,
A zatona yan uwan shi zasu shigo ko don dan uwan su da akaiwa haihuwa amma babu wanda yashigo gidan ranan,
Washe garima basu shigo gidan ba sai wajajen karfe biyu sukazo ganin baby nasan daga gidan Umma suke,
Matsalar da akasamu shine nadai yi masu abinci dadare na basu amma da rana Anty hindatu ta hana na basu,
Shiru shuru suna jiran nakawo masu abinci basu ga na shigo dashi ba ga yarana zaune falo suna cin tuwo shimkafa da miyar agushi yaji manja da nama hudun gudun,
Gwagon ce tafito take ce min Aisha sai naga har yanzu ba,a kawo wa maijego abinci ba dai,
Nace a gwago ita Amarya bata fada maku cewa girkin mu ba,a hade yake ba don haka ko na jiya dai na taimaka ne nabayar kawai,
Subbahanallahi inji gwagon tana cewa ya akai haka kuma, gida daga ki sai diyan ku ace an raba girki nace gwago matsalar yarki ce itace ke da bukatan hakan don ra,ayin ta ne,
Gwagon ta juya zuwa dakin dake cike taf da jama,a sai hira akeyi tace Habiba yaya tsarin gidan nan yake maku ne wai don nasamu kishiyar ki da zancen abinci take ce min wai ba hakkin ta bane hakan,
Gaba daya dakin tsit akayi ana sauraren zancen gwagon sai yan katsalanda suka fara cewa wai ga zancen banza may take nufi da fadar hakan,
Gwagon tace ku dakata koma may ye ai ita habiban tasani don dole akwai matsala ai,
Ita ko Biba cewa tayi ga yar iska kawai yar rainin, wayyo bari na fita nai mata magana may take nufi,
Wasu suka ce a,a kira mijin ku kawai ki hada yar iska dashi amma ta yaya za,a haihu kice bakiyiwa yar uwar ki girki saboda kishin tsiya,
Kiran Hamza tayi yadauko yana fadin salamu Alaikum, tace amin wa,a laikun sallam my kana ina ne,