Showing 273001 words to 276000 words out of 299981 words

Chapter 92 - Sarautar Mata By Makawa

04 Dec 2025

17652

Don Allah kazo gida don akwao magana saboda Aisha ta hana min abinci ni da yan uwana,
Yace kamar ya bata baki abinci ba kuma zata fara magana yace ke ganin zuwa ajirani nazo ya kashe wayan kawai,
Sai da ya,dan dauki lokaci yashigo gidan da sallama ina dakina kwance don hadarin da akayi ba ai ruwa ba yasa wa garin ni,ima,
Hakan yasani jin dadi har barci ya dan kwashe ni ban sani ba duk da yaran suna ciki suna kallo don na hana su zama falo don ina gudun su ja man fitina,
Yaran suna gaishe shi amma duk banji sai da ya karaso inda nake kwance yaja min kafa a hankali idona da nauyi barci na bude su kyat yana tsaye a kaina yake ce min,
Wai may ke faruwa ne naji wanan ta kirani a waya wai ko zancen abinci,?
Dan tsuki nayi ina mikewa nake cewa wai kamar ya abinci cikin matse fuskana yace min zo muje falo muyi magana a can,
Da kyat na samu na mike zaune ina daukan dan kwalina da ya zamay a kaina nabi bayan shi nasan yace mu fita dakin ne don yaran dake ciki suna kallo,
Dakin Biba ya leka yace su zo ita da gwagon ta suka fito a tare muka shigo falon da su lokaci guda,
Yace maynene kike fada min awaya ne wai don ina a cikin mutane banji sosai,
Tace wanan yar bakin cikin matar taka mana ta ki dafa muna abinci ga mutane a dakina har ni kaina banci komai ba,
Ya juya inda nake yace Aisha yaya akai hakane wai,
Nace ban gane yaya akai haka ba ka manta cewa tace bata son hada girki damu ne ko kuwa dan ina Aishan sokaye sai naje mata girki tace wayasani,
Ko kuwa don ina neman suna sai naje girka maki abinci ki koro min shi don nasan ba zai maki wuya ba hakan,
Munafuka dama,muna funcin da kika hada ke nan ashe ban sani ba ai dana sani da nasan shirin da zan maki nace to ai yanzu kin sani don haka sai ki shirya da kyau,,
Badai haka kikace ba akwai zamu zuba cikin gidan nan ni da dake shege ka fasa munafukar banza da wofi kawai,
Ke yadaka mata tsawa cikin wani irin murya mai firgitawa, yace da idanuwan shi da suka kada sukai jawur tare da nuna mata dan yatsan shi,
Wallahi Biba ki shiga hankalin ki ke wallahi kin isheni kin isheni a,rayuwana wallahi nayi dana sanin auren ki wallahi,
Fitinar ki yakai min ko ina wallahi ace mace bata da,aiki sai kirkiro jidali
Wallahi bari kiji ban auri macen da zatazo cikin gidana ta,wullakan ta min matana na ba,
Wai ashe matace ai ban sani ba take idanuwan shi suka kada sukai ja yace ashe baki sani amma daga yanzu zaki sani ai ban san baki san matana bane tun farko,
Ya kada kai yace ba komai zan fahintar dake mutanen dake dakin ta suna jiran aci min mutinci sukai tsit suna sauraren mu,
Ita gwagon ta sai fada takewa Biba tana cewa ashe banda mutunci a idon ki habiba,
Yace gwago wanan yarinyar bata da mutinci sam bata son a zauna lafiya a gidan nan,
Gata a tsaye ita da kanta tai tsaye kan sai na raba girki a tsakanin su don ita bata iya girka abinci Aisha da diyan ta suci,
Don gudun fitana badon tafi karfina na yarda aka raba don may kuma yanzu zatace wai Aisha ta girka mata bayan kowa na bashi wanda zaiyi amfani dashi a kitchen din shi,
Don may yasa na yarda da hakan badon kawai a zauna lafiya ba ta manta da irin wanan ranan lokaci da take kulla tsiya a ranta ko,
To Aisha bazata girka maki abinci baki bari itama in ta haihu kada ki girka mata bashi ke nan, ba,
Dama ai ance inzaka gina ramin mugunta gina shi yazam gajere,
Ya juya inda nake yana cewa koma dakin ki kawai shike nan zan san abin yi,
Nace tare da jefa mata harara nace baki da,wayyo Biba da baki wanan haukan ba sakariya kawai,
Nasa cikina gaba na shige abina nabarta nan tana haushi kamar karyan da ta haihu,
Nashiga dakina ina mai jin haushin wanan halin na Biba sai dai ba yadda zanyi don zama ya hadamu sai hakkuri kawai namiji mai aure aure tun yana auro na kwarai dama,watarana sai ya,auro manya, da zata cinye shi ta cinye mutanen gida,.

Komai na shagalin buki a hannu na yabar shi wanda za,ayi a cikin gidan nace bazan karba ba yace shi tsarinshi ke nan,
Don haka duk abinda za a aiwatar nice zan aiwatar dashi ke nan, ya bani wanan damar,
Yai muna sallama yatafi sauke farali kasa mai tsarki shida wasu abokan shi,
Data kirashi kan yaya za,ayi yace ki tambayi matata na bar komai a gurin ta,
Haba ina wuta Biba ta sakani ranan nasha balai da masifan zagi a gurin ta kamar zata cinye ni dan ya,,
Sun kira shi akan don may zaiyi masu haka yace don tasan cewa Aisha mata ta ce shiya na lurar da ita cewa a,tare ta samay mu,
Doleba yadda za,ayi suna ji suna gani dole suka barni ana karban komai a gurina daga su har yan uwan shi,
Anyi suna an watse lafiya yarinya taci sunan mama hafsi bakin ciki a furin Biba bai missaltuwa don har cewa tayi anyi hakane don aci mata fuska an sawa yar ta sunan mama hafsi,,
Sai faman nuna ni aje gani da cikina,tsiriri sai bina da idanuwa kawai akeyi kowa da irin abinda ake fadi a kaina,
Nikan ina dakina da mutane na abokan arzikina da suke tare dani muna hurdan alheri,
Yadda taso ayi shagali na gani na fada hakan bai samu ba don babu halin hakan daure ko ina don ya hana mata kudin komai sai cewa yayi duk abinda za,ayi a tambayi Humaira zata bayar,
Ita kuma kishi ya rufe mata ido bata iya tambayan na komai don fadin rai irin nata,
Haka akai shagalin ba,wani abin azo a gani na shagali da akayi kamar ba gidan mai hali ba,

****** ********* ******
Asaudiya bayan ya isa ya samu su mama hafsi da su Ummina a masaukin su, yakara masu kudi akan wanda aka basu guzuri na mahajjata,
Kamar yadda suka tsara haka akayi don sunyi Meeting kan harkan bunkasa harkokin business din su,
Suna gurin Meeting din ne aka bugo mai cewa Baba Mudi baida lafiya don haka ana tashi yace zaizo yaga surukin shi don baijin dadi,
Sai suke cewa ya,shigo su rage mashi hanya su sauke shi sun tafi masaukin sai babba daga cikin abokan nashi suke cewa bari su shiga,su gaida mara lafiyan,
Gaba,dayan su suka,shiga dakin don ganin jikin Baba dake fama da zazzabi da mura,
Mama hafsi da Ummi suna dakin a lokacin sai dai jin mazane suka,shigo dakin yada,su juya bayan su,
Suna tsaye mutane suna magana suna gaida baba daya bayan daya sai babban nasu yake fadin,
Manene likita yace yake damun shi muryan mutum yasa Ummi saurin dago kanta dake duke don murya ne na mutumin da bazata taba mantawa dashi ba murya ne na mutumin da taki jini a,rayuwan ta da can baya,
Sai dai kuma,shi wanan murya hausan ta yasha banban da muryan wanda take tuhuma saboda hausanshi a kwai surki a cikin ta,
Saidai ta dan davo kai taga wake da wanan muryan mai balain kama da nashi haka,
Fuskan shi ne karara duk da ya kara kiba farin shi ya kara fitowa ya koma wani babban mutum a idanuwan ta,
Bata san lokacin da tace, yaya Bello dama kana raye a duniyan nan kabar gida kabar yan uwa ka kabar kowa naka a gida hankali a tashe,
Kallonta yake acikin mamaki bashi ba harsu hamza dake dakin kallon mamaki sukewa Ummina,
Sai da yai murmushi dama murmushi halin shi ne yake cewa wanake gani kamar Fatima,
Sai kallon ya koma akan su cikin mamaki ya nuna ta da yatsa a cikin harshen yaren kasar Ivory cost yake ce masu sister din shi ce kuma matar shi ce ta da har sun haihu da ita,
Gurin da Hamza yake tsaye yai mutuwar tsaye a lokacin yace ma hamza din a ina kasan yar uwata wanan yar uwatace kuma matata da muka rabu har na haihu da ita,
Yace nafada maka cewa ni dan Nigeria ne tun farkon haduwar mu ni mutumin yankin sokoto ne zamane yakaini kasan da ka ganni,
Har Allah yai min arziki haka ina kuma da iyali a can din yanzu haka,
Sai kallon mamaki sukewa mutumin harda Baba mudi dake kwance saida ya dan mike zaune yana cewa ikon Allah dama kana raye ake nemanka an rasa inda ka,shiga Alhaji Bello,
Ya nuna Hamz yana cewa wanan da kake gani surukin kane mijin yarka Aisha wacce yanzu take da yara biyu na,uku na cikin ciki,
Shine kuma yai muna,sanadin zuwa sauke farali ta hanyar arzikin da,Allah yaba shi,
Zaune mahaifina ya kai daga tsayen da yake yana cewa ikon Allah Alhaji Hamza dama kai nawane ashe Allah mai iko,
Dalilin da yasa ke nan ashe naji ka kwanta min a rai abinda ban taba yi ba aruyuwa na don ban yarda sam da mutanen,Nigeria saboda sun faye yaudara,
Hamza yaji a take wani nauyi da kunya ya kamashi na mutumin, da aka kira da sunan surikin shi a gaban shi,
Ummina ta kara cewa haba yaya Bello kabar gida da yan uwa a ciki tashi hankali har yau suna a cikin bakin rashin sanin in da kashiga a,duniyan nan,
Murmushi kawai yake yana dan buga kafanshi a hankali, tare da tunanen abinda ya faru tsakanin shi da yayan shi shekarun baya da har yai mai gorin arziki akan gona,



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABUIDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA PLEASE DON HAKA CIN AMANA NE,,,,,,


ALLAH ya dawo muna da shi lafiya mun tare shi a cikin jin dadi a can yabar su baba sai jirgin mahajjata na hudu zasu dawo,
Sai da yai wanka ya huta yaci abinci don lokacin, yamma tayi da ya iso, garin,
Daki ya samay ni zaune gurin da na idar da sallah na tasa cikin da yai mai girma a gaba sai damu na da motsi yakeyi,
Ya shigo dakin saye da sabon jallabiyar shi, fuskan shi dauke da murmushi yana min kallon kauna a fuskan shi,
Yace wanan cikin Humaira nake ganin kamar yafi na su Jidda girma sosai don baki taba ciki haka yai girma ba,
Nace cikin ya mutse fuska wallahi nima haka nake ji ga kuma shurina da ake kamar ana kwallo dani kayan ciki na,
Dariya yayi yace kila dan kwallo kika samo min wanan karon nace ni uwar diya mata ne fa inji Umma ka manta tace mata zanta haifa ma tunda suna fara dasu,
Shirmay ke nan zancen Umma wake shiga daki dashi tunda ba itace Allah ba,
Yace ni har ma kin bata min rai wallahi ko diya bata dozen za,a haifa min ni ina maraba dasu Allah yabani abinda zan duba tarbiyan su dashi kawai,
Yace ke nazo ne fa in maki wani albishir na gyara zama ina cewa masha Allahu tun ban ji may zaifada min ba,
Yace amma sai naji goron da za,a bani tukun don ba karamin albishir nazo maki dashi ba,
Nace to may zan baka tunda na fahinci abin babban yadda naga kayi serious akai,
Yace cikin shafan fuskan shi kema aikin san abinda zaki bani ya wuce kibani jikin yau namora son rai na,
Dariya nayi nace kai wallahi yaya baka gajiya da wannan har kan kai yace ina zan gaji da bautar Allah Humaira,
Nace yanzu dai fada min albishiri din yace to kema kin yi alkawari ko nace ai wanan tun ranan daurin aurena nai alkawarin hakan yace good,
Tau nafa ga Abba Humaira nace cikin tambaya Abba wani Abba ke nan yaya yace Abba Bello mana mahaifiki,
Wani, irin zabura nayi daga zaune na mike tsaye don har na manta da cikin da ke a jikina a lokacin,
Nazo gap dashi nace wai da gaski dan Allah dai yaya,?
Yace wallahi Allah har Ummi ma da baba sun ganshi don muna tare dashi,
Wani irin ihu na tsaga sai kuma ga hawaye shar sun zubo min ban san lokacin da na fada jikin Hamza ba,
Ihun danayi ya jawo hankalin kowa a cikin gidan suka yo dakina har Biba da gwagon ta dake zaune damu a gidan suna tambayan ko lafiya,
Ganina sukayi rugumay ajikin yaya ina kuka yana dan bubuga min baya a hankali kamar karamar yarinya,
Azaton su ko Ummina ce ta mutu a makka don har Biba tafara fadin gwai muga karshen bin bokaye,
Gwagon take tambaya sai yadan dago fuska da murmushi yana fada mata cewa mahaifinta da ya bata shekara da,shekaru, tin tana goye ne ya,baiyyana,
Allahu akbar inji gwago din tace Allah may iko sai biba ke cewa a,saudiya yana takari ko?
Wani kallo yai mata yace ko a inane ai angode Allah tunda ya baiyyana dai,
Gwagon ta,shiga fadin wanan abu yai dadi gaakiya,ikon Allah ashe yana kasar Saudiya ke nan duk dadewan nan,
Sai Biba tace ai hakana mutanen mu ke yi sai ki ga, don wahala da kwadai mutum yabar gida ya koma can yana watsar da kai don son abin duniya,
Abin yai min zafi a,rai amma yanzu ba lokacin mayar da martani bane agareni lokaci ne na farin ciki da godiya ga Allah ubangiji talikai,
Shiru yabiyo dakin gaba daya har yara duk suna tsatsaye suna kallon yadda nake kuka yana lalashi na,
Yace ai gwago mahaifin Humaira ba saudiya yake ba yana nan kasan Africa zaune,
Rashi sani bayau bafa nasan shi don a,gurin shi muke sarin motoci can kasan ketare da muke zuwa ,
Biba ta wani cewa may ne,?
A gurin shi fakace kuna sarin motoci da kuke shigowa dasu yace kwarai kuwa don shi ya na cikin mayan dilolin kasan Africa da aka sani,
Shi mahaifin Aisha din Biba ta tambaya yace mata kwarai ban san lokacin da nakai gurfane a kasa ba na fara rusa wani irin kuka mai tsuma zuciyan mai sauraren ta,
Cikin kuka nake cewa Allah na gode maka da ka baiyyana muna da Abba lafiya,
Biba bata kara magana ba tun lokacin da taji amsan da ya bata atake,
Cewa tayi gwago muje Allah ya kyauta , kawai tafita daga dakin sai gwagonta dake tsaye tanace min kiyi hakkuri haka Aisha ki godewa Allah,
Yace mata ai kukan murna takeyi shi yasa nabarta tayi mai isar ta har tagaji,
Tace kaiko Hamza ka lalashe tabar kukan haka kaga ba ita kadai bane a jikin ta kada kukan ya taba abin cikin cikin ta,
Sai muryan Biba take cewa gwago ki fito mana nace mu koma daki tace ai gani tafe ke dai yar nan a tafi abarta tana kuka,
Saida ta dan tsaya tabani magana irin na su na manya sannan tafita daga dakin,
Nai shiru kamar yadda tace ita da hamza yajani zuwa bakin gado na zauna yaci gaba da bani labarin yadda suka hadu dashi har da Umma,
Nace cikin goge fuskan yanzu Abbana yana raye shine ya bata haka yabar gida yabar kowa nashi ya koma inda baida kowa yace min ya fada min yai aure har da yarinya daya da yaro saidai ba babba ba ce nace Allah mai iko ashe harda kanne, gareni,
O, o Allah na Allah na gode ma da wanan ranan dama kullun,
Yace yanzu mabar dashi cewa idan ya koma ya huta, zai shigo kasan nan ya gan ku,
Ranan barci rabi da rabi nayi don murna bai banni nayi barcin dadi ba ranan duk da gajiyan gurzuwan da nayi a wurin maigidan don sai da ya karbi goron shi,
Dasafe tsab na,shirya don zuwa gidan mama Rahana shikuma zai tafi gaida Umma,
A kofan gidan su Mama rahana ya sauke mi har yaran gaba daya su biyar nan mukai mashi sai mun dawo yake cewa idan zamun dawo zaizo ya dauke mu,
Labarin da na bata yasa ta mamaki tace shin anga Yaya Bello kikace nace wallahi mam a har Ummi ma tagan shi sunyi magana tace shine din ma ba tantama shi din ne tunda har Fatima ta gan,shi,
Nan mukaita hiran yadda za ayi dakuma irin yadda ya kwashe shekaru baigida bai kuma waiwayyo gida ba tsawon lokaci yana raye,
Mama tace ai mutane da yawa sina wanan hallin su shige cikin duniya,subar iyalin su ba tare da sin dawo gida ba,
Tace wani ajaline da kasa kan kirashi nisa da gida wani kuma,arzikin shi ne kan kirashi har inda yake walau na diya ko na kudi,
Nace to yanzu mama yaya zamuyi da mutanen gida tace aikiran su zamuyi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login