Showing 114001 words to 117000 words out of 252835 words
it idan kina bina hka, please stay away from me, i don't have any feelings for you now, snn kuma i am married.. good luck..", da haka ya nufi motarsa ya shiga ya bar Eatery din, Ruqayyah taga kamar birds ne suke yawo a kanta kafin ta fara ganin harabar Eatery din bibbiyu daga nan kuma bata sake fahimtar halin da take ciki ba. farkawa tayi ta ganta a restroom na Eatery din mutum har huɗu akanta, ta miƙe zaune tana kallonsu kafin ta dafe kanta, wata mata ce tace "Alhmdllh sannu ko..", Ruqayyah ba ta iya cewa komai ba kawai binsu take da idanu, wani mutum wanda shima staff ne a Eateryn yace "ki bamu contact din wani naki a kira a gaya musu halin da kike ciki..", a hankali Ruqayyah ta girgiza masa kai tace "no need ngd sosai..", ta miƙe da kyar kanta na sarawa, waitress din da itama ke wajen ta miƙa mata ragowar bottle water da aka yayyafa mata ta farfaɗo tace "ga ruwa ko zaki sha..", Ruqayyah ta girgiza kai tace "nagode.." ta nufi ƙofa zata fita, mutumin ya sake cewa "da dai kin jira an kira ƴan uwan naki hajiya", bata tanka masa ba sbd ita kaɗai tasan abinda take ji, da kyar ta kai kanta bakin titi ta tsari napep, ba ta ma gaya masa inda zai kaita ba kawai ta shiga, saida suka fara tafiya snn ta gaya masa inda zata, Ruqayyah na zuwa gida direct hanyar room dinta ta nufa, Momy dake zaune palour ta bita da kallo tace "baki da lfy ne..?", gyaɗa mata kai Ruqayyah tayi, Momy tace "sannu..", room dinta ta wuce zuciyarta kamar an ɗora mata dutse, tayi wurgi da handbag dinta a kan bed kafin itama ta zube akan bed din, Momy ce ta shigo da plate din abinci da ruwa, ganin Ruqayyah a kwance ta ajiye plate din akan mirror ta iso bakin gadon tana feeling body temp dinta, jikin nata zafi ramm, with care Momy tace "zazzaɓi kike ne Ruqayyah..?", Ruqayyah ta yunƙure ta miƙe hawaye na zuba idanunta wani nabin wani, sosai hankalin Momy ya tashi ta zauna gefen gadon, Ruqayyah ta ɗora kanta a kafaɗar Momy ta fashe da kuka mai ƙarfi tace "Momy kiyi haƙuri, am so sorry".
★Ƙarfe takwas da rabi Nurain ya isa gidansa, basket din abinci da ya taho dashi daga gidansu ya ɗauka kafin ya fito daga motar, ya ciro ledar take away na abinci da ya siya baici ba dan tinda ya saka a motar baima bi takansa ba, Inuwa ya bawa ledar abincin ya wuce ciki da basket na abincin gidansu, upstairs ya haura yayi refreshing kansa kafin ya sakko sanye da white pajamas ya shiga kitchen ya ɗakko plate da spoon da drink, saida yayi powering TV snn ya zauna cin abincin, ko rabin abincin bai ci ba ya ajiye spoon din yana kallon stairs, lokaci guda ya miƙe ya haura saman, toh me tasamu taci bayan ya kashe mata gas, har ga Allah mantawa yayi ya bawa Inuwa ya siyo mata Charcoal ko firewood da safe in yaso sai tayi amfani dasu tayi girkin, still yayi a corridor yana kallon ƙofar ɗakinta, ya haɗe gira ya murɗa door handle ya shiga, yayi sallama ƙasa ƙasa, Hajar ta ajiye wayarta kan mirror ta dubi ƙofar, tin ɗazu take kiran Umma amma no respond, suna haɗa ido dashi ta murtuke fuska ta galla masa harara ta ɗauke kai, duk da ya lura da hakan amma he don't care, with a repartee yace "hey..", bata bari taji sauran maganar ba ta katsesa da fadin "can kaje ka nemo hey dinka nan Hajar ce ba Hey ba", Nurain was more than shock jin abinda ta faɗa, furiously yace "young lady, na fahimci kanki na rawa kuma baki da kunya, amma please enough don't try me..", wani irin yamutsa fuska tayi tace "Au haba, so kake na ɗauki mayafi na kirma a ka na rufe fuskata shine zan zama me kunya ko me.." haɗiye sauran maganar tayi ganinsa a gabanta, ita dai bata san lokacin da har ya taho yazo gabanta ba, wani mugun bugu zuciyarta ta fara yi, ta ja baya da sauri tana zare ido, tana ƙoƙarin sake ja da baya ya kama dukka hannayenta ya mayar dasu baya ya rutsasu duka da hannu ɗaya, riƙo bana wasa ya mata ba don ji tayi kamar shoulders ɗinta zasu karye, turo baki tayi tace "malam ni ka sake..", bata gama maganar ba yasa finger ya ɗalle bakin rashin kunyar, tini Hajar tayi shiru tana jin azaba a lips ɗinta, yana ganin ta fara motsa lips alamar za tay magana ya sake ɗalle bakin, gashi ta gagara motsi babban weapon dinta kuma an hanata amfani dashi wato her mouth, motsa lips din ta sake yi nan ma ya ɗallesa, tini lips din kwa sukay jajir, thick eyebrows dinsa a matuƙar haɗe yake kallon fuskarta, wani yunƙuri tayi zata fixge, da sauri ya kuma matseta ya ɗalle lips din a karo na huɗu, lulu eyes ɗinta ya kalla da suka cika taff da hawaye, lokaci guda tears din suka fara zarya kan kuncinta.....✍️
💛 HAJAR 💛
{51..}
Hajar tafi minti ashirin tsaye bakin titi tin fitowarta daga gida kafin ta samu abin hawa, ta gayawa mai napep din inda zai kaita, bayan tafiyar rabin awa suka iso, ta sauka daga napep din ta buɗe hand bag ta ciro 1k ta basa, ya bata canji da haka ta shiga gate din asibitin, can jikin wata bishiya ta tsaya ta ciro wayarta tayi dialing numbern Umma, Umma na picking Hajar tace "Umma kuna emergency room ko..?", Umma tayi jimm kafin tace "badai fitowa kikay ba Hajara..?", Hajar ta sunkuyar da kanta tace "fitowa nayi gani ma a asibitin..", Umma tayi ajiyar zuciya tace "toh kinga dai yanzu ni ina gida ban taho ba amma mal da Nasiru na nan..", Hajar tace "toh bari na shiga kafin kizo.." da haka ta katse wayar, wani worker ta tmbya ina Emergency room yayi leading dinta, gradually ta fara duba ko wane bed bayan shigarta E.R din, Naseer ta fara hangowa aikam ta nufi wajen, tana zuwa gaban gadon da Mu'azzam yake ta durƙusa har ƙasa ta gaida Baba, Baba ya amsa yana ƙare mata kallo, ta gaida Naseer ma, yace "lfy lou Hajar ykk, ygida..?", tace "lfy lou Yaya, ya aiki..?", yace "alhmdllh..", tashi tayi tana kallon Mu'azzam dake jingine da gado, shima kallonta yake, hankalinta ya mugun tashi ganin condition dinsa, ta dubi Naseer tace "Yaya hatsari yayi ne..?" don Umma bata gaya mata ainahin me ya faru ba kawai tace mata bashi da lfy suna asibiti, Naseer yace "ke karki ɗaga mna hankali..", ta ringa kallon Mu'azzam idonta ya ciko taf da ruwa tace "sannu Yaya". babu jimawa da zuwan Hajar saiga Umma tare da Sabra, da gudu Sabra taje ta rungume Hajar, Hajar tayi murmushi a takaice tace "ashe dai kina sona ƴar kanwata..", Baba ya tashi daga kan kujerar da yake ya ciro kuɗi daga aljihu ya bawa Umma yace "ko za a buƙaci wani abun", Umma ta karɓa tace "tom", yace "sai anjima..", Naseer ya tashi shima don tare zasu tafi da Baban yace "Umma saina dawo da daddare, zanje wajen police din ma akan case din, ya kamata a kama yaran nan...", Umma tace "toh Nasiru, Allah yayi albarka..", yace "Ameen" snn ya bar room din, Hajar tace "Umma hatsari yayi ne naji Yaya Naseer yace zaije police station...", Umma tace "ba hatsari yayi ba ƴan daba ne suka farr masa..", Hajar ta zaro ido tace "innalillah wa'inna ilayhirraji'un", sai kuma ta dubi Mu'azzam tana kallon inda aka sassaresa a jiki, Umma ta rausayar da kai ta buɗe ledar abinci da ta zo da ita, ta zuba masa abincin, da kanta ta ringa basa yana ci sbd karayar dake hannunsa. wajajen ƙarshe uku da rabi sai ga Anty Jamilah tare da Abdallah dake riƙe da basket, Anty suka gaisa da Umma ta mata ya me jiki, Abdallah ya russuna yace "Umma ina wuni, ya me jiki...?", Umma tace "alhmdllh, ya kasuwa..?", yace "alhmdllh..", Umma tace "madallah..", da mamaki Anty take kallon Hajar da ta gaisheta, Anty ta riƙe haɓa tace "ita kuma wnn har ta fara fita..?", Hajar ta sunkuyar da kanta ba tace komai ba, Umma tace "nima dai hka nagani, yanzu nke shirin ce mata ta tashi ta tafi ban kai ga gya mata ba sai gaku..", Anty tace "ai ya kamata dai ki tashi haka Hajar, ina ma laifi dan ma dai ɗan uwanki ne ba lfy..", wani tashin hankali ne ya baibaiye Hajar, ji take kamar ta kurma ihu tsabar baƙin ciki, itafa bazata koma gidan nan ba wlllh tllh, ko wace walle walle za ai ayita ta ƙare, da kyar ta iya cewa "ana yin sallar la'asar zan tafii..", Anty tace "ai la'sar din ta kusa..", tashin hankalin Hajar bai linku ba saida taji kiran sallah, Anty ta shimfiɗa dardumar da tazo da ita ta kabbara sallah, tana idarwa Umma ta miƙawa Hajar ƴar purse ɗinta tace "riƙe min nayi sallah". Hajar ta saka ƴar purse din a hijab, a hankali ta zuge zip dinta ta fara lalube, can ƙasan purse din ta jiyo keys, ta ciro keys din ta buɗe tata jakar ta saka a ciki, Umma na idar da Sallah tace "toh Hajara ayi harama..", Hajar tace "toh Umma bari nayi sallah..", tana idar da sallar tayi musu sallama ta fita, tana fita taji ance "Hajar..", ta juyo taga Anty ce, Anty ta ƙarasa har inda take tana mata kallon tsanake tace "Hajar Allah yasa dai baki ɗaga hankalinki a gidan ki ba.. idan da akwai matsala ki gaya min..", Hajar tayi rau rau da ido ta shanye kukan da yake shirin taho mata tace "A'a Anty babu wata matsala faa kawai dai nayi missing su Umma ne..", Anty tayi ajiyar zuciya tace "toh alhmdllh, toh ki kwantar da hankalinki kinji, karki sawa kanki damuwa ko wace mace a haka ta saba da gidan mijin, ai kowa yana son gidansu..", Hajar ta gyaɗa kai don huɗubar Anty bata shigeta ba bare tayi tasiri, abinda ta ƙulla shi zata warzar yanzu ma kuwa, tace "toh Anty ki gaida min da Hafsah" da haka sukay sallama, Hajar na fita bakin titi ta tsari napep tace "Dala zaka kaini..", mai napep ya gyaɗa kai ya gaya mata kudi, a bakin layin gidansu ta sauka bayan sun zo unguwar, a hankali ta shiga lungun ta wuce gida, da ido Maimuna da ta fito daga wanka ta bita tana taɓe baki, Hajar ko kallon inda take ba tayi ba ta wuce ƙofar ɗakin Umma ta ciro keys din da ta ɗauka ta buɗe padlock din ta shiga, rufe ƙofar tayi ta saka sakata, ta faɗa kan gado tana sauke ajiyar zuciya. Maimuna ta shiga ɗaki tana kallon Maama tace "ko me tazo yi oho..", Maama tace "wa knn..?", Maimuna tace "Hajara mna gata can ta buɗe ɗakin uwar ta shiga ta rufe..", Maama tace "ita Hajarar ce tazo gidan nan", Maimuna ta taɓe baki tace "ita fa", kwandon kayan shafa ta ɗakko ta zauna ta buɗe BSC cream ta lafta a fuska. saida aka kira sallar magrib Hajar ta fito tayi alwala ta sake komawa ɗakin ta rufe, ta haɗe kanta da guiwa bayan ta idar da sallar isha'i. wajen takwas da rabi Umma ta dawo, ta buɗe ƴar purse dinta zata ɗauki muƙulli, wayam taga babu alamar mukulli a jakar, ta kunna torch light din wayarta don babu nepa a gari tana haska alhargar ƙofar taga a buɗe, sai a lokacin ta lura da hasken dake ɗakin ta jikin window, jikin windown ta isa ta bankaɗa labule tana kallon cikin ɗakin tace "waye a nan", Hajar ta kalli window ta tashi ta buɗe ƙofar, Umma ta ringa kallonta don ta rasa ma me zatace mata, Sabra tace "laa Adda anan zaki kwana..?", Hajar dai na tsaye a inda take tamkar wacca aka dasa, Umma ta shiga ɗakin ta samu gefen gado ta zauna still idanunta na kan Hajar, Hajar ta sulale ƙasa daga nan inda take ta fashe da kuka tace "Umma... Umma.. bazan iya zaman auren nan ba wllh.."
★Nurain yayi folding din takardar da ya gama karantawa ya saka a pocket, ajiyar zuciya yayi yana kallon stairs kafin ya tafi ya haura, room dinta ya buɗe ya shiga to make sure, ya ƙarewa ɗakin kallo yaga dai babu alamarta anan, har bathroom ya buɗe ya duba, har zai fita daga ɗakin sai kuma ya dawo ya buɗe wardrobe, baiga alamar ta dauki kaya ba, fita yayi daga ɗakin ya sauka downstairs, ya shafa cikakkiyar sumarsa maganganun Abba na yawo a brain dinsa, compound ya fita thinking of what to do, ya sake shafa kansa kawai ya nufi ɗakin mai gadi, sallama ya masa, Inuwa ya fito ya russuna yace "Alhj", Nurain yace "kamar ƙarfe nawa ta fita daga gidan nan..", Inuwa yace "Hajiya..?", Nurain yace "Eh..", Inuwa yace "wajajen ƙarfe biyu..", Nurain ya gyaɗa kai yace "buɗe min gate..", Inuwa yace "tom" ya tafi ya fara buɗe gate din, Nurain ya nufi parking space, motarsa ya buɗe ya shiga, yafi minti biyar zaune a motar kafin ya kunnata, driving slowly ya fita daga compound din, yana hawa saman titi ya take accelerator, with speed yake driving, yana shiga unguwar ya rage gudun cause kwaltar a ragargaje take, gefen titi ya samu ya parker motar yana kallon lungun, unguwar duhu dunɗum sbd babu nepa sai fitilu na masu shagon chajin waya da provision, bai san wane bayanin zaiwa Abba ba hakan shine one Solution dinsa, buɗe motar yayi ya fito yana ƙarewa unguwar kallo, gently ya fara tafiya ya shiga lungun, tsaye yayi a ƙofar gidan, luckily for him yaga wani yaro zai wuce, kiran yaron yayi yace "shiga nan gidan kace Hajar tazo...", yaron yace "tom" ya shiga gidan da gudu, Umma na tsaye bakin ƙofar ɗakinta tare da Naseer da yake mgana ƙasa ƙasa kar Maama ta jiyosa, Umma tace "yanzu an kama yaran..?", Naseer yace "an kama mutum biyu saura uku, tinda an kama Ogan nasu suma za'a kamosu ɗaya bayan ɗaya..", Umma tace "dan Allah Nasiru a musu kwatankwacin abinda sukama yaron nan..", Naseer yace "ai sai sun ɗanɗana kuɗarsu Umma, na bawa ƴan sandar wani abu..", Umma ta gyaɗa kai tana jin wani sanyi a ranta tace "yauwa..", yace "bari na tafi asibitin..", Umma tace "toh da yake ma Abdallah na can tare dashi..", a daidai nan yaron ya shigo yace "wai Hajar tazo inji wani..", Naseer ya kalli Umma yace "daga asibitin nan tayo..?", Umma tayi ajiyar zuciya tace "Eh.." sai kuma tayi shiru ta rasa abin faɗa, Naseer yace "ai saita fito ko mijin tane yazo tafiya da ita.." sai kuma ya dubi yaron dake tsaye yace "kace gata nan..", yaron ya fita da gudu, har lokacin Nurain na tsaye bakin ƙofa ko soron bai shiga ba, tunani yake is he doing the right thing, ɗari biyar ya damƙa a hannun yaron yace "good boy", Naseer ne ya fito bayan ya yiwa Umma sallama, yana ganin Nurain a ƙofar gidan ya miƙa masa hannu sukay musabaha, kallon Nurain yake a tsanake yace "ko kaine kake kiran Hajar..?", Nurain yace "yeah..", Naseer yace "kai ne mijin nata..?", Nurain yace "yeah..", Naseer yace "kayi haƙuri fa na cika ka da tmbya, duba da yadda auren ya kasance shiyasa nake tamby tinda ban sanka ba, anyway ni yayanta ne..", Nurain yace "Okay nice to meet you..", Naseer ya sake miƙa masa hannu yace "same" sai kuma ya kalli cikin gida kafin ya koma ciki. Umma na kallon Hajar da take ta sharar hawaye tace "toh ni yanzu ya zan miki Hajara, na tmbayeki dalili kince min ba komai, komai fa saida dalili, haka kurum bazan tunkari mal nace akashe miki aure ba, yanzu idan kika gyamin dalili kinga na samu hujjar da zan goya miki baya a wajen mal, ba kiji farin cikin da mahaifinki yake ba da wnn auren, yace Allah ya zaɓa miki miji na gari, juma'ar da ta wuce mijin naki da mahaifinsa suka zo har nan yaron ya gaida mal, nutsuwa da hankali ai suna bayyana kansu, mal yace shi dai baiga aibun wanda ya aura miki ba, kema yanxu na tambayeki kin ƙi bani amsa, kin san dai mahaifinki ba lfy ya cika ba idan kina so ciwonsa ya tashi ta dalilinki toh maza ki ɗau harama Hajara..", Hajar ta cigaba da sharar hawaye nan ma ba tace komai ba, Umma tace "A zamanin da haka ake auren, toh kema mahaifinki ya miki zaɓi amma kina ƙoƙarin bijire masa, idan kina samun wata matsalar ne a gidan naki ki faɗa in yaso sai iyaye su shiga idan zaman naku bazai yiwu ba sai a raba, akwai matsala ne..?", Hajar ta girgiza kai, Umma tayi ajiyar zuciya tace "toh shknn, zan turo Jamilah kuyi magana da ita, mal din ma zan masa mgana, kinga ynxu hankalinsa ba a kwance yake ba, tashi ki tafi kar ya dawo ya sameki a gidan nan .." Naseer da ya shigo gidan ya tsaya bakin window yace "ke Hajar kin bar mutum a tsaye fa..", Umma tace "gata nan". saida Hajar ta share minti uku wajen saka hijab da ɗaukar jaka, kamar wata chameleon haka take acting, murtuke fuska tayi ta fita soro, tin kafin ma ta kai bakin ƙofa hancinta ya shaƙi scent dinsa, yana ganinta yaji wani relief cause he can't imagine abinda Abba zai masa, ba tare da ta dubesa ba tace "takardar ka kawo..?", yace "yeah ita na kawo miki..", wani sanyi taji har cikin ranta, ta juya ta zuba masa lulu eyes dinta ta miƙa hannu tace "kawo..", duk da duhun dare saida ya lura da hasken hannun nata da taimako hasken farin wata, yace "ohk, ai takardar na mota idan kina so kizo ki amsa", yana gama faɗin haka ya juya ya fara tafiya, tabi bayansa da harara sai kuma ta bisa walking slowly, yana fita bakin titi ya tsaya kusa da motar yana jira ta ƙaraso, tana