Showing 243001 words to 246000 words out of 252835 words
sai kuma ta ɓangala dariya har saida rabbit tooth da both dimples dinta suka fito, Hajar ta fara mata wasa ita kuma ta ringa kyalkyala dariya har da ƙoƙarin shiɗewa, Nurain ya kallesu ya shafa kan Nanerh yace "Princess", shima ta basa nasa kason na dariya sai kuma ta fara miƙa masa hannu wai ya ɗauketa, da taga yaƙi ɗaukarta sai ta fara mimmiƙewa za tayi kuka, Hajar ta ɓalle belt din Carrier ta juyar da Nanerh ta kalli window, hakan yasa ta haƙura da zuwa wajen Abban nata da yake driving ta ringa kallon motoci, Nurain yace "Wifey mene burinki a karatu?", da sauri Hajar ta kallesa don bata taɓa tunanin zai mata mganar cigaba da karatu a yacca yke da mugun kishin nan ba, ya kalleta yace "Uhmmm kinyi shiru baby wife", Nanerh ta fara gantsarewa ta ringa ƙoƙarin juyowa don taji muryan Abbanta, Hajar ta hanata juyowar ai kam ta saka kuka, saida Nurain ya dauketa snn suka samu salama, ɗaukarta da yayi bai hanasa cigaba da tuƙi ba tunda bata takura masa ba, tinda ya ɗauketa daru ya ƙare, sai a snn ya samu chance din cigaba da tmbyar Hajar akan karatunta, tace "dana gama secondary school Nursing school ita nake da burin zuwa, sai dai kuma ban samu na shiga ba..", yace "Nurse kike son zama baby wife...?", ta gyaɗa kai tace "shine babban burina a karatu", yace "Okay... kin taɓa applying ne...?", ta gyaɗa kai, yace "Ohk i see, in dai school of Nursing ta kano state ce nasan ba tada kyau, siyasa kawai suka saka a gaba, basa bada Admission sai kanada hanya idan yarinyar ka ma ta shiga schl din akwai wni exams da suke yi su zubar da yara, ita exams din ba qualifications din yaro suke dubawa ba cause siyanta ake da kuɗi ko kuma hanyar ƴan siyasa..", Hajar ta zuba masa manyan idanunta, yace "I heard that from integrate person wnda ko ban gani ba amma na yarda, So you will not go to that bushy school a bar musu kwalinsu, i will find the best Nursing school for you insha Allah", wni sanyi ne ya ratsa zuciyar Hajar, wai itace zata koma schl abinda bata taɓa kawowa ba, Nurain ya kira Sakeena ta sake tuna masa sunan hospital da Address, gab da magrib suka isa hospital din, bayan Nurain yayi parking ya kalli Nanerh yace "weldon Princess kinga kin sa mun daɗe a kwalta", dariya ta ɓangala masa, ya kashe motar snn ya zare key daga ignition, da zafin nama Nanerh ta kaiwa key din cafka, gamm ta riƙe key din da ƙarfinta taƙi saki, ya bar mata a hannunta ya buɗe motar ya sauka, Hajar ta fito ta ciro basket daga booth suka shiga cikin asibitin, Mami da Sakeena sai Aunties din Abdul mijin Noor biyu suka tarar, Hajar ta ajiye basket din hannunta ta gaida kowa da ladabi, Nurain ya miƙawa Mami Nanerh ya amshi cute baby boy din Noor dake hannun Sakeena, after 3mins ya mayarwa da Sakeena babyn yace zai fita sallah ne tinda magrib yayi, Mami tace "Wnn ba key din motarka bane hannun takwarata..?", yace "Eh shine", Mami tace "Ohk toh amshi abinka kar ta cilla wni gurin da za ayi ta nema", yace "Toh" ya ƙaraso zai amshi key din, ai kam tini Nanerh ta gantsare zata saka kuka, sakar mata yayi ta cigaba da wasanta yace "Ai kuka za tayi ne fa", Mami tace "Au kuka za tayi, shknn idan ta wurgar ai ka yanko wni", ya juya ya fita yana shafa kansa, wato ya yarda ya yanko wni ɗin da Princess dinsa tayi kuka, Hajar dai ta amshi baby ta koma gefen gadon da Noor ke kwance tana bacci ta zauna, tinda ta haihu take bacci don long labor tayi, almost 48hrs tana labor, sai bayan sallar isha'i snn Noor ta farka, Mami tasa Hajar ta haɗa mata shayi mai kauri, Hajar ta miƙawa Noor mug din shayin tace "Sannu", Noor ta numfasa ta amshi mug din, Hajar ta zauna gefenta tace "ynxu kin gane gidan glass din da nake gaya miki..?", Noor ta sauke wni ajiyar zuciya tace "gidan glass ɗaya ma knn, ke nifa nan da kika ganni na buga final insha Allah", Hajar ta guntse dariyar da ta taho mata tace "A haba dai nan da 1yr ki silliɓo wta please", Noor tace "tsakani ga Allah tawa ba irin taku bace Hajar, na samu tear fa sosai", Hajar tace "Ayya sorry, ai kwalliya ta biya kuɗin sabulu your baby is so cute..", Noor tayi murmushi, Sakeena ta kallesu tace "wai ƙus ƙus din me kuke ku ka wni haɗa kai..?", Noor tace "ba komai", Sakeena tace "Toh maza ki shanye tea din". 2weeks Later Hajar na zaune palourn downstairs tare da Sabrah wcca ta ɗakkota shekaran jiya, Sabrah sai wasa take yiwa Nanerh da toys dinta da take zaune baja baja a cikinsu, kayan wasa gareta masu yawo sai kace abinci, a cikin kayan wasan harda horse toy da Ashraaf ya bata, shine ma a hannunta tanata gasa masa cixo da rabbit tooth dinta, Sabrah tace "Addah na ga Yaya Maimuna akan titi tana bara a cikin almajirai", Hajar ta dakata da latsa wayar da take tace "wace Maimunar..?", Sabrah tace "Maimunan Maama ta tsohon gidanmu", Hajar ta tsuke ido tace "Maimunan kika gani tana bara..?", Sabrah ta gyaɗa kai tace "Eh idan zanje schl nke ganinta akan titi", Hajar was very shocked amma kuma bata gamsu ba, Maimunan ce zata fito kan titi tana bara, a haba dai wnn ai impossible ne, Hajar tace "kawo min kayan abincin Nanerh naga kamar cikin yayi ƙasa", Sabrah tace "Toh", gwangwanin cereal food din Nanerh da Vacuum flask Sabrah ta kawo mata, tini Hajar ta damawa babynta cereal food dinta a ƙaramin silicone bowl dinta, Hajar ta ɗauki Nanerh ta fara bata abincin, ana yi ana wasa, don idan ba a wasan nan saita ƙi ci next action kuma kuka ne, bell din door aka danna, Hajar tace "Open the door Sabrah", Sabrah ta tashi da sauri ta buɗe ƙofa, Hajar ta buɗa baki ganin wcca ta shigo, Khausar ta ƙarasa shigowa ciki tare da friends dinta biyu, Hajar ta tarbesu, bayan sun zauna suka gaisa a mutunce, Khausar ta ɗauki Nanerh tana mata wasa, Hajar ta saka Sabrah ta kawo musu ruwa da lemo, Khausar tace "Ohh Hajar ynxu fa zamu wuce", Hajar tace "daga zuwa... ai kwa bari ku huta", Khausar tace "driver na jiranmu ai, daman IV card na kawo mki har gida", ɗaya daga cikin friends din Khausar ta ciro cards daga handbag ta miƙawa Hajar tace "ba ki gane ni ba ko..?", Hajar ta tsuke idonta tana so ta tuna inda ta taɓa ganinta, friend din Khausar tace "Banafsha ce", Hajar ta buɗa baki tace "Na gane... ykk Banafsha..?", Banafsha tace "fine Alhmdllh", su Khausar basu wni jima ba suka yiwa Hajar sallama suka tafi, sai bayan tafiyarsu Hajar ta duba cards din, nan da kwana shida ne bikin, ashe har lokaci ya taho, ranar sunan babyn Noor taji ana mganar bikin Khausar din amma bata yi tunanin yaxo kusa ba, komai mai wucewa ne indai kabi duniya da sauqi wai yau Khausar ce ta tako har gidanta ta kawo mata katin bikinta, baya ga haka ynxu sun ƙulla da Khausar suna zuba friendship dinsu sai kace tin da sun san juna. Daga hka aka shiga bikin Khausar da Farooq, sosai bikin ya zama na musamman don ya haɗa both side, ga ɓangaren Mami ga kuma ɓangaren Abba, bikin Farooq da Khausar yayi armashi ba ƙarya, gashi zumunci ya sake ƙulluwa, daman Mami da Ummin Farooq zaman lfy suke ba wni mganar facalanci shiyasa lokacin da Farooq ya jewa da Umminsa da mganar Khausar kai tsaye tace ta amince, kuma daman tasan wace ce Anty Zulaihah ƙanwar Mami, A ɓangaren Farooq Ango sam bai ɗagawa babban amini ɗan uwansa kuma abokinsa ƙafa ba akan sabgar biki, duk irin noƙewar da Nurain ya ringa yi hka Farooq ya ringa jajiɓosa suna shiga sabga, ɓangaren Hajar da Nurain kam drama aka ringa bugawa a wajen events, shi Nurain ya shige cikin Abokan ango wnda duk ƴan uwa ne, ita kuma hakimar tasa tana daga cikin friends din Amarya, duk inda Hajar tayi Nurain na ankare da ita wai kar wni yayi mata mgana, ita kam shigarta ma was more than decent don ba irin na bride mates bane. Hajjaju Hajiya ma ta baza capacity dinta daidai gwargwado, tace bikin Angonta ake don haka dole ta raƙashe, nan fa jikokinta suka yoh mata caaa da tsokana wai batada kishi za a mata kishiya tana murna, Hajiya kam tace ba komai ai wadata ce tasa yayo mata kishiyar, da za a tafi dauko Amarya Hajiya ce a gaba, daman tace indai tana raye kuma da lfyrta toh duk wata jikarta mace ita zata kaita ɗakin miji, haka zalika idan namiji ne itace zata ɗauko masa matar ta kai masa gidansa, ai kam a hannun Hajiya aka damƙa Khausar, Hajiya ta riƙo hannunta gam zuwa mota tana cewa "Allah yasa ki zama kamar matar Usuman, yarinya ƴar albarka irin albarka, ba sakawa bare aje ga fitarwa, nutsuwa hankali ga kawaici duk ta haɗa, ga uwa uba tarbiyya, Allah yasa kema irinta ce". Hajar dai ana shirin tafiya gidan Amarya ita kuma ta wuce gidanta don a zahirin gsky ta gaji snn kuma ga rigimar da Nanerh take mata itama ta gaji, Sabrah ma har ta gaji da rainon, wajen ƙarfe takwas na dare Hajar tayi wnka, ta lallaɓa Nanerh har tayi bacci, gashi dai bacci take ji amma ta kasa sbd mijinta bai dawo ba, a zabure ta miƙe zaune a kan gadonta ta janyo wayarta ta shiga kiransa, missed call biyu tai masa no response, habawa ai tini ta diro daga gadon ta hau shawagi ta cigaba da doka masa kira, sai a kira na huɗu ya ɗaga, tace "Moon", ƙasa ƙasa taji muryarsa yace "Wifey", daga nan bata sake jin muryarsa ba amma kuma taji alamar kamar driving yake, katse kiran tayi ta sake kiransa, an ɗaga amma kuma sai taji muryar mace, ji tayi tamkar an kwaɗa mata guduma a ka don har wani baƙi ne ya gilma mata.......✍️
💛 HAJAR 💛
{97..}
Sauke wayar Hajar tayi daga kunnenta ta wurgarta kan gado ba tare da tayi ending call din ba, wata irin tafasa zuciyarta ta ringa yi har jiri na neman ɗibanta, ta ja ƙafa ta hau kan gado ta kwanta ta cusa fuskarta a pillow, tunanin zuƙa zuƙan friends din Khausar da suke shige da fice a bikin ta ringa yi, bayan friends dinta ga cousins dinta na ɓangaren uba suma masu yawa kuma kyawawa, Hajar ta suntuma tayi famm saura ƙiris ta fashe, idonta ya soye don duk uban baccin da take ji ya gudu, duk bayan 10 to 15 mins saita ɗaga kai ta kalli agogo, har ƙarfe goma ya wuce Nurain bai dawo ba, ita abinda yafi ƙona mata rai shine da bai sake kiranta ba, tashi tayi ta fita palournta na upstairs, ta kalli Sabrah wacca ta barta tana kallo amma kuma tayi bacci ynxu, daman ita da Nanerh ne suke kwana a bedroom din Hajar ita kuma Hajar ta kwana a turakar mijinta, a yau ba ta jin zata kwana a turakar tasa don wnn fitowar da tayi sbd ta rufe ƙofa ne, tana cikin wnn tunanin aka buɗe ƙofa Nurain ya shigo, ɗaga kai tayi ta kallesa nan ta sake jin wni raɗaɗi a zuciyarta, abinda yasa taji raɗaɗin shine kyan da yayi, lokaci guda pure and breath taking scent dinsa ya cika ɗakin, ya mayar da ƙofa ya kulle yana kallonta yace "Baby wife", ba ta ko kallesa ba ta ƙarasa gaban center table ta ɗauki remote ta kashe kayan kallo, kawai gani tayi har ya matso kusa da ita, da sauri taja da baya ta zille masa, ta juya da gudu ta shiga bedroom dinta, lokaci guda hawaye ya ciko idanunta, ai tini Nurain yabi bayanta, kwance ya sameta kan gado ta rufe da duvet har kai, ya sauke ajiyar zuciya ya ƙarasa gaban gadon ya zauna gefenta, Calmly yace "Baby girl.." sai kuma ya kai hannu ya kwashe duvet din, ta sake janyowa ta rufe kanta, saida sukay haka sau uku, yace "Me nayi kuma Baby wife...?", a ɗan fusace ta miƙe ta zuro ƙafafuwanta ta sauka daga gadon, ganin ta nufi hanyar closet yayi sauri ya tashi ya riƙota don yasan next action din nata, bathroom zata shige kuma duk bala'i ba zata buɗe ba, ƙoƙarin fixge kanta ta ringa yi, ita so take ta gudu taje tayi kukan da take dannewa, ganin yacca ta haƙiƙance ya juyo da ita ya rumgumeta tsam a jikinsa, hakan yasa ta gagara motsi, with cracking voice tace "please let go off me", yace "I will not", fashewa tayi da kuka tace "Ni ka kyaleni ka tafi can wajen sabuwar girlfriend din da kayi", ya waro ido yace "wollah bbu wata girlfriend da nayi Baby wife..", ta fara jan shessheƙa tace "Ai naji muryarta kuma har dasu bata waya tamin mgana", yace "No ba haka bane Baby", turasa tayi ita a dole sai ya saketa, ya kai lips dinsa saitin kunnenta yace "don't cry and listen to me..", yana rumgume da ita ya fara tafiya zuwa gefen gado, ya zaunar da ita snn ya duƙa gabanta gami da riƙo hannayenta cikin nasa, ta saukar da kanta ta wani sha kunu, shiru ne ya ratsa room din, shi kam kawai kallonta yake yana auna salon nata kishin, ta ɗago sukay ido huɗu, ta haɗe gira tace "Toh idan ba girlfriend kayi ba wce ta ɗauki wayar..?", ya sauke numfashi yace "Sumayyah ce fa", ta zuba masa ido tabbas sai ynxu ta ɗan gane muryar Sumayyah taji, ya murza hannunta dake cikin nasa yace "muna tare da Iron Lady xan kaita gida ne kika kira baby wife, Hajiya ta hanani yin wayar wai baxan kifar da ita a mota ba, tace wai ina driving ina waya ai baxai yiwu ba, shine na bawa Sumayyah wayar nace ta miki mgana tinda har da ita zan kai gida tare da Iron Lady...", Hajar tayi ajiyar zuciya a bit relief, yace "ina kaisu gidan zan kiraki Charge dina ya ƙare" da haka ya ciro wayarsa ya nuna mata taga tabbas ta mutu bbu Charge, ta juya lulu eyes dinta gami da turo baki tace "Amma baka dawo da wuri ba", yace "Punk... ya hanani sakat saida muka rakasa gidansa snn na samu na gudo", tayi shiru ba tace komai ba tana jin duk raɗaɗin zuciyarta yana zagwanyewa, yace "Daman nace Princess a wajenki ta koyi rigima...", tace "Ai ni nawa da dalili", ya waro ido yace "Ina dalilin anan, har an kusa bani though punishment daga an kira waya anji muryar mace", ta ɗan hararesa, murmushi mai sauti yayi ya janyota yayi kissing idanunta da suka kumbura yace "My ƴar rigima". Washe gari ƙarfe takwas Hajar ta sauka downstairs da Nanerh a hannunta, kawai ƙamshin turaren wuta da freshener ne yake tashi don masu aikinta har sun gama aikinsu, sosai take jin daɗin zama dasu sbd suna jin mgana snn ga tsafta, idan ta gaya musu abu sau ɗaya shknn, saida ta bawa Nanerh abinci ta sakata a kekenta snn ta shiga kitchen ta hau shirya musu nasu abincin, Sabrah ce ta shigo kitchen din, Hajar tace "kin gama shiryawar?", Sabrah ta gyaɗa kai tace "Eh... Addah me zan kama miki..?", Hajar ta bata cabbage tace "ki yanka sa ƙanana", Sabrah ta amshi cabbage din tace "Toh", Hajar tace "kiyi a hankali karki yanke", Hajar ta buɗe fridge ta ciro marinated chicken ta fara mata yankan tsayi tace "Sabrah ranar nan kina gayamin kinga Maimuna tana bara, kin tabbata ita kika gani..?", Sabrah tayi shiru tana tunani, Hajar tace "ba ita bace ko..?", Sabrah tace "Ni wcca nake gani har fuskarta baƙa ce, ita kuma Maimunan Maama fuskarta fara ce ƙafarta da hannunta baƙaƙe", Hajar ta girgiza kai, wnn bai isa ya zama hujja ba don Maimuna bleaching take ta iya yiwuwa ita Sabrah ta gani, Sabrah tace "kuma har ciwon da Maimuna take dashi a goshi na gani", Hajar ta numfasa ta kawar da zancen, kawai dai sai taji ta kasa samun sukuni ne, bata son ahalin Babanta a irin wnn rayuwar, she wish sauran ƴan uwanta su nutsu su koma kamar Nabilah.
★Da kyar Maimuna take jan ƙafarta da ta mata mugun nauyi sbd cikin jikinta da ya girma, tayi wani mugun baƙi sai kace wacca ta shafa gawayi, wata fatattakakkiyar roba sai kace ta kwasar kashi ce a hannunta, tayi wata iriyar rama sai kace wcca ta shekara goma tana jinya, gida ta shiga wanda a ynxu ya sake ruɓewa, tana shiga soro ta tsaya ta janyo duƙunƙunannen hijab dinta da ya koɗe ta goge hawayen da suke sauko mata, wucewar da za tayi wajen shagon Iliya mai awo aka samu wni mutum ya gwaɓa mata mgana, da haka ta shiga gida tana jan ƙafa, sororo tayi tana kallon Maama dake sanye cikn wasu ruɓaɓɓen kaya duk sun zama tsumma, Maimuna tace "Maama..", Maama ta ɗago ta kalli Maimuna sai kuma ta saukar da kanta, Maimuna tace "Na shiga uku... Maama mai ya faru dake", Maama tace "ciwon Sa'adatu ne ya tashi tayi min duka", Maimuna ta ƙarasa ciki tace "Tana ina..?", Maama tasa haɓar zani ta toshe hancinta da ke yoyon jini tace "da kyar na samu na rufeta a ɗaki", Maimuna ta ajiye mushiyar robar dake hannunta ta matsa gaban windown ɗakin da Maama ta rufe Sa'adatu, malelekuwa kawai Sa'adatu take a ƙasar ɗakin da ko leda babu, gurnani take sai kace mage lokaci guda kuma saita kurma wni uban ihu, Maama ta leƙa robar da Maimuna ta ajiye sai kuma tace "yau baki samo komai a wajen maular ba..?", Maimuna tace "Na samo naira talatin", Maama ta fara matsar kwalla tace "yau ko na kwakin bamu samu ba knn... innalillah wa'inna ilayhirraji'un", rabonsu da abinci tin shekaran jiya kuma shima