Showing 36001 words to 39000 words out of 162658 words

Chapter 13 - BA NI DA GATA COMPLETE HAUSA NOVEL

29 Jan 2025

42946

re da fad'in,
"Alhamdulillah you're home sister. I'm so sorry for allowing you to follow him, I won't do that again. Please pardon me sister. But did he hurt you?". Fanan ta k'arisa ta na dudduba jikin ta domin ta ga ko akwai in da Suhail d'in ya ji mata ciwo da dukan. Sam ta manta ma idan za ta shekara ta na turanci Bintyn ba za ta San abunda ta ke ce wa ba.
"Dalla matsa ko in bige ki a nan wajan. Da ma ke ki ka ce mata ta je wajan shi ko?". Fad'in Barrister Fu'ad ya na hararar Fanan d'in.
"Ohhh brother lemme explain". Fad'in Fanan a marairaice.
"Heey! Not a word. I don't need your explanation. Talkative". Fad'in Barrister ta re da matsar da Fanan ya ruk'o hannun Binty su kai part d'in Anna (Hajiya Na'ima).
"Ohhh please bro, won't you hold my too?". Fanan ta sha gaban su ta re da mik'a hannunta.
Girgiza kai Barrister ya yi ta re da rik'e hannunta ita ma.
A parlourn k'asa su ka taras da Annah sai sama da marwa ta ke yi. Ka na ganin ta kasan hank'alinta a tashe ya ke.
"Anna she's back. Bro Fu'ad brought her back. Look at her here".
Da sauri Anna ta juyo ta re da sauke idanuwan ta a kan Binty. Wani sanyayyar ajiyar zuciya ta sauke ta re da k'arisawa in da su ke ta rungume Bintyn.
"Wannan beauty d'in fa za ta kwace miki autahood d'in ki". Barrister Fu'ad ya fad'awa Fanan a kunne at the same time kuma ya na mata dariya da gwalo.
"Brooooo". Fanan cike da shagwab'a.
Zaro mata idanuwa ya yi ta re da karyar da wuyarsa ka na ya ce,
"Yessss. How may I help you?".
Turo ba ki ta yi ta re da ita wajan su Anna da ke rungume da Binty ta ce,
"Anna me too". Ta fad'i hakanne ta re da ware hannunta cike da shagwab'a.
Murmushi Anna ta yi ta re da had'a su duka ta rungume su ta na kissing forehead d'in su.
Mai da du ban ta ta yi ga Barrister ta yi ta re da fad'in,
"Fu'ad, I hope he didn't do anything to this little girl? Cus wallahi this time I can't hold it".
Ajiyar zuciya Barrister ya sauke ta re da fad'in,
"He's about to, sai Allah ya kawo ni da sauri. Maganar gaskiya Anna ki bar ni in d'au mataki a kan wannan d'an iskan yaro da ya ke nai ma ya lalata mana sunan gida kuma uwar sa na sane ba za ta iya d'aukan mataki ba. Wallahi jiya sai da wani abokin aiki na ya min magana akan in rik'a kula da shi saboda last 3 days gasa su kai a kan kwayar doki, kuma shi ya ci gasar. Yaro duk ya bi ya lalata kan shi, k'arami da shi. Ko nineteen years fa bai yi ba. He's just eighteen. Haba Anna, dan Allah ki bar ni na d'au mataki. Ki na ganin da ya Julaibib ya na nan zai kyale shi ya yi duk abunda ya ga da ma ne. Wallahi duk ranar da yaya zai sauke k'asar nan ya ji labarin abunda Suhail ya ke yi, to wallahi sai ya karya shi. Ke Anna ai kin fi kowa sanin halin sa. Dan Allah ki bar ni in gyarawa yaran nan zama tun kamin yaya ya dawo ni ma ya had'a da ni. Don cewa zai yi ina kallo ya lalace".
"Enough barrister! You can go back to your work. Ku ba ku san abunda na sa ni ba. Duk abunda na ke yi ina da dalili na. Suhail d'an uwan ku ne, ni kuma d'an mijina ne da na ke ma sa kallon d'an ciki na kamar kai da ka ke ga ba na. So just do as I say".
"As you wish Anna". Fad'in Barrister in a cool way. Cus har ga Allah ya na son d'auka mataki kwakkwara akan d'an uwan na sa. Domin idan ya lalace kamar shi ne ko Zaid k'anin sa ne ya lalace.
"Anna I'm going". Barrister Fu'ad ya sa ke fad'i ya na kallon Binty da ita ma shi ta ke kallo. Kuma Sam ta ka sa fahimtar mai su ke cewa kasancewar su na had'a turanci a cikin maganganun su.
"OK". Anna ta fad'a a tak'aice ta re da rik'e hannun Fanan da Binty su ka nufi stairs.
"Anna, why not malamin ya rik'a shigowa har parlourn nan k'asa ya na masu karatun? Cus zaman su a waje is not safe for the little girl".
Ba ta re da Anna ta juyo ba ta ce,
"Zan masa magana, ni ma hakan na tsara". Ta fad'i hakane su na hayewa steps d'in.
Ajiyar zuciya Barrister Fu'ad ya sa ki, ya na son tambayar Anna wacece Binty, amma yadda ya ga Anna ta yi kicin-kicin da fuska sai ya had'iye tambayar sa ya fi ce don ka da ya yi latti.
Shiga mota ya yi ta re da reverse ya fi ce. Ya kai gate d'in k'arshe wato gate d'in su Oga Solomon ya sauke glass ta re da yafito Solomon d'in da ke rik'e da gate d'in da ya bud'e masa. Da sauri Oga Solomon ya isa wajan motar tare da sarawa Barrister.
"I need to talk to you, but leter in the night when I come back". Fad'in Barrister Fu'ad.
"OK sir". Oga Solomon ya fad'a ta re da k'ara sarawa Barrister Fu'ad.
Mai da glass d'in sama ya yi ta re da ficewa daga gidan. Shi kuma Solomon ya rufe gate d'in ta re da dawowa wajan zaman shi ya soma wak'an yaran su.


.........."Kar ko da wasa wanda ya fita da ke yau ya sa ke kiran ki, ki bishi. Kin ji abunda na ce miki?". Anna ta fad'a ta re da rik'e kunnanta d'aya.
"Eh Anna na ji. Yaya Fu'ad ma ya ce min haka. Wai idan na saki wani namiji ya tab'a ni, zan mutu. Ya ce ka na yi wasa da maza idan ba haka ba zan mutu".
"Abunda ya fad'a gaskiya ne. Ba ke kad'ai ba, dukkan ku har da ke Fanan". Fad'in Anna ta re da mai da dubanta ga Fanan d'in da ke kwalalo idanuwa.
"Now go and perform ablution and pray. And don't forget to teach her how to pray". Fad'in Anna saboda kiran sallar la'asar d'in da ake yi.
Fanan ce ta soma mik'ewa saboda Binty ba ta san mai Anna ta ce ba kasancewar da turanci tai maganar.
Hannun Binty ta rik'e ta re da fad'in,
"Mu je mu yi sallah sis".
"A'a ni bazan yi ba, ke ki je ki yi. Ni na gaji yau bazan yi ba sai gobe da safe. Dama ni sau d'aya kawai na ke yi. Shi ma Hadaan ne ya ce na rik'a yi idan ba haka ba Allah zai saka ni a wuta".
Fad'in Binty ta re da zame Hannunta ta kwanta a kan carpet.
Zaro idanuwa Anna ta yi ta re da fad'in,
"Binty ai duk wanda bai sallah wuta zai shiga. Banbancin mu da arna kenan ai. Dole ne ki yi duka salloli guda biyar a kowace rana".
"Anna menene arna? su waye arna? Su ma mutane ne?".
Kallonta Anna ta yi cike da tausayi da kuma mamakin daga wani k'auye ta fito da ba su san addini ba haka.
"Binty ina ne k'auyan ku?". Fad'in Anna ta na kallon ta.
Shuru Binty ta yi ta na tunanin sunan da Kandala ta fad'a mata idan an tambaye ta garin su. Can ta ce,
"Can k'auyan Saminaka". Fad'in Binty ci ke da jin dad'in tuno sunan da ta yi.
Jinjina kai Annah ta yi ta re da fad'in,
"Binty Arna su ne wad'anda ba su bin duk abunda Allah ya ce ayi. Ba sa sallah, Ku ma ba su yadda da fiyayyan halitta Annabi Muhammad SAW ba, sanna ba su yadda Annabi Isa ba Allah ba ne". Fad'in Anna.
"Annah wanene Annabi Muhammad, kuma wanene Annabi Isah?" Fad'in Binty ita ma ta na kallon Anna.
"Ohhh may God! Binty ba ki san su ba? Amma dai ba kya zuwa islamiya ko? Ai duk musulmi ya san tarihin su. Kuma yasan su Annabawa ne da Allah ya aikowa mutane".
"Quiet please". Anna ta fad'a ta re da kallon Fanan d'in.
"Annabi Muhammad SWA shine manzo na k'arshe da Allah ya turo. Allah ya turo shi ne domin ya wa'azantar da al'ummar sa domin su bi hanya na gaskiya. Haka shi ma Annabi Isa".
"Menene wa'azi Anna? Kuma su waye su ke bin hanyar dai-dai, kuma suwa su ke bin wanda ba dai-dai ba?". Binty ta sake fad'i.
Ajiyar zuciya Anna ta sauke ta re fad'in,
"Binty ku je ku yi sallah, a hankali za ki ga ne komai idan har za ki nutsu wajan malam. Zai koya miki komai. Kuma ki masa duk tambayar da ki ke son yi kin ji? Kuma ka da ki sake cewa ba za ki sallah ba. Sallah wajibi ne akan kowani musulmi".
"To Anna. Daga yau kullum zan rik'a sallah".
"Good girl. Allah ya mu ku albarka. Ku je ku yi sallah". Fad'in Anna.
Mik'ewa Binty ta yi, Fanan ta ka ma hannunta su ka wuce d'akin Fanan d'in don gabatar da alwala da kuma sallah.

Sosai hankalin Anna ya ta shi da irin jahilcin da Binty da kuma jama'ar k'auyan su ke fama da shi. Yanzu kenan duk kallan da su ke wa Kandala ita d'in jahila ce.
"Wannan yarinya Sam ba da aikatau ta da ce ba, da makaranta ta da ce. Ga kyau iya kyau amma kwakwalwa cushe ya ke da kashin kafinta. Dole na yi tsaye a kan yarinyar nan ta yi makaranta kamar yadda zan yi a kan Fanna. Wannan yarinya na zama uwarta da ubanta. Babu wanda ya isa ya karb'e ta a hannu na. Zan tsaya iya tsayin daka naga ta samu ingattaccan ilimi da izinin Allah. Ta yadda za ta ceto k'auyan su daga halakar da su ke ciki. Ya Allah ka taimaka min a kan haka". Fad'in Anna ta re da d'aga hannu sama ta na rok'an Allah.


*8:15pm*
Wasu had'ad'd'un motoci guda tara ne su ka danno cikin layin. Hu'du a gaba, hu'du a baya. Sai guda d'aya a tsakiya wanda Alhaji Usman Mai rabo ya ke ciki ya na duba sak'on email a wayarsa.
Horn su ka danna. Oga Solomon da ke magana k'asa-k'asa da Baban Haruna ya zabura ya mik'e ta re da fad'in,
"Baban Haruna, Alhaji is back". Ya fad'i hakane ta re da sauri isa ya wangale gate d'in. Takwas d'in farkon nan su ka shiga ciki ka na motar da Alhaji Usman ke ciki ya danno kai.
Tsayawa driver ya yi, domin ya san Alhaji a nan ya ke sauka domin ya duba ma'aikatan sa. Duk nisan da ke tsakanin gate d'in farko da kuma ainahin cikin gida, haka ya ke tafiya a k'afa don kaf sai ya ji lafiyar ma'aika da kuma idan su na buk'atar wani abun ka min ya k'arasa wajan iyalansa.
Aje tsaleliyar wayarsa ya yi a kan briefcase d'in sa. D'aya daga cikin bodyguard d'in sa ya fito da sauri ya bud'e masa murfin mota.
Kyakkyawan k'afarsa ya fara fito da shi, ka na ya fito da gangan jikinsa. Saboda yadda gaba d'aya gidan ta ko'ina akwai globes farare, dai gidan yai haske kamar ba dare ba. Ko babu wutan nepa su na da k'aton jen *MIKANO* standby a gidan. Babu yadda za'ayi kazo gidan ka ga ba wuta.
Gaba d'aya ma'aikata da su ke wajan su ka k'araso su na kwasar gaisuwa.
Shi kuwa dattijo cike da fara'a da kamala ya ke amsa masu kamar ba ma'aikatan sa ba. Babu wani d'auke kai ko nuna isa irin na ubangida da bawan sa.
"Baban Haruna, Soloman, D'an kwairo, Tanimu, ina fatan dai babu wata matsala ko?". Fad'in Alhaji Usman fuskan shi fad'ad'e da fara'a.
"Yallab'ai babu matsalar komai wallahi". Gaba d'ayansu su ka amsa".
Cike da farin ciki Alhaji Usman ya jinjina kai. Kallon Solomon ya yi, duk da yasan ya na jin wani hausan, sai dai mayarwan ne ke masa wuya. Don fita hak'k'i sai ya ce,
"Is there any problem Solomon? If there's, fell free to say it".
"No, no sir. There's no problem sir". Fad'in Solomon ya na girgiza kan sa.
"OK. But have you eaten?". Alhaji Usman ya sa ke tambayan sa.
"Yes sir. We are full".
Jinjina kai ya sake yi ta re da mai da duban sa izuwa ga su Baban Haruna ya ce,
"Ina fatan duk kun yi sallah, kuma kun ci abincin".
"Eh yallab'ai. Mun yi sallah kuma mun ci abincin". Fad'in su Baban Haruna.
"Alhamdulillah! Ba ri na k'arisa ciki". Fad'in Alhaji Usman ta re da yin gaba don duba sauran ma'aikata. Dama tuni motocin da su ka kawo shi sun yi ciki don sun riga da sun san da k'afa zai k'ariso. Sai ya duba ma'aikata sa kaf ya tabbatar da lafiyan su ya ke shiga ya ci abinci ya yi bacci.
Yauwa sai da ya kwashi kimanin mintuna arba'in ya duba ma'aikatansa, sannan ya shiga main part d'in gidan. Da part d'in Hajiya Mansura matar shi ta biyu ya soma. Part d'in wacce ya ke d'akinta ne na k'arshe haka k'a'idar sa ya ke. Kullum sai ya duba lafiyar matan shi da y'ay'an shi kamin ya kwanta.
Sallama ya yi ta re da murza key ta re da tura k'ofar ya shiga. Babu kowa a parlour kamar yadda ya yi tsammani. Sama ya hau. Ana ne ya d'an ji motsi a d'akin Hajiya Mansuran.
Kwankwasawa ya yi ya d'an jira domin ta zo ta bud'e masa k'ofa.
K'ofar aka bud'e, Wasila y'ar aikin Hajiya Mansura ta fito kanta a k'asa ta re da fad'in
"Sannu da zuwa yallab'ai. Ina wuni?".
Kallon ta ya yi daga sama har k'asa ka na ya girgiza kai ta re da fad'in,
"Lafiya k'alau". Ya fad'i hakane ta re da shigewa d'akin Mansuran.
Kwance ya same ta lullub'e da bargo har wuyanta. Zama ya yi a bakin gadon ta re da fad'in,
"Mansura lafiya dai ko? Na ga ba sanyi ake ba amma kin lullub'e kan ki. In ce dai lafiya". Ya fad'i hakan ya na kallon ta.
"Mtsw". Hajiya Mansura ta d'an ja tsaki ta re da fad'in,
"Sannu da zuwa. Kai na ne ke d'an sara min, ga d'an zazzab'i da ke son kama ni".
"Tashi maza muje asibiti". Fad'in Alhaji Usman ta re da mik'ewa.
"A'a ba sai munje ba. Ba ka ga fitan Wasila ba, ai yanzu nasa ta ba ni magani da ruwa na sha. In sha Allah ka min safe zan warware". Fad'in Mansura.
"Kin tabbata?". Fad'in Alhaji Usman ya na tab'a goshinta da ke sanyi k'alau ba alamar zazzab'i.
Jinjina masa kai ta yi ta na k'ara jan bargo.
K'ara gyara mata bargon ya yi ta re da manna mata kiss a goshi, ka na ya ce,
"Ki yi addu'a ka min ki yi bacci. Allah ya k'ara ma ki lafiya. Sai da safe. Amma dan Allah ki

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login