Showing 21001 words to 24000 words out of 162658 words
ke son ga ni?".
"A'a ban fasa ba". Binty tai saurin fad'a ta re da yin ga ba ta wuce kaka da ke kallon ta ya na girgiza mata kai.
Juyowa ta yi ta na kallon kakan. Wani irin zaro idanuwa ta yi sakamakon ganin Kandala da Basira sun bi ta jikin Kaka sun wuce. Za ta yi magana ta ji Ba kin ta ya mata nauyi. Kaka kuwa cewa ya yi,
"Shikenan Binty, sai wani jik'on. Allah ya tsare ki da tsarewar sa". Ya na ga ma fad'in haka b'at ya b'ace.
Sosai Binty ta ke son ta yi magana, amma ba kin ta ya mata nauyi. Sosai ta ke jin ba dad'i ta re da kewar Kaka. Haka ta yi ta bin Kandala zugui-zugui har su ka samu taxi su ka hau.
Tafiya su kai sosai kafin su ka zo wani unguwan marasa k'arfi. Domin kuwa in da su ka b'aro unguwa ce na masu hannu da shuni. Wannan unguwa Ku ma da su ka zo yanzu, unguwar ya Ku bayi ne. Wa ni madaidaicin gida su ka shiga mai d'auke da d'akuna guda shidda ciki da parlour-parlour.
Datu ce ta fito hannunta d'auke da tsintsiyar kwa-kwa ta na mitar ba ta dad'e da sharar tsakar gidan ba har an b'ata. D'ago kan da za ta yi ta sauke idanuwan ta a kan Kandala.
"In ce dai lafiya Kandala na gan ki tafe da Basira da Kuma wanna kyakkyawar y'a haka? Ina ki ka sa mo ta?". Fad'in Datu wacce ta yar da tsintsiyar hannunta ta na k'ara k'arewa Binty kallo.
"Hmm Datu ke dai bari. Wannan magana ce mai tsayi. Yanzu dai na kawo ma ki Basira ta zauna a nan don yanzu ko ma wa zan yi na kai wannan kyakkyawar yarinya gidan Alhaji Usman Mai Rabo, ita za ta mate gurbin Basirar. Sauran labarin sai na dawo ka da wata ta riga ni. Amma kin ga wannan y'ar iskan, ta so tai mana asara babba wallahi. Ba ri dai in je in dawo za ki sha labari". Fad'in Kandala ta re da aikawa Basira da harara har da rankwashi a tsakiyar ka sai da Basiran ta da fe kan ta.
"Kash! Kin san hali na Kandala wajan san labari. Dan Allah ki d'an so ma fesa min ka min ki dawo". Fad'in Datu.
"Kai, ai kin ga matsalata da ke kenan. Na ce mi ki sauri na ke yi, sai ka ce zan gudu. Ke dai bari na je na dawo". Fad'in Kandala ta re da ka ma hannun Binty su ka juya.
"Dan Allah kar ki wani wajan, don wallahi ko fitan da nai niyya na fasa, ina nan ina jiran ki".
"Ba matsala sai na dawo". Fad'in Kandala ta re da barin gidan.
Tafiya su kai kusan na kimanin mintuna talatin ka na su ka iso wani katafaran unguwa da ke da gidaje iri d'aya. Fenti ne kawai ya ban-banta. Fad'in tsaruwar yanayin unguwar da gidan wajan b'ata ba ki ne. Daga gyefan dama zuwa na hagu, duk tsarin ginin gidajan iri d'aya ne. Gida na tsakiya da ke gyefan hagu su ka nufa. Kwankwasawa Kandala ta yi ta re da d'an ja da baya. Wani soja ne ya bud'e k'aramar k'ofar k'atuwar gate d'in ta re da fad'in,
"Who's that? Who are u looking for? Who u wan see?". Cike da muzurai sojan ya fad'a kamar wanda ya ga suspect.
"N...na mie who de bring people for Alhaji wife to wash da kuma sauran gyaran gida to her". Da kyar Kandala ta iya had'a broken d'in, shi zaman bariki ne ya sa har ta iya shi. Kasancewar Kandala ta yi sana'a Kala-kala har da su sai da abincin a tasha. Ku ma ta yi zaman tafa. K'awarta da ta kwaso k'anjamau ne ya tsorata ta dai na wannan harkan ta koma d'auko y'ay'an mutane daga k'auye ta na kawo su aikatau.
Sojan nan ya shiga k'are ma ta kallo, duk da kuwa ya san ta, kasancewar ba yau ba ne rana ta farko ko na biyu ba da zuwan ta gidan. Mai da kallon sa ya yi zuwa ga Binty da ke tsaya ta na cin k'unban hannunta.
"Don't tell me say u bring this pretty girl to come and work here?". Fad'in wannan sojan ya na kallon Binty da ta zuba masu idanu domin Sam ba ta jin abunda su ke fad'i.
"Na madam se me ka bring her to do work for her pikin". Fad'in Kandala.
"Her pikin? Are you mad. You no say da guy na ashawo. Hin dey spoil peoples daughter. And na you dey bring them. God go punish you and madam pikin. God they see everything. If na your pikin will you allow her to come and work here? You'r selfish woman. God go punish you. And lemi warn you, if you tell hajiya watin a say, wallahi a go remove one of your leg that you uzam bring peoples daughters. Enter before I shoot you u with my gun".
Da sauri Kandala ta ka ma hannun Binty su ka shige cikin gidan.
Ban da gate d'in farko sun wuce gate kusan biyar ka min su isa ainahin gate d'in da zai sadaka da cikin gidan.
Hanci, baki, ido Binty ta saki ta na k'arewa wannan makeken gida da su ka shigo cike da k'auyan ci. Ga ma'aikata nan ta ko ina. Masu gyaran fulawa daban, masu bai wa fulawan daban. Masu kula da tantabaru daban, mata y'an aiki kuwa sun kai goma. Ka'totan gida mai d'auke da part part kusan goma. A gate na shida ne ma'aikatan gidan maza su ke da quarter d'in su. Su kuma mata quarter d'in su ya na cikin asalin gidan. Hakan tsarin mai gidan ne wato Alhaji Usman Mai Rabo.
Wani shashi su ka fara nufa wanda shine shashin uwargidan Alhaji Usman Mai Nasara, auran saurayi da budurwa kenan tun bai da ko sisi.
Zaune ta ke a kan d'aya daga cikin tantsama tantsaman kujerun d'akin. Sanye ta ke cikin wata doguwar rigar shadda wanda ya amshi jikinta. A k'allah za ta kai shekaru amsin a duniya, amma sam jikinta bai nuna hakan ba saboda kyawun jikinta da kuma hutu da gyara da jikin ke samu. Kyakykyawa ce sosai kuma fara tas. A ba kin ta akwai hak'orin maka har guda biyu gyefe da gyefe kalar golden wanda ke k'ara haskaka fararan hak'oran ta. Waya ce a hannunta ta na karanta Alqur'ani mai girma a cikin wayar.
Sallama su ka yi, sai da Hajiya Na'ima ta kai aya sannan ta rufe wayar ta re da amsa sallamar ta na mai kallon bakin k'ofar.
Shigowa Kandala ta yi ta re da zubewa a k'asa ta na gaida uwargida a wajan Alhaji Usman. Gyefe guda kuma ta na tsungulin k'afar Binty a kan ita ma ta gaida hajiyan, amma inaa Binty ba ta san ma ta na yi ba. Domin ta shagala da kallon tsararran d'akin da ya kusa tsayar da numfashin ta.
"Kandala ya gida? D'azu kuwa idan ba kunne na ba ne, na ji kamar Fasila ta na fad'a min kin zo d'azu gaishe ni, ni kuma ina sallah".
"Eh kwarai ni ce Hajiya. Na zo ki na sallah shi ya sa na tafi". Fad'in Kandala.
Jinjina kai Hajiya Na'ima ta yi ta re da mai da kallon ta izuwa ga Binty da a kallon farko ta ji ta shiga ran ta, ta ce,
"Kandala wannan kyakkyawar yarinya fa?".
K'ara gyara zama Kandala ta yi ta re da fad'in,
"Hajiya Mansura ce ta ce na kawo mata wata y'ar aikin wacce na kawo watan ba ya ba ta yin abunda ya da ce, shi ne na kawo wannan d'in".
"Ita d'in wannan y'ar wacece? Kuma ki na da tabbacin za ta iya abunda wancan d'in ta kasa?". Hajiya Na'ima ta jeho mata tambaya ta re da tsare ta da idanuwa.
"Em..ehyyy.. Ita d'in yar k'ani na ce a can Saminaka". Fad'in Kandala ci ke da in'ina.
Haka nan Hajiya Na'ima ta ji ba ta gam su da zan can da Kandala ta fad'i ba. Musamman da ta ji ta na in'ina.
"Me ye sunan ta?". Hajiya ta sa ke tambayan ta ta na mai tsare ta da idanuwa.
A nan ne kuma gaban Kandala ya fad'i, domin Sam ba ta san sunan yarinyar ba. Ta man ta shaf ta tambaye ta. Tab'o Binty ta yi ta re da fad'in,
"Ke wai ba ki iya gaisuwa ba ne? Ki gaishe da Hajiya mana".
Sai a lokacin hankalin Binty ya dawo. Hajiya ta kalla ta re da fad'in,
"Ina wuni?". Da ma Hamdan ya ko ya mata yadda ake gaisuwa.
"Lafiya k'alau Beauty, ki zauna mana".
Binty kuwa wani dad'i ne ya kusan sumar da ita saboda sunan da Hajiyan ta ki ra ta da shi. Kallon Kandala ta yi ta re da fad'in,
"Kin ga ni, ita ma ta san Hadaan. Ga shi ta ki da ni da irin sunan da ya ke kira na da shi".
Murmushi Hajiya Na'ima ta yi ta re da fad'in,
"Yaya sunan ki y'an mata?".
"Binty y'ar bola". Binty ta fad'a ta na murmushi.
Kallon Kandala Hajiya ta yi, ka na ta mai da kallon ta izuwa ga Bintyn ta re da fad'in,
"Binty 'yar bola kuma?".
Kamin Binty tai k'arin bayani caraf Kandala ta amshe ta re da fad'in,
"Binty ai a kwai shirme. A can garin mu ne fa ake kiran ta da haka kasancewar ba ta k'aunar wanka kullum dak'an-dak'an za ki ganta. Shi ne yara su ke kiran ta da Binty y'ar bola. Shine fa duk wanda ya tambayeta sunan ta sai ta ce Binty y'ar bola. Amma Sunan ta Binty ne".
Dariya Hajiya Na'ima ta yi ta re da fad'in,
"Duk yarinta ne za ta bari, wata rana ma idan aka ce tai kwana d'aya ba wanka ba za ta iya ba. Amma fa ni da ba din kin ce Mansura ta ce ki kai mata ita ba, ai da na ce ki bar min ita a waje na".
"Ai ba matsala Hajiya, idan ki na son ta ki karb'e ta, idan ya so na kawo mata wata. Ai duk d'aya ne da ke da ita". Fad'in Kandala kamar mutuniyar kirki.
"A'a ba za ai haka ba. Ai tun da ta riga da ta mi ki magana, ki kai mata ita kawai. Ni da ma ba y'an aiki na ke nai ma ba. Kawai yarinyar ce ta shiga rai na". Fad'in Hajiya Na'ima.
"Wallahi Hajiya ba matsala ki d'auke ta kawai".
Shuru Hajiya ta yi ta na wani tunani. Tabbas idan har ta ba ri Hajiya Mansura ta karb'i wannan yarinya to ba bu makawa d'an ta Suhail sai ya lalata ta kamar yarda ya saba lalata y'ay'an jama'a uwar sa ba d'aure masa gindi.
"To ki bar min ita". Fad'in Hajiya Na'ima.
Hankad'a labulan d'akin ta yi ta re da fad'in,
"Wannan k'aya ne wallahi. Yarinya ni na saka a kawo min ita, kuma babu wacce ta isa ta karb'e ta idan ba ni ba".
*HMMM AKWAI FA CAKWAKIYA.*
*ASSALAMU ALAIKUM READERS, GA NI NA ZO MA KU DA SABON LITTAFI NA MAI SUNA A SAMA, WANDA YA ZO DA ZAFI-ZAFIN SA, KUMA NA TABBATA ZA KU JI DAD'IN SA. BA ZAN CI KA KU DA SURUTU BA, KAWAI KU BI NI A FREE PAGES, KU DA KAN KU ZA KU GA NE BOOK D'IN NA DABAN NE. KAWAI KU NU NA MIN ONE LOVE WAJAN SIYAN BOOK D'IN AKAN FARASHI AKAN FARASHI MAI RAHUSA KAMAR HAKA:*
*FREE PAGES SUN K'ARE*
*Normal group shine mutum zai bi ya 500 idan ka ti ne, idan kuma ta account ne 300.*
*VIP kuma 1000 ne idan kati ne. Idan kuma ta account ne 700.*
*MUTANAN NIGER KUMA ZA SU BI YA KAMAR HAKA*:
*Normal group shine mutum zai bi ya 500F idan ka ti ne, idan kuma ta account ne 300F.*
*VIP kuma 1000F ne idan kati ne. Idan kuma ta account ne 700F.*
*EVIDENCE OF PAYMENT 08128755583*
*IDAN HAR BA KI KARANTA BOOK D'IN NAN BA WALLAHI KIN YI MISSING.*
*DAN GIRMAN UBAN GIJIN HALITTA IDAN HAR KIN SAN ZA KI FITAR MIN DA BOOK, KA DA KI SA YA, WALLAHI BA NA BUK'ATAR KUD'IN KI. KI TAIMAKA DAN ALLAH*
*MATAR SAYYADEE*
🌹 *15-16*🌹
Wani kanne ido d'aya Hajiya Na'ima ta yi ta na kallon Hajiya Mansura wacce ita ce matar Alhaji Usman Mai Rabo ta uku, wa to ta tsakiya.
"Ya ki ke haushi ke ba kare ba Mansura?". Hajiya Na'ima ta fad'i ta na sakin wani shu'umin murmushi.
Hajiya Mansura kuwa kallon Hajiya Na'ima ta yi, ta kuma mai da du ban ta ga Kandala da tu ni ta jik'e da zufa sai sa ka hannunta ta ke ta na sharewa. Sa ke mai da du ban ta tai izuwa Hajiya Na'ima ta re da fad'in,
"Ni ki ke dangantawa da kare a gaban wad'an nan fak'iran".
"You made me sai that. Ba yan kin fi kowa sanin yadda na tsani ihu a kai na. Ku ma na sha mi ki warning a kan shigo min d'aki ba bu sallama. Yarinya ku ma na hana, ba zan ba ki ita ba. Ta sa mo mi ki wata. Wannan ta wa ce". Fad'in Hajiya Na'ima ta na kallon cikin idanun Hajiya Mansura da ke jin kamar tai bindiga.
"Mu zu ba mu gani". Fad'in Hajiya Mansura ta re da watsawa Kandala wa ni mummunar kallo ka na ta nufi k'ofa. Sai da ta kai ba kin k'ofa ka na ta ce juyo ta kalli Kandala ta re da fad'in,
"Ki sa me ni yanzu a sashe na". Ta na gama fad'in haka ta wuce fuuu.
Kallon ta Hajiya Na'ima ta yi ta re da mik'ewa daga kan kujeran da ta ke ta ce,
"Ki jira ni yanzu ina zuwa". Ta na gama fad'in haka tai hanyar stairs. In ten minutes ta dawo parlourn hannun ta rik'e da wani babban ledan AYK da ke d'auke da tambarin fiffiken d'awisu a jiki. Atampopi ne guda uku masu tsada da kuma turare da kuma duba d'ari a ciki ta mik'awa Kandala ta re da fad'in,
"Za ki iya tafiya yanzu".
K'ara tankwashe k'afa ta yi za ta fara koro godiya Hajiya Na'ima ta d'aga mata hannu ta re da fad'in,
"Ba na son jin komai, kawai ta shi ki tafi, idan ina buk'atar ki zan nai me ki".
Mik'ewa Kandala ta yi ta re da nufar k'ofa. Da sauri Binty da tun d'azu sai k'ara k'arewa D'akin kallo ta ke yi ta bi ba yan ta ta re da fad'in,
"Ina za ki ta fi ki bar ni kuma? Ina Hadaan d'in?".
Kallon Kandala Hajiya Na'ima ta yi ta re da fad'in,
"Zan haura sama, idan kun ga ma, ki turo min ita sama".
"To Hajiya in sha Allah, Allah ya k'ara girma".
Cikin zuciya Hajiya Na'ima ta furta ameen ta re da hayewa sama.
Kallon ta Binty Kandala ta yi ta re da b'ata rai sosai ka na ta ce,
"Kin man ta abunda na ce mi ki kenan? Ba na ce mi ki Hadaan ya je k'asar waje karatu ba. Kin yi alk'awari za ki yi duk abunda na ce ki yi. Hakan shi zai sa na kawo mi ki Hadin d'in ki. Amma idan har za ki rik'a bijirewa umarni na, to wallahi ba zan ka ko mi ki Hadin d'in ba. Ku ma daga yau duk wanda ya tambayi sunan ki,