Showing 27001 words to 30000 words out of 120027 words

Chapter 10 - Halysaah Book 3 By Khaleesat Haydar

ga hassadarta kwance fuskarta kiri kiri, duk wani African in ya zo wuce wajen sai ya sake kallon Khaleesat, Ajay ya karasa har inda Hajja ke zaune ya gaisheta, Hajja na kallonsa tace "Junaid sai da aka kare convocation zaka zo saboda Allah? To menene amfanin zuwan ka kenan muna kokarin komawa gida?" Ajay yaki tanka ta ya dau Apple din kusa da ita, ya gaida su Gimbiya Firdausi dake gefenta duk suka amsa masa babu yabo babu fallasa, kallon Mami yayi ita ma ya gaisheta ta amsa, Khaleesat ta duka gaban Hajja ta gaisheta cikin sanyin murya, neutrally Hajja ta amsa tana kiran jikar wata aminyarta da ta hango wai ta zo ba ayi hoto da ita ba, Khaleesat ta kalli su Gimbiya Firdausi su ma ta gaishesu, har sai da Hajja ta kallesu tace "Ana gaishe ku" sannan suka amsa don yi suka yi kamar basu ji ba gaba dayansu kuma, still at that ma Aunty bata amsa gaisuwar ba fuskar nan nata a murtuke kamar bata taɓa ko murmushi ba, Khaleesat ta ɗan kalli Walid da ke gaisheta yana kallonta, sunkuyar da kai tayi ta mayar masa da gaisuwan, A takaice Ajay ya amsa gaisuwan Cousins dinsa, Jay kuwa dama tuni ya bar wajen yana answering phone call, Baby tayi fari da ido tana kallon Khaleesat tace "10/10 kika yi kyau...." Su Iklima duk suka juya suna kallon Baby, ita dai Khaleesat murmushi kawai tayi ta kalli Baby tace "Thank you" Ganin har sannan Khaleesat na durkushe Hajja tace "To ki je ki yi ma Hadiyah Allah sanya alkhairi mana, ga can kannen mijin ki kuma sai ki duka a nan" Mikewa Khaleesat tayi cikin sanyin gwiwa ta ɗan kalli Ajay dake kallonta, sai kuma ta karasa har inda su Hadiyah suke hotunansu tana Kallonta tayi mata congratulations, Hadiyah tayi kamar bata san da ita take ba sai jawo cousins dinta da kawayenta take suna hotuna happily, duk da tun da taga Khaleesat Happiness din nata yayi vanishing kawai pretending ta ci gaba da yi take fara'an da bai kai zuci ba, wata kawar Hadiyah dake ta kallon Khaleesat kamar ta samu TV tace "Hi, I love your dressing, you look beautiful" Khaleesat tayi mata murmushin karfin hali tace "Thank you, and you too" Hadiyah ta kara jin wani kololuwar bakin ciki ya tokareta kawai dai ta ci gaba da sabganta bata nuna ba, Shahuda dama barin wajen ma tayi gaba daya, babu wanda ya bi ta kan Khaleesat dake ta tsaye a wajen da suke hotunan, daga karshe cikin sanyin jiki ta koma gefe ita kadai ta tsaya, ganin Ajay ne ma yasa duk suka kama kansu babu wanda ya tsaya disgata a wajen cause he is looking at each and every one of them, ita kam Khaleesat time to time take satan kallon inda Jay ya koma ya tsaya da Maminsa tana masa magana, ta kalli wajen for the 4th time kawai suka hada ido da shi and he took his eyes off her ya juya baya, a hankali ta sauke idonta, duk Ajay na kallo, bayan Jay ya gama magana da Mami ya tafi gun wani abokinsa ya tsaya, wayarsa ya ciro yana dannawa, Khaleesat ta bude jakar ta jin shigowar message wayarta, ta ciro wayar tana kallon message din babu ko kiftawa, Ajay dai kallonta kawai yake daga inda yake tsaye, can yaga ta juya a hankali ta kalli inda Jay yake, Jay ya ɗan kalleta bayan sun hada ido ya dauke kai ya mayar da wayarsa cikin aljihu, Wani Apple din Ajay ya dauka zai bar vicinity din Hajja ta bi sa da kallo tace "Ahmad Junaid" Juyowa yayi, sai kuma ya dawo ya tsaya kusa da ita yana jiran jin me zata ce, tayi shiru kamar bazata ce komai ba don babu abinda ya tsaya mata a rai irin yanda taga daga shi har Jay babu wanda ya kalli inda wani yake balle yayi ma wani magana, kamar ma basu taɓa sanin juna ba, duk tunaninta ko ba komai suna gaisawa, can ta kallesa, shi dai cin Apple din hannunsa yake with calmness yana kallon Khaleesat dake danna wayarta alamar she is sending a message, sae kuma ta juya ta kalli Jay that is looking at his phone too shi ma ya ɗan juya ya kalleta, Ajay ya dauke kai daga direction dinsu ya kalli Hajja yace "I am listening" Ajiyar zuciya Hajja ta sauke tace "To shi ma hotunan baza kayi da yan uwanka ba kenan kake nufi ko me? Ban ga alamar kayi niyyar zuwa taron nan ba don da kayi niyyar zuwa ba sai da aka watse taro zaka zo ba" Ajay yace "Ni zan je in samesu mu yi hoto?" Hajja ta kalli Baby da ta zo daukan Apple tace "Ke Hauwa kira min Hadiyah" Baby tace to sannan ta tafi, sai ga Hadiyah ta zo fuskarta babu wani fara'a, to cover that up tace "Wallahi na gaji kaina ma ciwo yake min, da ma mu tafi gida kawai" Hajja tace "Hadiyah ba ku yi hoto da yayanki da matarsa ba" Hadiyah ta kauda kai tana ɗan yatsine fuska sai kuma ta juyo tace "Oh haka ne fa" Kiran me yin hoton tayi sannan ta koma gefen Ajay ta tsaya me hoton ya fara daukansu hoto, Hajja ta kara aika baby taje ta kira Khaleesat, after snapping 2 pictures with Ajay Hadiyah ta zaro ido tace "Wayata fa? Waye na ba wayata ko nayi misplacing dinsa ne?" Da sauri ta bar wajen irin zata je tambayo cousins dinta da kawayenta wanda ta ba wayarta a cikin su, nan kuma hoto ne da Khaleesat bazata yi ba, Hajja ta daga kai ta kalli Ajay tace "Kai yanxu abinda kayi jiya ka kyauta Junaid? Ko da yake bari mu karasa gida tukunna ba maganar nan wajen bane" Dai dai nan Khaleesat ta iso gun Hajja bayan Baby taje ta kirata, ta kalli Ajay da ya juya ya bar wajen sannan ta duka gaban Hajja tace "Ga ni Hajja" Gimbiya Firdausi ta karaso kusa da Hajja tace "Hajja ga mota za a fara kai ki gida" Bata rufe baki ba sai ga Jay ya iso gun yana kallon Hajja, calmly yace "Hajja za ayi dropping din ki gida, the driver is around" Hajja tace "Toh" Kallon Khaleesat Jay yayi yace "Are you following Hajja Home?" Gimbiya Firdausi ta kallesa tace "Kamar ya kenan? Manyan ta basu fara tafiya ba sai ita Jawwad, wannan kuma wani lissafi ne, ae su Hadiyah zata bi ba Hajja ba, Hajja da Fulani kawai za aje ayi dropping a dawo a motar" Jay dai bai ce komai ba, Gimbiya Firdausi ta kara da cewa "Tun da ta shigo zuri'a babba haka ai kamata yayi ta dinga sakin jiki tana shiga yan uwan mijinta ba ta dinga rabe rabe ba" Jay ya kalli Khaleesat calmly yace "Go nd meet them, naga baku yi hoto ba" Ita dai Hajja babu abinda tace a wajen, Khaleesat ta mike a hankali ta nufi inda su Hadiyah suka taru, sai da ta isa wajen ta fara waigen inda zata ga Ajay amma bata gansa ba, kamar yanda suka mata daxu yanxu ma babu wanda ya bi ta kanta harkan gabansu kawai suke suna nishadin su, Shahuda ta lura Ajay baya surrounding din alamar ya bar wajen, hakan yasa ta karasa har gaban Khaleesat fuska daure tace "Wai ke halan mayya ce da dole sai kin zo inda muke? Tun daxu muke avoiding dinki amma sae kara cuso kanki kike wajen mu, Waye ajin ki a nan ko kuma uban wa ya gayyace ki?" Su Iklima duk suka juya da sauri don ganin ko Ajay na wajen sai suka ga baya nan, haba nan duk suka kallo Khaleesat, tana ganin haka bata sake tsayawa ta ji abinda za su fada next ba ta juya ta bar wajen ta koma can wani waje daban ta tsaya cikin sanyin jiki tana dube duben inda zata ga Ajay......

*Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah, ur evidence via 07087865788*
HALYSAAH PAGE 114

Khaleesat dai na tsaye tana ta kallon yanda motoci ke ta zuwa daukan masu sarauta zuwa gida kuma babu wanda ya bi ta kanta, Hadiyah sai aikin makale ma Jay dake rike da graduation folder dinta da wayarta take duk inda yayi sai ta bi sa, a hankali Khaleesat ta bude jakarta ta ciro wayarta, call log dinta ta shiga tana ta kallon number Ajay, can dai tayi dialing number ya fara ringing amma har ya katse bai daga ba, ta sake kiransa nan ma no reponse, jira tayi taga ko zai biyo kiran amma still har bayan 15 mins bai kira ba, mayar da wayar tayi cikin jaka cikin sanyin jiki, ta ci gaba da bin kowa na wajen da kallo, duk baƙin da suka zo taya Hadiyah murna sai da aka tabbatar an maida su masaukin su, ya rage iya Cousins dinta kawai da 3 of Her friends ne a wajen sai Jay, Jay na son ce ma Khaleesat ta je ta hau mota ganin she is just standing amma bai san ta ya ba saboda yanda Hadiyah ta makale masa not even giving him a breathing space, Khaleesat na hada ido da Walid da ya dawo wajen ta sauke idonta kasa, ya nufi har inda take tsaye yana kallon fuskarta yace "Hey, mu je inyi dropping din ki a gida ko?" Da kyar ta daga idonta tace "Yace min yana zuwa in jira sa" Yana mata wani kallo yace "A ina ku ka sauka?" Ta girgiza masa kai tace "Nima ban san wajen ba" Wani shegen murmushi yayi mata yace "Za mu hade...." Daga haka ya juya ya bar wajen ta bi sa da kallo zuciyarta na bugawa, har kasan ranta take tsoron Walid da Aunty, Duk Jay na lura da su kuma duk tunaninsa da Walid yaje wajenta zai ce mata su je yayi dropping dinta a gida ne amma sai kuma yaga ya tafi ya bar ta tsaye wajen, a hankali Khaleesat ta sake bude jakarta ta ciro wayarta tayi dialing number Ajay, har ya katse bai ɗaga ba nan ma, ta sake kiransa no response again, jiki a sanyaye ta mayar da wayar cikin jaka gashi ta gaji da tsayuwa, After some more minutes Jay ya juya ya kalleta, sai kuma ya dubi Hadiyah dake making phone call, ya jira har ta gama sannan yace "Hadiyah go and tell her to come over ku tafi gida it's getting late, the second car is back...." Hadiyah na kallonsa tace "Who?" calmly yace "Halysaah" Da wani expression tace "Wacece kuma haka?" Bai sake tanka ta ba, ta juya masa kunnenta tace "Ni dai cire min dankunnen nan Honey, it's very tight...." Yace "Ba gida za mu tafi ba why remove it?" Ta hade rai tace "A'a just take it off pls, I am not comfortable with it" Bai sake ce mata komai ba ya kai hannu ya fara cire mata dankunnen nata, yana cirewa ya daga kai ya kalli Khaleesat da tayi masu kallo daya ta dauke kai, ya gama cire earrings din ya mika ma Hadiyah tayi masa side hug tana kallonsa tace "Thanks love" Khadijah ya kira bayan ta iso wajensu yace "Je ki ce ma Halysaah ga mota yana jira za ku tafi gida" Hadiyah ta wani hade rai tana kallonsa tace "C'mon Honey ba fa tare muka zo nan da ita ba, definitely mijinta ne zai tafi da ita since they came together, jiya ma ai shi yaje ya dauketa daga can gida suka yi tafiyar su" Khadijah tace "Tare fa suke da Ya Junaid and he is somewhere around here, salon mu tafi da ita mu yi masa laifi, balle ma ya nuna baya son ta zauna cikinmu, gwara kawai a bar masa ita kawai Ya Jay ba ruwana da jarabansa" Jay dai bai ce komai ba ya ciro wayarsa dake ringing yaga Mami ke kiransa, picking call din yayi ya koma wani wajen ya tsaya yana answering call din nata, bayan ya gama wayar kawai ya ɗan kalli side din su Hadiyah kafin ya juya ya nufi Khaleesat, har ya isa inda Khaleesat take tsaye bata yarda ta kallesa ba yace "Ga mota can ki tafi ki shiga a maida ke gida, or are you waiting for anyone to pick you up?" Tayi shiru bata ce komai ba, sai kuma ta daga kai ta kallesa a hankali tace "Nace ina son magana da kai" He was quiet for few seconds bayan ya dauke idonsa daga kallonta, ganin Hadiyah ta nufosu don sai a sannan ta kula ya tafi wajen Khaleesat, yace "Let's chat, ki je ki shiga mota kawai" Nuna mata inda motar yake yayi, ta juya ta nufi wajen tun Hadiyah bata karaso wajensu ba, shi kuma ya ciro wayarsa ya kira driver din ya ce masa ya tafi da ita kadai ba sai ya dauki kowa ba a motar, Hadiyah ta hade rai bayan ta iso gabansa tana kallonsa tace "Dole ne sai kayi magana da ita ne Baby? Shi mijin nata da ya kawota bai san zai maida ta ba? What's ur business with her??" Jay ya kalleta strictly yace "It's my duty to make sure everyone leaves here to their various destination Hadiyah, stop questioning me" Hadiyah ta ɓata fuska tana kallonsa, ya ja hancinta yace "To yi kukan mu ga" juya masa baya tayi, ya kamo hannunta ya juyo ta yace "Zaki fara ko" Ko da wasa Khaleesat bata yarda ta juya ba har ta isa gun motar, tana shiga ciki driver ya ja suka bar wajen, gaba daya jikinta a sanyaye yake, nan ta fara tunanin ko kawai ta gaya masa sunan hotel din da Ajay ya kai ta jiya yayi dropping dinta a can a maimakon gida don ita tsoron zuwa wannan apartment din take bata san me zata je ta tarar ba, gaba daya family din ma tsoro suke bata she is not comfortable staying together with them, tun bata bari sun yi nisa ba kawai ta gaya masa ya kai ta hotel din, haka kuwa aka yi bayan kusan tafiyar minti ashirin da biyar suka isa babban hotel din, ta bude motar ta sauka tayi masa sai anjima sannan ta shiga cikin hotel din ta wuce sama, a hankali ta bude kofar dakin ai kuwa taji sa a bude ta shiga cikin dakin closing the door gently tana kallon Ajay dake kwance kan gado yayi rub da ciki yana bacci ta can ɓangaren gadon ba inda ta kwanta ba daren jiya, haushi ya cikata lokaci daya ta hade rai, shine zai yi tafiyarsa ya bar ta ita kadai a wajen ya dawo nan yana bacci abunsa, shi yasa take ta kiransa no response, tana tafiya a hankali ta karasa cikin dakin ta ajiye handbag dinta ta cire mayafin kanta ta sauke gashinta da ta nannade sannan ta fara cire jewelries din jikinta gaba daya ta ajiye su saman bedside drawer, ta cire rigar jikinta kenan ta ajiye gefen gado zata dau doguwar rigarta dake linke ta ajiye saman akwati taga ya bude idonsa a hankali sae a cikin nata, zaro ido tayi with shock ta durkusa kasan dakin da sauri ta rufe fuskarta da gado taji kamar kasa ya bude ta shige don she is just wearing bra and pant, kauda kansa yayi daga kallonta ya mayar zuwa daya side din dakin ya lumshe idonsa, Khaleesat tafi minti uku bata dago kanta daga boyewar da tayi jikin gado ba tsabar kunya, a hankali ta lalubo rigar da ta cire a gefen gado, tana durkushe a haka ta saka rigar don ta kasa tashi tsaye, bayan ta mayar da rigar ta dago kanta a hankali taga har sannan yana facing daya bangaren dakin, da kyar ta mike kamar munafuka ta shiga banɗaki don bata yi la'asar ba, ta kulle kofar bandakin ta jingina jiki tana turo baki, ta fi minti goma a toilet din ta kasa fitowa duk da ta gama alwala, daga ƙarshe ta dake ta fito sai taga ya ma fita daga dakin, ita dai har lokacin kunya bai saketa ba, da ta sani bandaki ta tafi ta canza kayan, she thought he was sleeping deeply shi yasa har ta cire kaya a dakin. Ajay na zaune dakin da Hajja take wajen karfe bakwai da rabi na dare yana sauraronta, Aunty da Gimbiya Firdausi da Hajiya A'isha duk suna zaune dakin su ma ko wacce ta murtuke fuska, rai bace Hajja taci gaba tace "To ina amfanin tahowa da ita in haka ne? Aikin banza kenan ai in dai zaka kai ta wani waje ka ajiye bayan kasan al'adar mu ba haka take ba, sam baka dau al'adun mu a bakin komai ba Junaid a haka wai kuma kai ne Yarima me jiran gado, ke kuma Fulani wannan maganar ma har sai kin gaya ma Sarki? Akan me zaki gaya masa?" Gimbiya Firdausi tace "To baya ganin kowa da gashi Hajja, baya mutunta kowa, gwara da ta gaya ma sarki don shi kadai yake gani da mutunci kuma bazai ki jin maganar sa ba, banda raini da walakanci yaushe zai dauki yarinya bai ji kunyan idonmu ba ya kai ta wani wajen ya ajiye bayan yasan duk waje daya ake sauka idan sha'ani irin haka ya tashi, ita yarinyar er gidan uban wacece ita da bazata zauna a gidan nan ba? Wani irin fi'ili ne wannan yake son shigo mana da shi family? Ko akan sa aka fara aure? Auren nasa ma auren joni" Hajja ta kalli Junaid tace "Ka je ka maidota gidan nan har zuwa sanda za ku bar kasar nan da daddaren nan ba sai gobe ba, in ka san bamu kai ta zauna gida daya da mu ba da ka bar ta can Amurka kayi tahowar ka kai kadai tunda kai ne dolen Hadiyah ba ita ba" Aunty da Hajiya A'isha suka gyada kai alamar dai dai kenan yaje ya dawo da ita, After few seconds Ajay ya kalli Hajja calmly yace "Why is it a must

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login