Showing 39001 words to 42000 words out of 431207 words
na ci gaba da tunanen hiran mu da ya Amina din murmushi nayi nace baki san komai ba yar uwa.
Zaki sha mamaki idan kin san nice mai shirya wanan plain din haka murmushi na dan sake nace ashe nima shu,umar kaina ne ban sani ba.
Kiran Yusuf ne ya shigo min yana tambayan ina ina nace hostel a takaice yace akwai mutane ne nace akwai su amma kadan yace gashi nan zuwa yanzu sai kazo nace dashi ya kashe wayan.
Maryam ta dawo daga wurin gyaran kai ta samay ni akwace take fadin ai na dauka barci kike yi nace na fara ya Amina ta tayar dani ga waya.
Nan nake bata labari hiran ya Amina dani tayi dariya tana bude tukuyan abincin mu tace bata san ke ce mai director ba yanzu na zuciyar shi.
Da sauri nace zuciyar shi fa kikace tace uhumm wai ke baki sani ba idan baso a tsakanin ku kina nufin zai ko kalle ki ne ma.
Shiru nayi ban bata amsa ba sai da ta zauna nace wai ke da tunanen ki ke nan akai mu tace bani ba kowa ma saboda kun dace dashi.
Nace baki ji ba ke nan don babu ta ida muka dace dashi wallahi ni ina ni ina wanan miskilin mara dariya da fara,a.
Zaiyi dariya wata rana sai kinyi mamaki zakice nace maki watarana amma fa idan kinyi nasaran canza shi din don kan ki ne zaki taimaka ba wani ba.
Nace a a gyara maganan ki dai maryam don ba gaskiya zuciyar ki take fada maki ba tayi murmushi ta soma cin abincin ta.
Yusuf ya kirani yace fito gani a waje ban bata lokaci ba na mike saboda na matsu inji abinda yasa suka tsayar dani garin har wanan lokaci.
Dan simple makeup nayi na fito a can nesa da mu na hango motar su a fake na karasa inda yake da sallama na gareshi.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Agidan su kuma Nafisa ne ke waya da kawar ta da ta baro kaduna wace suke kira da madam a cikin su tantiriyace ta kwarai na fada.
Da mijin ta sai dai kamar itace mijin ba mata ba don sai yadda tayi da mijin a gidan idan tace kada ya zauna bai isa ya zauna ba.
Atakaice dai ya zama mijin tace ga madam ko kawayen nata zasu iya aiken shi ya tafi komai nisan wuri koda da kafane sai yatafi yadawo.
Itace Nafisa ta kira tana son fada mata abinda ya faru da ita bayan barin su kaduna ta dauko wayan ta madam ta soma nema a wayan sai dai wayan nata ringing ba a daga wayan ba takaici ne ya kama Nafisa.
Ta ja tsaki ta na fadin yar iskan ko gidan uban wa ta shiga waya nata ringing haka bata dauka ba har ya katse bata dauka ba kin sake kiran layin tayi a lokacin sai taci gaba da tunanen ta tanayi tana kada kafan ta daya dake har de.
Babu abin da take tunawa sai irin shirmay da ta tafka jiya din akan bakin kishin dake damun zuciyar ta akan mijin ta wanda take mashi son daba taba yi ma wani abu ba sai dai kuma a kasan zuciyar ta ba so bane can na har abandan don da zai iya shiga wani halin jarabtan rayuwa a yanzu tsaba zata iya gudun shi ta koma wa mai maski.
Wayan nata aka kira ya hanata karasa muna jin birnin zuciyar sai ta dan sake guntun murmushi tana daukan wayan nata tare da fadin Aloh ina kika shiga nake ta kiranki baki daga waya ba.
Cikin muryan barci madam din tace tana hamma baki hangale bata fasa magana duk da tana hamman tace wallahi barci nakeyi tunda rana.
Tsuki Nafisa taja tare da fadin barci sai kace wata mai ciki ko kasa ni don Allah watseke fuskan ki kiji ni magana nake son muyi dake ki ban shawara.
Madam tace ina jin ki matar manya dadi Nafisa take ji idan su madam na fada mata wanan sunan madam din ne tace ke nake sauraro fa.
Wallahi ke dai madam kin san ko sai da munafukar tsohonwan nan ta hadamu da yarinyar da nake fada maku tace mu rage mata hanya ?
Don Allah ki bari madam ta fada itako tace sosai kuwa ai saida muka dauke ta a mota daya mukai tafiyan.
Tace yaya kika bari haka ya faru don Allah kin ko san iein mijin ki neman su mata keyi ido a rufe nasha fada maki ki nisanta shi daga ko wace mace in ba muraharamin sa bace har kika yarda hakan yafaru dake.
Ke dai bari madam nanu mashi rashin yarda na ga hakan amma ya rufe ido yace shi yace umurnin mahaifiyar shi ce dole ya bi.
Madam tace yaya kukayi a motar injin baki basu daman sakewa da juna ba a motan ?
Tace ai in fada maki ban yarda ko daga kai yayi ya kalle ta ba kuma nima ban sake ayi hakan ba sai dai mun kwashi rikici dashi sosai da muka iso gida wai zai tafi office a sauke shi sai a wuce da ita.
Bude mashi wuta nayi sosai in fada maki sai da mukayi kaca kaca dashi na kuma hana shi fita sai da aka kaita a ka dawo san nan ya tafi.
Da haushi da bakin ciki ya kamani duk na farfasa kayan falon nan gaba daya don in nuna mashi bacin raina don gobe kada ya kara min haka.
Madam tace kash aike kinji matsalan ki ke da zaki bishi da lalama ki nuna mai ba wata mace sai ke a duniya daga baya sai mu sake shirya wa tace.
Madam idona ya rufe a lokacin da kishin ganin wanan yarinyar a kusa dashi amma da ya fahintar dani shi irin su ba su gaban shi shi yanzu wace mace zai kalla ta bashi sha,awa sai naji hankalina ya dan kwanta a lokacin.
Madam tace amma kin so ki bada mu wallahi kai kin ma dai kwafasa wallahi yanzu ke ko irin matan abujan nan ya lalubu maki har ki ta da hankalin ki haka mudake da wuka a hannun mu nama kawai muke jira.
Kawai yanzu idan ya dawo kije ki bashi hakkuri akan abinda kikai mai din don kada ya zarge wani abu a gare ki.
Kin ga zaki ji a bakin shi ko ita wanan yarinyar wacece a garesu kin dai san yadda zaki bugi cikin shi ai muji komai a saukake.
Tace zanyi kamar yadda kika ce din amma ba yanzu ba zan dai saka ido in gani idan suna tare ko basu tare sai musan abinda zamuyi daga baya.
Sun dauki lokaci suna maganan akaina ana ta kulla sheri da tugu akan mazajen su kafin suyi sallama madam tace zata kira zuwa gobe taji indan da wani matsala kuma.
Na gama shiga da komai daki na da taimakon wata yar gidan namu da ta dawo tagan ni da kaya ta tsaya taimaka min.
Kayan jikina na fara cirewa san nan na fara gyara kayan ina aje komai a inda nake bukatan shi na gama na zauna ina tunane a raina.
Bakomai nake tunane ba sai mijin buzuwa da Allah ya jefo a rayuwana a dan lokaci ya taimaka min yau gani da kudi a hannu na wanda yakai dubu dari ta dalilin mijin buxuwa da iyayyen shi duk na samay su.
Waya na dako a cikin handbag dina ina neman layin ya Amina don in fada mata abinda ya faru don komai ya faru dama nakan kirata in fada mata.
Kira uku ta daga wayan ina ji bata kusa da wayan ne a lokacin mun gaisa nake tambayan yaranta tace suna lafiya sun tafi islamiya.
Nace anty kin san wani abu da ya faru yau tace ina zan sani Khady nidake kaduna zaune kina abuja ke.
Nace anty yau na hadu da mijin buzuwa danaje sayayya tace kun sake haduwa kuma again nace wallahi anty wai duk wanan uban kayan da na sawo nazo biya sai ake ce min ai ya biya bayan da suka sauke ni ranan ya ba driver dubu hamsim ya bani.
Kai da gaske khadija nace wallahi anty kuma su suka kaini gida sai dai shi bai so su dauke ni ba sai abukin shi ne yace saboda mama ne suke min haka.
Dariya tayi tace to Allah ya saka da alheri ki dai bi a hankali inda duk kuka hadu don buzuwan nan ba imani ke gare ta tana iya komai akan mijin ta.
Ya Amina ni inama zan kara ganin shi kuma Allah dai ya tsaga rabona daga Aljihun shi wanan karon mutumin da ko yaushe take a cikin hade fuska banda gaisuwa may zai hada ni dashi kuma.
Daga haka muka kawar da zancen shi muka dauko na iyayyen take fada min cewa sunyi waya da baba yana fada mata kudin su na ritaya ya kusa fitowa kwanan nan.
Ihun jin dadi nayi don murnan iyayyen mu zasu fita acikin hali talaucin da suka shiga na ritayan da mahaifin namu yayi muke cikin halin kaka nakayi.
Tace ai zan riga ki ji idan kudin sun sauka don haka sai abinda kika samu daga baya nace ai ni indai daddy zai samu bukata na ya biya ke nan.
Yanzun ma shawara nakeyi inje banki gobe in tura mai kudin da mijin buzuwa ya bani don akwai kudaden da zasu isheni a hannu na tunda ina da abinci waddatace .
Tace haka akeso mutum idan ya samu ya tuna da iyayyen shi dama dako kin kyauta wallahi dama sallaman ki ya hanani tura mashi kudi wanan watan.
Haka dai mukai ta hira da ita daga karshe mukayi sallama na kashe wayan tare da mikewa na jona electric dina don in dafa dan abinda zanci da dare.
Kira, a na saka a wayana ina aiki ina bin kira a don ni gwanace a wurin iya hadda tun ina yar shekara sha hudu na sauke alkurani mai girma na sake maimaitawa yakai kashi uku yanzu don duk wanda yasan yaran minna ya sansu da ibada da kamun kai ga girmama na gaba dasu a duk inda suke.
Da wanan halin namu nake shiga ran mutane farat daya kowa tsakani na dashi gaisuwa ne na mutunci da sani girman wanda ya girmay mun.
Na gama na zuba a plate na dauko ledan ruwa guda cikin wanda na sayo na aje a dakin na zauna don in fara cin abincin sai ga kiran waya ya shigo min.
Binta ce ta kirani a lokacin na dauka kafin wayan ya tsunke hiran mukayi sosai ranan da ita har nake mamakin ko nawa ta sa awayan ta haka don da mun sake wanan hiran take dauko min wani.
Har take fada min yadda akayi ranan da zamu wuto da buzuwar yayan su tace bazata shiga mota dani ba mama ta dage daya zo mata da maganan kan lalai sai sun tafi dani.
Nace kin ko ga tunda muka kama hanya batai min magana ba nima ban masu ba daga ita har mijin ta.
Tace wanan ai dama shi miskili ne magana kamar aiki yake ganin sa a gare shi zai iya zama da kai kuyi awa daya baice uffan ba haka kuma matar shi anty fati itama take shiru shiru bata magana.
Nace aiyanzu sun samu mai magana a tsakanin su haka yasa ta samu daman musguna mata yadda take so ai.
Tace ke kin ko san halin wanan matar shu,uma ce wallahi ta karshi da farko da tazo boye halin ta tayi kamar wata mutumiyar kwarai da ita.
Sai daga bayane ta fitar da kalar ta kowa ya sani bata kaunan ko dan uwan yaya ta ganshi a gidan nan wallahi.
Nace wuri ta samu wallahi ni kar nake kallon ta don banga abin tsoro ba anan ku dai na fahince ku kuna bata girma ne don mijin ta yana da hali a cikin ku.
Tace ga tsiya nace eh mana haka din ne amma in bashi ba ta yaya zaku zauna wanan matar ta dinga raina maku hakali har tace wai idan tana wuri kada ayi dariya .
Tace ina ma kika sani khadija ai sai wani lokaci da mukaje hutu wurin su a abuja ba girma muka dawo gida kwanan mu biyar ko sati bamu kai ba matsi yai muna yawa a gidan.
Muka matsa ma yaya zamu dawo ga yan uwanta nan muna ganin yadda take ji dasu amma mu ko falo ta hana mu fito muka koma kamar wasu bare ba yan uwan maigidan ba.
Dariya nake mata sosai tace Allah ko magana mai karfi wai ba ai mata a gida tace ba kallo ba komai sai zagi da hattara ga anty Fati damu da ita duk muka koma daya.
Bayan mun dawo sai ga anty Fati ma ta dawo wai a kaduna zata zauna bata iya zama da buzuwa a abuja bata bari ko miji ta gani idan yana gida.
Nace ke ki bari don Allah ashe ba karamar shuuma bace tace baki santa bane Khady wanan fa ko kashe mutu tana iyawa fa.
Nace wanda Allah yabata ikon kashewa ba wani kan ai yafi karfin ta wallahi ba abinda zata iya wanda Allah bai tashi yi da bawan shi ba.
Ni don Allah har kin ban haushi da wanan maganan naki don ba a gidan ku nake ba wallahi da taga tsiya a guri na nifa irin matan barikin nan haushi irin su nake ji.
Zako kiji nata don bata da hali mai kyau ko kadan akan mijin ta zata iya yiwa mutum komai musan man ma ce ko waya tayi da wata ranan sai sunyi jidali sosai da ita ke ta zama mai kaya ko shi yanzu bai da yadda zaiyi da ita ne kawai wallahi.
Nace ya dai ga dama ne Binta idan ka ganshi ga mutum har mutum amma baida kuzari gun mace tir yayan ku ya zama mijin hajiya wallahi.
Haushin abinda na fadi taji da fada muka karasa wayan a rana na kashe ina mata dariyan shakiyanci na gama na wanke kayan na samu wuri na kwanta.
Washe gari da wuri na fita don ban yarda in makara in ba wani dalili ya tsayar dani ba mai karfi shi kadai zai sani makara kawai.
Ban da yawan kawaye sai mutum biyu yan department din mu kosu shirin mu dasu don sun ga nafisu kawo wuta sosai a class din shine likewan su dani.
Banda wasa ga abinda ya kaini abujan daga school sai gidan mu sai ko idan wani dalili zai sa na fita a ranan zan fita.
Yau ya dawo a gajiye don daga wurin aiki ya wuce wuri wasan polo da suke yi don dan wasan ni ne sosai wanda yana daya daga cikin abinda ke kawo mashi kudi a lokacin bai dogara ga aikin shi ba yana buga buga irin na maza gida da waje shike sa yana samun mahaukacin kudin da yake riko.
Wanka yayi yana saka kaya a jikin shi ta shigo dakin dan juyawa yayi ya kalle ta ya kawar da kan shi yaci gaba da abinda yake yi.
Karaso wa tayi gare shi tana wani rangaji na daukan hankalin shi ta sake abinda yake so ya sauko mata har mazaunan ta.
Cike da sallo ta iso gare shi sai dai tsiyan shi da ita duk gayun ta bata damu da saka kamshi ba kuma har yanzu ba gwanewa tayi ba da iya kwalliya shine ma yake kokarin wurin gyara mata idan tayi wani kwaliyan zasu fita.
Gata da son karya sai dai ko bokon kasar su bata samu ba kuma babu na Allah a tare da ita abin ya taru yai mata yawa amma hakan bai hana shi son abin shi ba.
Rungumoshi tayi ta bayan shi ya sauke wani ajiyan zuciya yana dan murmushin jin dadin ganin ta tace yau ina ka shige haka ne ta dawo ta gaban shi suna fuskantar juna.
Bai ce komai ba yadan jajeyeta ya dauko turare yana fesa ma jikin shi tace har da daren ma sai an feshe jiki da turare ko fita zakayi ne haka ?
Sai lokacin yayi magana yace sai zan fita ne zan saka kamshi a jiki na ke baki son kamshine ashe yasa baki sakawa .
Taji zafin maganan amma ta daure don in da sabo ta saba da gorin saka kamshin da yake mata din ko yaushe kuma hakan bai sa ta saba da sakawa ba.
Tace muje kaci abinci yace na koshi ta dubeshi da sauri tace tare da fadin ban gane ba yace mun ci abinci da Yusuf kafin in dawo.
Juyawa yayi ya nufi saman gadon su yana jawo laptop din shi tasan idan ya fara dakilan laptop sai ranta ya baci kafin ya gama.
Idan tayi magana kuma yace business yake a ciki shi ko wani abin dariya tayi ya dago yana duban ta na lafiyan ki kalau kuwa ?
Sai yaji tace maganan turaren da kayi ne dai yaban dariya har na tuna da yarinyar da mama ta saka mu dauko ranan.
Bakaji wani irin kamshi tiraren da takeyi ba kamar tayi wanka dashi yace tasan kan ta ne yasa ta saka