Showing 72001 words to 75000 words out of 431207 words
fito na canza kaya jikina zuwa dogon riga nayi kyau sosai a cikin rigar lokacin yamma yayi sosai nace zan je gidan su hafsat kawata da tai aure ta haihu bani gari.
Kallon da mamaki min ne yasani tsarguwa sai daga baya na fahinci rigar da na saka ajikina ne yasa take min wani kallo da bashi ba.
Sai na dawo tace min batare da ta kalle ni ba na fita jiki a sanyayye zuwa gidan hafsa din dake bayan minna minicipla coucil.
Hafsa kawa ta ce tare muka taso da ita kasancewar unguwar mu ba nisa da karatuna ya dawo minna na hadu da ita muna zuwa girl day dake a bayan old airport tare kusa da tsohon makarantar wtc na mata.
Bayan mun gama ta samu wani guy ta aura dan kabilar Nufe dake tashen kudi a lokacin .
Na fito gida a hankali nake takawa iskan marance yana kadawa inda nake ganin fuskokin wa yan da na sani muna gaisawa jefi jefi dasu a hanyan.
Har na isa gidan na samay ta tana girkin abincin dare tana gani na ta tare ni da murna muka gaisa ta nufi falon su dani ina biye a bayan ta.
Sai bayan na zauna ne ta dauko min baby ta har yaron ya fara wayo sosai ta miko min shi sai bina take da kallo wai na sauya gaba daya na zama wata big girl dake nace kai haba dai hafsat har dake cikin fadin haka.
Tace wallahi gaba daya kin sauya ma sani na ne khadija nace yanayi ne kawai wallahi yazo a haka ba wani abu may ye sunan yaron na tambaye shi.
Muna hira tana duba girkin da takeyi har ta karasa takawo min nace wallahi hafsat a koshe nazo gidan nan watarana zanci.
Mikewa nayi saboda magariba daya kawo jiki sosai na bata asai ma yaro takalma ina shirin fitane mijin ta ya shigo gidan.
Allah ya gani jini na bai hadu da mijin ta ba tun farko asali ma nice ya fara cewa yana so sanin shi da nayi dan duniya mai wayan yan mata da kyale kyali yasa ban bashi fuska ba.
Naje hutu kaduna kafin in dawo na samu sun dinke da hafsa har sukai aure yanzun ma da ya shigo gidan ya samay ni sai da ya daga min gira ba tare da sanin hafsa ba.
Harara na watsa mai na fice gidan tare da yi mata sallama nadan yi nisa naji muryan shi a baya na yana fadin khadija ji mana.
Juyowa nayi fuska a daure ina kallon shi nace lafiya dai ko ya washe baki yace don Allah sorry to distub you kin boye fa da yawa ban san kin zo garin ba ai dana kawo maki gaisuwa.
Dan murmushi nayi nace ba komai ai gashi mun gaisa yanzu dama boye nazo gani na ganshi har yayi wayo.
Yace in ba laifi ki bani layin ki akwai maganan da zamuyi kin san dai yanzu ba da bane zaki iya fahinta na har yanzu ba kin fita raina bane.
Auren hafsa Allah ya nufa sai munyi da ita amma ni ke ce choice dina tun farko hafsa dai ta shishige min har na aure ta.
Dakata Adam kada ka kara taro na da irin wanan maganan ko da hafsat bata gidan ka kai ba choice dina bane ka sani ban hurda da maza irin ku da kafan su bai tsayo a guri daya ba.
Ke kizo kici arziki kibar arziki kawai don yanzu arzikin bana yaci uban na da zan iya daukan lalurar ki da komai naki wallahi.
Wani kallo na watsa mai na up and down nace a haka din kake tunanen zan iya cin amanar kawata aminiya ta nace Allah ya tsare ni da masu irin halinka.
Na wuce na barshi tsaye a gurin yana bina da kallon zalama irin ta yan iskan maza yana sosa kan shi baida mu da mutanen dake wuce ba a saman titin.
Na shigo gida ana kiran sallah magariba dakina na nufa sai da mama ta gama alwala ta kwada min kira na fito inyi sallah lokacin sallah yayi.
Nace mama kin manta bana sallah ne ta ce oho ta shige dakin ta sai bayan sallah isha,i daddy ya dawo gidan suka zauna a dan falon mu har kanne na ciki suna kallon NTA dake labaran marance.
Daddy ya duba bai ga na shigo ba yake tambayan ina nake mama tace ina dakina kafin yace wani abu wayan shi ne yayi kara ya dauka bayan sun gaisa ne yayi mai magana yana son magana da mama ne daddy yasa handfree din wayan yadda zai ji abinda yake fadi.
Sun gaisa yace mama don Allah a dan sasauta ma khadija da takurawa tace na saka kuna zargin ta da aikata ba daidai ba ni kuma nasan idan har kun yarda da tarbiyan da kukai mata ba abinda zaisa ta canza daga baya kuma.
Mama kiyi hakkuri khadija na nan a yadda kika santa alheri kuma yanzu na fara maku kuda ita muddin ina raye sai abinda yafi karfina ne bazan maku ba.
Alherin yar ku gare ni ne ya jawo maku hakan ba ina nufin Khadija da wata manufa bane sai alheri don ta cancanci haka a gare ni so kuyi hakkuri a sake mata fuska babu komai sai alheri ga haduwana da khadija.
Bayan sun gama waya da mama ya gama daure ni a gaban su da ban gane manufar maganan shi ba daddy ya kwala min kira daga falon.
Da sauri na shigo dakin har lokacin shigan da na fita gidan hafsat ne a jikina ban cire ba na samay su a zaune falon.
Gaidasu na fara yi tare da samun wuri na zauna mama tace khadija yaushe ne kika canza haka wai ?
Nace cikin dago kai da mata kallon mamaki nace mama wanin abin nayi kuma again tace yanzu bamu da shakat a gidan nan dan abu kadan sai ki kai karan mu ga saurayin ki.
Da sauri nace mama wane saurayina kuma danakai karan ku gare shi tace wanda kika jajibo a Abuja mana wanda ya fimu sanin zafin ki a yanzu.
Mama ni ba saurayina bane wallahi ba wani abinda ya taba shiga tsakanin mu na soyayya har yau tace in babu yaya kika kai karana wurin shi wai na saki gaba a gidan nan tunda kika dawo.
Kai kai innalillahi haka yace maku mama fada nayi mai fa akan abinda yayi min nace kina zargina ga abinda kika gani ya bari ban so.
Daddy sai dariya yake muna ni da mama don yasan duk iya binciken shi bai gano wani abu da nake aikatawa a bayan su.
Tun daga wanan ranan mama bata kara daure min fuska ba muka koma daidai a gidan kamar yadda muke a baya.
Wayana gaba daya na kashe sai zan kira nake kunna wa don ban son wani abinda zai haifar min da matsala kuma tsakani na da iyayyena a gida.
Ya rage saura kwana biyar mu koma makaranta sai ga kamal mai bi mun ya shigo da kaya wai ya Amina ta shigo gari.
Da gudu na kwasa nayi waje ina masu sannu da zuwa tana sallaman driver da ya kawo ta gida na rungumay ta na sake ta naja hannun yaran na rungume su a jikina.
Ciki muka shiga gaba dayan mu bayan ya Amina ta huta taci abinci tana zaune a falo na shigo da karamin dan ta a hannu na tace dada hutu ya kusa karewa dai nace wallahi ya Amina.
Nakai zaune kusa da ita tace dama ina son in zo gida in samay ki kafin ki koma ne nace tau wani abin nayi ya Amina ?
May ye ma baki yi ba khadija ina ke ina Abdulsamad mijin buzuwa fati da mijin ta ta barshi dole don wanan buzuwa ke yanzu kike kokarin jefe kan ki ciki.
Kai ya Amina kuna bani mamaki wallahi wai ya fada maku muna soyayya dashi ne halan na san dai shi ba zai fada ba.
In kuma don wanan abinda yayi ne kuke zaton muna tare ne da bakin shi ya fada ma daddy gaskiya ba sona yake ba.
Haka kike tsamani ke ko azaton ki duk wanan alaman da yake gwada maki ba so bane hakan wani namiji zai samay ki yace bai so ki.
Kin fi buzuwa durin na ya mace sai dai fari da gashi zata gwada maki ko farin ma ba wani can ba don ke ma ba baya ba.
Sai yanzu nake gane maganan baban boy da yake cewa ke din matar manya ce watarana ina ganin kamar fadi dai yake yi.
Abin mamaki ne yadda har Abdulsamad ya fada tarkon ki abinda ba wanda ya taba tsammani zai iya sai gashi lokaci guda har kin fara canza shi da naki sallon soyayyan.
Mama da ta shigo dakin dauke da kwanon da ta tuka muna tawaska ta aje tana cewa ke ma dai kya fada idan anyi magana tace an matsa mata ba soyayya suke da shi ba ko takai karan guri shi.
Shi ko ba kunya gare shi ba ya kira mutane yana rokon su akan a daina matsa mata don Allah ni daddy ku har mamaki yake bani yarda ya yarda da mutumin nan a lokaci daya.
Da ban san halin shi ba sai ince ko don kudin shine yake son shi ya Amina tayi sauri cewa a a mama ba halin daddy bane haka da yana bin kudi da ba zan auri Abban su boy ba.
Mama tace nasani ai shine abin ke ban mamaki yanzu ai tace yarda ne kawai wallahi in badon buzuwar matar shi ba ai Abdulsamad mijin aure ne ga ko wace mace ta samay shi.
Nan ya Amina ta fara ba mama labarin shi da rayuwan su har karshe nace wai ku may yasa kuka damu da wata buzuwa can ne.
Kowa tashi tafishe shi amma ni bata cikin tsarina ni dai kawai bai min bane ina zan jefa kaina ga family man mai iyali da yawa haka.
Wanan duk ba matsala bane tunda yana da abin kula da koda mata nawa yayi niyar yi abin damuwa shine kishi da wanan buzuwan da bata da imani ko kadan.
Balle idan taji ba barin shi zatayi ya aure ki ba kuna tana iya yima rayuwan ki illar yada taiwa fati ko sunan ta baya son ji yanzu.
Allah bai bata iko a kaina nace ke don Allah rufawa mutane baki ana baki kina roko may kika taka da kike fadan haka nace mama Allah.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Mommy wayayir mace mai haba haba da jamma irin matan nan ne masu fara,a a fuskan su kuma ita har cikin zuciyar ta haka take da kowa sai dai bata daukan raini.
Abin ta bai rufe mata ido ba tana da ilimi na boko wadattace don duk matan na Abban su Abdulsamad suna da ilimin su ya aure su in ka debe ummi wace iyakarta secondary kadai tayi har hajiya mama mahaifiyar Abdulsamad a gidan shi ta hada karatun ta na NCE wanda dama koyarwa take koda ya aure ta.
Ita anty amarya ma da aikin ta ya auro ta wanda yanzu ta daina duk ya hana matan nasa aiki ya tsaya ga bukatun su kuma.
Mommy ne zaune tare da Abban yana karyawa hajiya mama wadda yaranta ke kira da hajiyan mu ko hajiya mama ta shigo falon.
Akan maganan tafiyan mommy da Abdul din ya bugo yana mata tuni a daren jiya don sun fara tatauna maganan sai Abban bai bada goyon baya akan haka ba.
Yanzu shine ta shigo ayita akaare idan zai yarda shigowan mama yayi daidai da shigowan hajiya ummi da anty Amarya data kira kaffinta shigo.
Sun sami wurin sun zauna tare da fuskantar shi yasa yasan da magana sukazo mai ummi ce ta fara maganan amma sai anty amarya ta dan saka larin kishi a ciki tace ni naga ai ba sai taje ba ya mayar da matar shi mana zaifi sauki.
Ummi da wanan kkaron bata goyi bayan maganan anty amaryan ba tace a a Sadiya tunda har kika ji wanan yaron ya bukaci hakan ai sai mu gode ma Allah da har wanan tunanen yazo mashi a rai.
Ko ba komai ya kamata ace sanin halin ita Nafisa ya kamata wani daga cikin mu yaje ya zauna kamar yadda ya bukata din don ace mai daki shiyasan ida ruwa ke yoyo a dakin.
Nidai kunsan ba lafiya ke gareni ba ba zan iya zuwa ba ita dai suwaiba din ya dace ta tafi don ita dai zainab din ya dace taje ta zauna dasu ta saka ido tunda da iyan bawa zasuyi tafiyan.
Murmushi Abban yayi yace ke nan dai kun gama magana kuna goyon bayan dan ku ko ummi tace ba hakana bane Alhaji.
Ganin dai dacewan hakan mukayi yasa muka goya baya ga maganan shi da kan shi babangidan ya fara tuntubana da wanan zancen da yazo na bashi goyon baya akan haka.
Sai anty amarya ta kalle ta ta rausaya da kanta gefe daya bata kara magana ba har lokacin da Abba ya gama ja ma mommy kunne akan zaman da zatayi a gidan dan nasu.
Suka bar mommy dashi a falon kowa ya kama gaban shi tun wanan ranan mommy ta fara shirin tafiya Abuja gidan Abdulsamad wanda suke kira da babangida kasancewa sunan mahaifin maigidan su ke gare shi.
Abdulsamad bai fada ma Nafisa zuwan mommy ba gidan sai cin karen su ba babbaka suke ita da yan uwanta a gidan banza ta fadi masu kasa gasasa dama haka aladansu yake yar su ta auri mai arziki dangi su kwaso a taru aci arzikin ta.
Mommy bata boye ma Anty Fati zancen tafiyan ta ba inda ta kirata ta fada mata da bakin ta tare da cewa zatayi iya kokarin ta taga ta shirya tsakanin ta da mijin ta kafin ta bar Abuja din.
Allah ya kiyaye hanya Fati tai mata tare da cewa mommy amma fa sai kin hada da hakkuri don kun san Nafisa bata kaunar taga kowa ya rabi yaya Abdulsamad.
Abinda yakai ni shi zanyi idan tayi ba daidai ba dole ne in fada mata gaskiya koda kuwa bata so dariya tayi don sanin halin Nafisa da tayi kamar yunwar cikin ta.
Tsaye yake tsakar falon inda yake umartan masu aikin da ya shigo dasu da su gyara part din Fati yana masu kwatance yadda yake son gyaran.
Nafisa da ke barci a dakin ta Yanyala ta shiga mata da maganar cewa may ke faruwa ne taga ana gyaran dayan part din da tace na uwar gidan ta ne.
Kamar ba cikine a jikin ta ba ta diro saman gadon ta fito inda masu aikin su nan ta hausu da fada wayasa su aiki a gidan ta ba a fada mata ba.
Daga bayan ta ya bata amsa yana saukowa daga sama yace nine nan maigidan na basu aiki suyi in biya su wani irin kallo mai kama da kai asuwa ta aika mashi.
Bai tsaya kulata ba sai kokarin shiga dakin da yake yi tasha gaban shi da sauri ta tsare shi may kake nufi ne samad da wanan gyaran da akeyi ?
Yace abinda kika gani Nafisa shi nake nufi don gida nawa ne ba naki ba kamar yadda kika fadi yanzu.
Nan hankalin ta ya tashi sai ta fara surutu ita may yake nufi da ita da zai mata haka yace don yaga zata haihu zai dawo da fati da yaranta gidan shi.
Tace nasan dama kule kulen da ake shiryama ke nan kake yawan zuwa kaduna akai akai yanzu dama ba so na yan uwanka keyi dani ba .
Shi dai bai mata magana ba don mazan dake gidan suna aiki ya fita batunta basu raba hali a gaban su ba.
Hankali tashe ta kira madam tana fada mata abinda ke faruwa madam tace kika sani ko watace zai dauko ya saka a dakin ba Fati ba ?
Nan hankalin ta ya kara tashi sosai tace Nafisa dam wanan tunanen baizo min ba sai da kika tunatar dani haka yanzu.
Madam tace to zauna nan kina fada akan fati wata tazo ta shige dakin kina gani saboda sakaci irin naki in zaki mike ki mike tun yaushe muka gama da wata fati can.
Wacce hudi daya mukai mata muka fitar da ita a gidan har diyan ta sai tarihin su yanzu har kike tunanen ita zai mayar dakin ta.
Ke kasar ku fa zaki koma aiki kaifi sai Niger nan kusa kafin ma mu dawo aiki ya kankama ko mu huta da ko wacece ma ke son muna kutse haka cikin ruwan sanyi.
Nafisa tace madam kin san ba zuwan ba kuma ba kudin nake jiwa ba don zan iya saida da duk wani kaddara da nake da akan wanan aikin tunda yanzu na rasa gane kan shi.
Matsala daya ne shine mutumin nawa yanzu kin san matsi yake min tun wanan tafiyan da mukayi ondo ya kara burge min a gidan nan baya sake min har yanzu ga kuma lalurar cikin nan dake jikina yanzu.
Madam tace ke dai kawai tawa ki nemi kudi in ma bai barki