Showing 279001 words to 282000 words out of 431207 words

Chapter 94 - Mijin Buzuwa By Makawa

04 Dec 2025

18344

hannu.
Ahhaye nanaye inji yan mata naki ikon da mulkin ke nan dadin abindai baki cikin gadon gidan nan idan ma don iyalin shi ne ba dai don ke ba bakar manya mai bakin nacin tsiya.
A haka zaki kare wurin kalan diya kina fadan gado dasu gadon da bazaki ci ko sisi a cikin sa ba kuma ki sani gidan nan gidanane kije can ki nemi gidan ki.
Nace gado gado yan cin gado manya to kin sani ko ki riga mai dukiyan mutuwa ko a lahira zakici gadon naki ke nan.
Bakar manya kurwa na kur akan ki ko kina yawo da maita a fili ne nafi karfin kamun ki wallahi ke har kin isa kizo ki samay ni kice ga yadda kike so a gidan nan.
Nace gashi kuwa na nuna maki isa ta a gare ki idan kin isa zoki kwata da karfi ki canza masu inda suke so din na juya wurin munafukar nace ke kuma sa aranki kamar kin bar gidan nan kun gama zama mu zuba dani daku agani.
Na kama karkada kafana daya tana kallon bata bar wurin ba sai da nasha gori ta kare da fadin bari samad ya dawo yau in san inshi ya baki wanan damar na takamu yadda kike so nace Allah dawo dashi lafiya.
Sai gab da magariba muka shige ciki ga yarinyar ta nason zuwa wurin yan uwanta amma sun hana karshe ma suka turata part din uwar nata aka rufe.
Abinci na dora muna dayake indomie zanyi dama yasa ban dora da wuri ba na fita da yaran shan iska waje.
Sai da nayi sallah na fito na dora ban fito ba sai da dahu na kwashe muna a babban plate ni dasu na zubawa laraba nata daban muna zaune muna ci ya shigo falon yana gyara nicktie din wuyan shi zuwa sasautawa.
Gaidashi da zuwa mukayi dani da laraba sai Affa ya gaida shi ya kalli karamin yace kai ba zaka gaida ni ba nacewa yaron daddy ka gaida Abba mana kamar yadda suke kiranshi.
Ina sauraren yai min magana akan Nafisa sai naji shiru bai ce kala ba ya juya ya fita daga dakin nan na fara ba laraba labarin abinda ya faru a falon.
Tace ikon Allah mata da son kai haka diyan gida ma ba zaki barsu suyi yadda suke so da gidan uban su ba.
Nace shine dalilin da yasa kikaga ban son su fita idan bangidan su kadai haka kuma rufe kofan da nake saki yi sanin halinta da nayi ne don zata iya shigo maku tace kunyi mata wani abin can daban.
Yanzun jiran shi nake ta fada mai yazo inji abinda zai fada kuma tunda bata laifi ita a gurin shi sai naga laraba tayi murmushi tare da fadin uhumm uwar dakina ai abin naki da sauki ke.
Ga yadda ta shigo gidan nan ta mayar da uwar yaran nan ko wata bora tafi ta albarka a gidan nan amma ke gashi har yana shigowa duba ki kuna tafiya a tare har kina iya mayar mata da martani ai abin naki da sauki sosai wallahi.
Ita fa mai gaba daya tai mata a gidan nan daga ita har yaran na ko ya koma bai ma kaunar ganin su ga baki daya sai da uwar shi ta tashi tsaye sosai fa akan lamarin.
Nace ko may akace wanan matar tana yi ai ba a mussu da hakan don ban taba fanin karfin halin kishi irin nata ba ni dai.
Shiru shiru har aka kwana biyu banji yayi magana ba kuma kullun idan na dawo zan kai yara su sha iska a wajen gidan.
Ashe abinda ban sani ba shine tun ranan tayi mai magana yace so kike in hana yara na jin dadin rayuwa in in ganta yan uwan ki a kan su .
Wai ke may yasa baki tunane kafin ki aikata abune don Allah nan dai suka dan kwasa da ga karshe ya fice ya bar mata part din ta.
Wanan dalilin ne ya sare mata gwiwa bata sake tayar da zancen ba sai dai zaman yaran a gidan yana matukar dagz mata hankali sosai da ta kalle su sai taji wani irun bakin cikin da ba gaira ba ta dalili ya rufe mata zuciyar ta .
Gidan madam ta nufa duk da cikin jikinta yayi nauyi yanzu madam ta tare da sheri ta ga ranta a bace yake take tambayan ta may kuma ke faruwa ne wai ?
Ta cire dan karamin gyalen da ta yafe a jikin ta tana fadin na gane wanan shegiyar yarinyar idan banyi da gaske ba a gidan nan madam wata rana zata iya cin duduniyata.
Wai ki duba yar iska da wayon banza zuwa tayi ta kwaso diyan samad daga kaduna wai sun zo mata hutu anan garin da sauri madam ke tambayan yaushe haka ya faru ?
Tace ba nakiraki nace sunyi tafiya ba satin can a aiko min da abinda zan saka ma shegiya a kofan ta madam ta tambaya tace kin saka din taja tsuki tace na saka mana amma banga komai ba wallahi.
Shegiya banda kyau da kara bajewa ba abinda take yanzu ni kaina na hango abinda samad yasa y auro ta ashe.
Madam ta kumshe dariyan ta tace lalai wanan yarinyar ba karamar yar duniya bace kinga hakan da tayi zai saka ta haskawa a idon shi yo wanda ke son dan ka ai yana son ka ke nan.
Kinga tafi mu dabara dauko yaran nan da tayi sai yanzu nima na kara gaskanta maganar Sabuwa na ranan da tace muna ganin ta hakana tunda tayi karatu kada ji mamakin tafi mu wayo .
Nafisa dake gefe tace komai aka ban inyi a kanta nayi amma banga wani ci gaban hakan ba dole yanzu sai idan na haihu in dire ma shegiya Niger ayita ta kare acan wata kila ma kafin in dawo ta kara gaba.
Ke yanzu ma fa zuwan nan gidan ki da nayi akan yadda take kokarin juya zuciyar shi da zancen yan uwana ne nazo.
Don indai yace sai ya kore min su to lalai nima ba zan zauna ba dama ni zaman ya zamay min kamar dole ne an takura min wallahi.
Kai haba Nafisa may ye matsalan ki yanzu a duniyan nan banda zancen kishiyan nan komai kika nema kin samu a gurin shi yai maki yaiwa yan uwan ki aiko Alhamdullahi ko.
Ta tabe baki tare da fadin hakane kuma inda wanan da wanan gaskiya ba abinda na nema a gurin shi da bai mun ba .
Gashi har yau asiri na aiki kan yar iska ko motar shiga ya kasa sai ma yar banza wai duk da haka baisa tayi ziciya ba ta fita.
Tana ganin yadda nake shiga ina fita ina saka gwalagwalai a gidan ina yadda raina ke so itako iyakarta part din sai kuma idan zata fita ya sauke ko yasa driver ya sauke ta.
Madam tace to mai yafi rai dadi ga hakan aiko wanan abin alfahari ne gare ki kinga taso muje ma wani guri da aka fada min wani kafirin kasan Togo ne yazo aka ban labarin shi ina Allah Allah dama in fada maki sai gashi kin shigo ma.
Da sauri tace shine baki sanar dani ba tun wuri ai irin su sun fi dadin aiki tunda kikaga har an dauko shi a kasan nan kin san ko yakai aiki kenan.
Suna a gaban arnen togo ya baza farin kudi irin na da da yake aiki dasu a gaban shi suna kallo mai mashi fassara yana gefen su zaune.
Sai da ya duba ya kada kai ba tare da sun mashi bayanin abinda ya kawo su ba ya fara bayani mai fassara mashi na fada masu.
Jikin Nafisa har rawa yake sai da ya gama bayanin shi tace ita dai kafin ma in kai ga ciki din har in haihu tana son in fice daga gida gaba daya.
A sa masu tsanar junan su ta daina burge shi yaji komai sunan ta aka kira a gaban shi ya tsane ta suka baje mai kudi ya basu iya sanin sa sukai godiya suka fita yace sati daya ya bata zan bar gidan nan kafin sati ya cika idan aiki baiyi ba zai bata kudin ta .
Jikina tsuma suka bar wurin arnen da farin ciki don zumudi ko gidan madam bata samu komawa ba ta wuce gida don fara aiwatar da abinda arnen yace tayi.
A dai dai lokacin ne kuma muke zaune a dakina da maryam take tambayana ko na aiwatar da abinda anty Salbiya ta bani inyi.
Nace kai maryam ni fa yanzu komai ya fita min rai wallahi irin abubuwan nan ni ba cika son su nake yi don ba yarda nayi dasu ba.
Wani kallo tayi min tace amma ke din nan to ki sani samu yaci annabawan Allah balle ke din nan khadija idan kina tashi tsaye ki tashi tun kan dare yai maki a gidan nan don wanan matar ba zaune take ba akan ki.
Nace taje tai tayi mana indai mijine gata gashi ai tayi ta kayan shi kai maryam ta girgiza tace lalai ba banza kila ta barki ba.
Nace kai maryam har kina ban dariya wallahi nifa duk abinda zatayi taje tai tayi ina kaya suke maryam ta tambaya nace suna a cikin jakkar da na fita dashi ranan har yau ban cire su a ciki ba wallahi.
Miko min su nan idan baki so nace kwasa duka ki ta kaya don Allah dauko min to nako mike na dauko mata ta duba sai naga ta falke ledan wanan hayakin ta mike boner din saka turaren wuta ta dauko a falo ta dawo kuryan ta turara min har yana hawa min kai sosai.
Nace gaskiya maryam ke ma shuumace dama anan zaki saka kikace in baki zaunar dani tayi ta fadakar dani sosai akan zamana da nafisa din a gidan har sai da jikina yai sanyi sosai.
Nace in Allah ya yarda yau din nan zanyi amfani da sauran ni da sabulai da na gyaran gashi kawai nake amdani dasu wanan din wagalan yi nake gani gare su.
Da dare bayan na gama komai a gaban maryam nayi amfani da komai yadda tace inyi dasu don a gidan maryam zata kwana tare damu.


ZAINAB IDRI MAKAWA
SEENABU
1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Madam zaune a dakin Nafisa sun baje suna shan ferfesu da aka sayo masu don ko tace su Samiha su dafa yanzu da take da cikin nan sai ta dinga jin karnin shi a bakin ta.
Madam tace wai shi wanan mai auren budurwan dai yau kwanaki sun kusa cika naji shiru mana .
Nafisa tace au kin dauka mu din na wasa ne ai wasa yake damu wallahi don haka zata bar gidan nan batare da ya san yar iska diya mace ba.
Dan bakar da na dana ma shegu na nan dam na aikin shi har yau dan yadda na daure su ko kallon yar iska da sha,awa bai iya.
Dariya suka sa madam tace aini na kosa inga yadda yar iska zata bar gidan nan ranan insha dariya don Allah da an fara ki kirani inzo insha kallo.
Ai tafiyan nan da yayi kwana biyu ne ya kofsa muna da yanzun kila ta dade da ficewa gidan nan kema Nafisa wani lokaci akwai ki da sanya wallahi ai da tun yana nan kikai ta masu overdoze din shi wallahi.
Samad akwaishi da shegen wayau wallahi ko ranan ina hayaki ya rutsa ni sai da na wayance mai da fadin turaren maiduguri nake bulawa gida.
Kin san ina ganin ganeni yayi sai dai baiyi magana ba don shi haka yake bai faye saurin magana akan abu ba da sauri..
Nan madam ta kara kitsa mata yadda zatayi abin yai mata aikin sauri ba tare da bata lokaci ba tace ai da ya dawo za,ayi ta ta kare gidan nan.

Daddyn mu ne ya kirani awaya yana sheda min alherin da AA yai masu na alheri tunda daddyna ya fara bayani ban iya magana ba shiru nayi ina sauraren shi.
Ajiya zuciya na sauke tare da fadin bai fada min ba daddy bai sanar dani wanan alherin da zai maku ba.
Daddy yace haka ake so khadija biyayan ki ne ya kaimu ga haka ai idan baiji dadin zama dake ba hakan ba zai samu ba kidai muna godiya don Allah sosai a gurin shi.
Mun gama waya da daddy ina mamaki a raina yadda AA yai wa iyayye na alheri bai sanar dani ba duk da daure mai danakeyi a kwanakin nan .
Gashi yanzu bai gari sun tafi jos wani aiki filin gwaunati da yace zasuyi acan kwana biyu kafin ya dawo wanan godiya ba awaya ya dace in mashi shiba sai idan Allah ya dawo dashi lafiya.

Yau tunda na tashi banjin karfin jikina tun cikin dare zazzabi da amai ya damay ni sosai har washe garin ranan monday din gashi zamu fara exam a ranan.
Dole haka na daure na fita na rubuta exam din cikin rashin walwala na juyo na dawo gida a falo na zube maryam da ta fito ta kirani nace da ita gani gida kwance banda lafiya.
Hankalin maryam ya tashi cewa tayi gata nan tafe hankalin laraba ya tashi sosai sai amai nake kwarawa a gurin.
Maryam ta shigo fitowan ta ke nan daga gurin exam bata je hostel ba ta wuto gidan daga school.
Tana zaune ta tsura min ido wayana dake gefena yai kara har ya katse ban iya dagawa ba wani kira ya sake shigowa again da kyar na amshi wayan hannun maryam da ta dauka tai recieving tana fadin AA ne fa.
Da kyat na dauki wayan na kara a kunne na da sallama da kyat shima na iya yi don yadda nake a galabaice kasan ties din falon.
Yadda yaji muryana yasa yace da sauri Deedar lafiya kike kuwa kafin in bashi amsa wani amai ne yazo min na mike da sauri don zuwa yi a toilet.
Maryam ne ta dauki wayan tai mashi bayanin halin da nake ciki yace please maryam ki taimaka kuje asibiti zan ma driver waya yanzu yazo ya dauke ku.
Ba a jima ba driver yazo muka fita zuwa asibitin Nafisa dake daki har labari ya samay ta dariya tayi tace wa Yanyala kilama mutuwa zan yi don ta hadani da wani katon bakin arne ne yai min aiki.
Dariya suka sa a lokaci daya Yanyala tace ita dama zamana a gidan yakai mata ko ina tana gudun inzo watarana in fara zama wani abu a gidan.
Yadda jikin nawa yake yasa dole aka daura min ruwa sai dai sunce ba kwana zanyi ba idan ya kare sunga yadda jikin yayi zasu iya sallamana inda sauki.
Yana jos ya matsa ma Yusuf sai su taso ranan da sauran abokan tafiyan shi dole suka kamo hanya dawowa Abuja din ba shiri.
Barci na samu sosai nayi da aka samin drip din tunda na falka around five na sake mayar da barcin sai yanzun da na falka kuma lokacin tara da wani abu na dare.
Tsaye suke a kaina shida Yusuf da wani daya da ban san shi ba sai laraba da yaran dake zaune a gefe na tayi tagumi maryam kuma tana shigowa dauke da kulan abinci daga kofa.
Dan murmushin karfin hali nai mashi tare da fadi da kyat yaushe ka dawo ne ?
Yace yanzun muka iso khadija ya jikin naki nace da sauki cikin rufe idona ina yunkurawa kamar zan tashi da sauri suke hada baki gurin fadin yi a hankali fa akwai ruwa har yanzun a hannun ki.
Kallon hannun da yai min nauyi nayi na mayar da idona ga sauran ruwan daya rage saura kadan ai Yusuf yace.
Maryam AA din ya juya ya duba tare da tambayan ta mai likitan yace yana damun ta ne ?
Tace Allah dai ya rabasu lafiya tace mai tana dariya Yusuf ne yace da ita kina nufin aure yai albarka ke nan dai tace insha Allahu ciki har ya girma haka.
Hararan ta nayi na lumshe idanuwa na cikin jin nauyi da kunya daya rufe ni a lokaci daya tambaya ya sake mata da cewa shi likitan ne ya fadi haka maryam ?
Yusuf yace muje mana muga likitan zaifi sauki ji a bakin shi suka juya zuwa wurin likitan tare da maryam da tai masu rakiya.
Likita yai masu bayanin yadda zasu gane yake sheda masu stress ne yai min yawa sai dan maleria da ya kamani amma sunyi min alluran maleria din insha Allahu zan samu lafiya ko yanzu idan ruwan ya kare zasu iya tafiya dani gida.
AA yace wa likita da sauri da dai an barni har zuwa gobe a gani likita yace ba damuwa zamu iya komawa gida ai.
Sai sha daya saura muka dawo gidan har shi don sai lokacin Nafisa tasan da dawowan shi garin.
Da yake ba nice da girki ba a ranan muna shiga muka rufo kofan part dina daki na shiga nayi wanka na fito ban jima ba zaune na kwanta sai safe.
Koda gari ya waye maryam da laraba suna kitchen har lokacin ban iya

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login