Showing 27001 words to 30000 words out of 95984 words

Chapter 10 - Mijin Marigayiyya Complete Sakina Yazid

18 Sep 2025

9716

bai daga ba sai ta zata ko fushi yayi, amma dai zuwa yau kwana uku abun ya fara bata tsoro kada taje ko wani abu ne ya sameshi.

Ta riga ta san babuu credit a wyar don haka ko balance ma bata duba ba; shi din ba mutum ne mai son saka mata credita ba, idan ma tayi magana sai yace wa zata kirawo ko kuma me zata yi da data din. Idan aka yi albashi dai idan ta yi magana yana saka mata naira dari biyar, shine zata samu ta raba ta sa data sauran ta dan yi waya. Don haka yanzun ma babu na wayar sai dai data din da ta yi mata saura. Tayi tsaki sannan ta sauka daga kan gadon Nabila inda take kwance ta wuce dakin Mommy.

A parlor ta sami Mommy tana zaune tana kallon tafsiri a tashar Sunnah TV, ta zauna a kusa da ita bayan tayi sallama ta amsa. Sai da suka dan yi jim kadan ta kula dai Mommy babu abinda zata ce mata sannan tace ‘Mommy don Allah ki dan saka min 1k a waya mana.’
Ta kalleta tana dariya tace ‘1k kuma? Ina Mustaphan ko kuma yau ba nashi kike so ba tunda kina gidana nawa kike so?’

Itama dariyar tayi ta kara langabe kai ‘A’a Mommy, don Allah dai ki taimaka, wallahi ya saka min kararwa nayi kuma dai kin san bani da kudi.’

‘Ke kenan kullum baki da kudi?’

‘Mommy bari dai na fara aiki.’

‘Uhm, shi Mustaphan ko dan na kashewa baya yaga miki balle gaki ‘yar makaranta?’

Ta dan marairaice ‘To ai kin ga yanzu anyi hutu Mommy, duk ‘yan sauran canjin ma na kashe.’

‘Shi yasa kike maula kuma? To dauko min wayata a daki na saka miki a cikin wanda mijina ya bani.’

Ta mike tana dariya tace ‘Mommy.’
PAGE 72
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)

Baffanta ba wai millionaire bane amma dai ta san yana da kyauta; duk da Mommy tana sayar da ‘yan kunnaye da sarkoki amma duk wata sai ya tura mata kudin kashewa account dinta sai dai ko ya tura babu yawa amma fa sai ya tura. Kuma idan dai ta bukaci wani abu bayan wannan to yana iya bakin kokarinsa wajen ganin yayi mata sai dai ko idan babu hali.

Tayi zaton haka zata je ta samu a wajen Mustapha, musamman da yake yana yawan yi mata kyaututtuka da saka credit a waya laokacin da yana neman aurenta. Sai dai bayan ta shiga gidan sai ta tarar ba haka bane; don wani lokacin a kan ya saka mata kati a waya ya gwammace ya bata aron wayarsa tayi waya. Ko da ta koma makaranta ma tayi zaton zai dan dinga bata kudin makaranta da kudin kashewa sai dai tun a ranar farko da gane ba zai jure ba. Domin da farko bayan ta gama shiryawa tayi zaton zai kaita ne, amma sai dai suna fitowa da aka zo inda zai dauke hanya ya wuce office dinsu sai yace ta sauka a nan ta hau motar haya. Da tayi maganar kudin mota kuma sai yace mata wai ya zata tana da kudi; ta dai samu ya bata naira dubu kamar ba da son ranshi ba. Tun daga ranar ma sai ya zama ta daina damuwa tayi saui ta shirya ta bishi, yawanci sai ta jira idan ya fita sai ta kama hanya a motar haya. Kudin motar ma tana shirin ta tambayi Baffa ya dinga bata aka shiga lockdown; kuma har yanzu tana da niyyar kafin ta koma gida ta sanar da Baffanta kawai ya dinga tura mata kudin mota. Tana ta wannan tunanin taje ta dauko wayar ta kawowa Momy; ba tare da bata lokaci ba ta tura mara katin naira dubu kamar yanda ta bukata.

Nan da nan ta koma daki ta sake hayewa kan gadon Nabila sannan ta danna masa kira.

Sai da wayar ta kusa tsinkewa sannan ya dauka, cike da isa yana magana da kyar ya amsa sallamarta, haka ma gaisuwarta kamar ba zai amsa ba. Wannan ya sa jikinta yayi sanyi kuzarin da ta fara wayar da shi duk ya gushe.
Cikin sanyi murya tace ‘Babe, ya na jika haka? Ko baka da lafiya ne?’

Sai da ya dan yi jinkiri sannan ya amsa ‘Umm, lafiyata kalau. Ke kin damu da lafiyata ne da kike wannan tambayar? Ba dole ki jini haka ba tunda kin zabi ki nesanta kanki da ni?’
PAGE 73
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)

Nan ta fahimci inda zancen ya dosa, amma da yake so take ta waske sai tace ‘Haba Babe ya za ayi na gujeka? Tunda fa kuka tafi daga nan nake ta yi maka message ta whatsapp, baka gani bane? Kuma wallahi wayar ma ka san bani da credit, yanzun ma da kyar na samu Mommy ta saka min dari biyu shine nake kiranka fa. Haba Babe ya za ayi kace ban damu da kai ba?’

‘To idan kin damu dani ya za ayi nazo har gidanku ga azumi kin sani kuma gashi ana lockdown? amma kina kallonmu ni da yarana duk muna ta murna zaki dawo amma kika ce ba zaki dawo ba sai bayan sallah.’

‘To ai na gaya maka wannan ba ni na tsara haka ba, Mommy ce. Kuma ka san dai idan mace ta haihu dai ana yin gyara da sauransu, sallar nana fa kuma saura bai fi kwana goma sha shida ba. Haba Babe to meye na fushin?’

Shiru yayi ba tare da yace mata komai ba suna sauraren numfashin juna. Itace ta gaji da sauraro tace ‘Ya naji shiru ne? ina yara na?’

‘Ai baki damu da su ba shi yasa sunata cewa ki biyosu kika ki.’

Ta fara gajiya da wannan mitar tsa da duk abinda tace sai ya ce bata damu da su ba shi da ‘yayansa, to wai ita ba ta bukatar a damu da ita ne ko me yake nufi? Shi ba zai iya kula da ita ba kuma ya barta ma cikin natsuwa a inda za a kula da ita ta dan sami natsuwa yana nema ya hana? Ta dan yi murmushi mai sauti ta danne fushinta sannan ta saita muryarta tace ‘To don Allah kayi hakuri ka daina cewa ban damu da ku ba, kai ka san na damu daku. Kamar tau ne zaka ga lokacin yayi ai na dawo, ko ba shikenan ba.’

‘Umm, amma dai da zaki dawo yanzu ai da ya fi ko? Haka kawai ni ba gwauro ba kin saka ni azumi babu mata. Kawai idan an bude gari na zo na dauke ki mu tafi, shine kawai zan san kin damu da ni.’

Ta dan daga murya tace ‘Ah, Babe to me zan cewa Mommy, ni dadi miji zan bi mijina kenana ko me?’

‘Ba wani dadi miji, ai aurene kuma itama ta sani.”

‘To gaskiya dai ka bari sai bayan sallar kawai.’

Haka dai suka dauki lokaci suna waya ba tare da ta amince zata dawo din ba, maimaita mas kawai take sai bayan sallar. Don haka kusan a fusace ya katse wayar ba tare da sun yi wata sallamar kirki ba.
PAGE 74
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)

Ta jefa wayar a kan gadon kusa da ita ta ja tsaki, sai kuma ta kifa kanta a kan pillow sai hawaye. Ta godewa Allah nabila tana dakin Mommy tana bacci da sai ta gayawa Mommy tana kuka. Ta fara nadamar sakawa da tayi Mommy tace ta zauna a gida har bayan sallah, yanzu gashi yana fushi da ita. Ita bata zata wannan abun zai sa yayi fushi ba don da ta san zai yi fushi ma da ko gidan ba zata taho ba zata hakura yaje ya daukota. Bata sani ba ko zata iya jure jinsa a cikin damuwa har na tsawon sati biyu ko uku, amma dai zata gwada. Don da kunya tace a barta sai bayan sallah sannan yanzu kuma ta zo tace zata koma.

Haka ta karasa wunin ranar cike da damuwa da nadamar zaman da ta zaba zata yi a gida.

Haka ta cigaba da hakuri tana buga masa waya wanda kullum idan ta buga gaisawa kawai suke yi babu wata magana mai dadi, kamar ma shi dole take masa. Abun yana matukar damunta don haka ta fara rama wadda Mommy ta zata don ta cigaba da azumi ne tunda ta sami lafiya; idan tayi zuru-zuru aka yi magana sai tace azumin ne da wahala.

____
Tun da ya kaisu gidan Hajia bai sake zuwa ba tunda garin a rufe yake ba a fita, sai yau asabar a lokacin saura sati daya sallah.

Yana fita ya tsaya a shagon telansa ya karbar musu dunkunan kayan sallansu wanda tun kafin a fara azumi ya kai; wanda harda na Khadeeja a ciki, ya tsaya aka bashi leda ya ware nata wadanda bashi da niyyar kai mata gidansu. Ya dai yarda zai ajiye mata a dakinta duk lokacin da ta dawo ta gani.

Yana karba kai tsaye ya wuce gidan Hajia cike da kewar yaransa.

Tun daga nesa ya hango Habib a zaune a kofar gida tare da wani yaro, ba wasa sukeyi ba a zaune suke kawai sun yi shiru kowa da abinda ya dameshi. Kafin ya karasa tsayar da motar ya taso da fara’arsa; ya gyara tsayuwar motar ya bude kofa yana sake karewa Habib din kallo wanda ya yi zuru-zuru kamar wanda ya kwana da yunwa.

‘Abba sannu da zuwa.’ Muryar Habib ta katseshi.

‘Yauwa Habib, ya naganka kamar kana jin yunwa ko azumi kake ya fara baka wahala tun da safe haka?’

Idonsa ya dan yi rau-rau yace ‘Eh, azumi nakeyi.’

‘To baka yi sahur bane?’
PAGE 75
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)

‘Ba sosai ba, bakin tuwo ne kuma bana ci gashi kuma babu wani abincin a gidan sai shi, na dan ci kadan dai.’

‘To ba sai ka fasa yin azumin ba? da safe kayi breakfast.’
‘Hajia ma haka tace na fasa yin azumin amma ni nace zan yi, idan ma ban yi ba ba abinci zan samu ba sai an sha ruwa. Tunda muka zo ma sau daya na sha azumi.’

Cike da tsananin mamaki yace ‘Ban gane ba abincin kake samu ba sai kace wani almajiri? Ba a baka abinci ne a gidan? Ina baito?’

‘Ai Baito sai da rana take zuwa, kuma safiya tana yi Hajia take cewa mu tafi gidan Anti Jidda muyi wanka a can muci abinci a can. Kuma idan mun je sai Anti Jiddan tace babu abinci sai dai kawi wata ran ta bamu bakin shayi da ragowar kosai ko doya. Idan kuma mutum ya dameta sai ta yi masa fada, itama Shukra da Nasreen ragowar kunu ne kawai ko kuma idan an yi sa a an rage abincin shan ruwa shine ake basu.’

Mamakinsa ya karu, yace ‘A’a, ai na turowa Anti Jidda kudi a sayi indomie da cornflakes harda madara, ba a siya ba ko me ya faru da su.’

Ya dan zaro ido ‘Tab, tunda muka zo bamu taba cin indomie ba ko cornfalkes. In an sha ruwa dai da yake muna gidan hjia shine aka hada mana shayi da madara harda kwai ma ake soya mana da kaza, amma dai da rana babu wanda yake bamu abinci. A wajen Hajia ma muke shan ruwa tare da ita da Alhaji.’

Yayi matukar mamaki kuma ya ji tausayin Habib; amma kuma yana matukar mamakin yanda za ayi ace Yaya Jidda ta bar masa yara da yunwa. Ranar da ya kawosu bayan ya tafi ta kirawoshi tana tambayarsa kudi a sayi kayan shayi da indomie, kua a take ya tura mata naira dubu goma don a siyo da wuri. To me ya faru da kudin da ake hora masa yara da yunwa?

Tare suka jero da Habib din suka nufi cikin gidan, suna daf da shiga suka ci karo da Afaf tare da Shukra da Nasreen kowacce sanye da hijabinta, nan da nan suka fada jikinsa suna murna ‘Abba, Abba.’

Bayan ya amsa gaisuwarsu yace ‘Ina zaku je?’

Afaf tace ‘Gidan Anti Jidda zamu je suyi breakfast.’

‘Ke kina azumin ne?’

‘Eh ina yi.’

‘To ku zo mu wuce ciki kuyi breakfast din a nan.’
PAGE 76
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)

Nasreen tayi dariya tace ‘Tab ai babu abincin, da an gama shan ruwa Baito take juye duk wani ragowar abinci ta tafi da shi. Kuma Hajia cewa take muje gidan Anti Jidda a dafa mana indomie amma idan mun je ba a dafa bana, bakin shayi ake bamu da ragowar kosai ko kunu.’

Ya dauki shukra ya ja hannun Nasreen yana cewa ‘ku zo muje.’
Bayan sun gaisa da Hajia tace ‘To ka barsu suje gidan Jidda ta dafa musu indomie din su karya sai su dawo ko? Yunwa suke ji gasu nan.’

Nan suka yiwa Hajia bayanin abinda ake basu idan suka je gidan yaya jidda; itama tayi mamaki sosai. Tace ‘To me yasa baku taba fada ba?’

Nasreen ta zumburo baki tace ‘Yaya Meena ce tace duk wanda ya fada sai taci ubansa ta karta masa rashin mutunci don ta san mu da tsinin baki.’

Daga Hajiyan har Mustaphan mamaki ne ya kamasu, Meena itace babbar ‘yar Yaya Jidda. To amma me zai sa tayi haka bayan Jiddan da kanta ta gayawa Hajia ya turo kudin indomie da kayan karin kumallon yaran?

Tace ‘Lallai daga Aminan har Jiddan zasu zo su sameni.’

Saboda tsabar takaici Mustapha kasa magana yayi. A nan ya sake bada kudi Habib ya fita kanti ya siyo musu indomie, yana kawowa Afaf ta dafa musu da kwai tunda dama da akwai kwai a gidan. Haka ya saka su a gaba duka saida suka karya azumin suka ci suka koshi.

Nan ya zauna suka cigaba da hira wajen Hajia tunda shima Alhaji ya fice; sai dai har la’asar ta kawo jiki Yaya Jidda bata zo gidan ba saboda yaronta Abdallah ya shigo gidan lokacin suna cin indomie shima ya zauna aka ci da shi kuma yana gamawa ya koma gida ya gayawa uwarsu Abban Afaf ya zo harma ya saan dafa musu indomie da kwai. Don haka tana sanetaki zuwa saboda rashin gaskiya.

Haka ya wuni a gidan ransa a bace yana tunanin mafita; tabbas duk Khadeeja ce ta janyo masa wannan wulakancin. Tunda da ta dawo babu wanda zai yi wa yaransa wannan wulakancin, Kuma shi ya tabbatar ta sami lafiya ko daga ganinta ma ai an San kalau take
PAGE 77
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)

To yanzu ya zai yi da yaran? Idan ya tafi dasu ba zasu barshi ya zauna a nutse ba, kuma ma ya san Hajia ba zata yarda ya tafi dasu gida su zauna tare da shi ba. Sai dai kamar yanda ta riga ta fada yaje ya siyo abubuwan da suke bukata ya kawo ita sai ta dinga dafa musu kafin Baito ta zo; domin itama Baito din mijinta ne bashi da lafiya take jinyarsa shi yasa ba zata iya zuwa da safe ba.

La’asar tana matsowa ranshi ya sake baci, kuma har loakcin Yaya Jidda bata iso ba. Bayan ya idar da sallar la’asar yana zaune a kan dadduma yana tunanin mafita Habib ya shigo ya sameshi. Bai dade da zama ba yace ‘Abba da ma ka kaimu gidan Mama, ka ga dama mun dade bamu je ba tunda muka koma gida.’

‘Um, to ai da sallah zaku je ko? Ko ba kwa son zama a nan din ne? ai ka ga yanzu Hajia da kanta zata dinga baku breakfast din ko?’

‘Um, nan din ma muna son zama amma can din ma muna so, in ya so idan Anti Khadeeja ta dawo sai mu dawo.’

Nan sauran yaran suka shigo suka saka shi a gaba a kan su gidan Mama suke so suje; shi din ma yana so ya kaisu don ya san ba za a barsu da yunwa a can ba tunda ko babu mai aiki akwai ‘yan mata. To amma yanzu hakan yana nufin kenan ba za a iya rike masa yaransa a gidansu ba ko me? Ita kuma Yaya Jidda me take nufi? Gashi taki zuwa, shi kuma ba zai je gidanta ba don ya fi so tazo suyi a gaban Hajia. Haka dai yaran nan suka saka shi a gaba dole ya amsa zai wuce da su. Itama Hajia da ya gaya mata zai kaisu sai da ta nuna bacin ranta don gani take kamar fushi yayi da yanda ya sami yaran, sai da Alhaji ya sa baki kuma suka ga nasreen tana nema ta saka musu kuka sannan suka bari ya kwashi yaran suka wuce gidan Maman su Ma’u.
PAGE 78
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)

Duk da bai ce mata zai zo yau din ba amma dai haka kawai zuciyarta take gaya mata zai zo tunda an bude gari kuma tun wancan lokacin da aka bude gari basu hadu ba. Ta san dai yana jin haushinta daga yanda yake amsa wayarta amma ta nutsu a zuciyarta cewa zai zo din. Tun wuri ta tashi tayi wanka ta shirya don ya sameta a shirye; sai dai ga mamakinta har azahar tana zaune a parlor tana ta faman duba waya, duk wanda ya buga gate da hanzari take tashi ta bude tana saka rai Mustapha ne amma har la’asar bai zo ba.

Dab da la’asar tana zaune a parlor tana ta faman latsa waya tana duba whatsapp ko ya bude sakon da ta tura masa amma ga mamakinta har zuwa lokacin bai bude ba. Mommy ce ta fito daga dakinta; har ta kama hanyar kitchen sai kuma ta kula da Khadeeja a zaune a parlor din. Ta dawo ta tsaya tace ‘Ya na ganki a nan, ina Nabila PA din taki?’

Tayi dariya tace ‘Tana can tana abinda ta saba wato bacci.’

Ta wuce kitchen ta barta a nan, jimawa kadan ta fito ta dawo parlor din ta zauna a kan three seater daga bangareb da yafi kusa da single seater din ta Khadeeja take zaune. Ta dan yi gyaran murya tace ‘Uhm, ai na zata Mustapha zai zo yau din, ko sai da yamma zai zo?’

Ta dan gyara zama tace ‘Umm! Ina jin dai sai da yamman, watakila gidansu ya wuce tunda shi da yara ne.’

‘Um to bari mu gani. Amma dai kuna waya ko?’

‘Eh, jiya da daddare ma munyi magana.’

‘Ai shikenan bari mu gani.’

Suka yi shiru na dan lokaci; jimawa kadan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login