Showing 45001 words to 48000 words out of 95984 words
a gidan nasu.
Bayan sun gama gaisawa da Baffan tace ‘A’a Baffa, ina nan ne muna shirin makaranta ni da yara.’
Daga daya bangaren Baffa yace ‘Karfe nawa ne lecture din naki Dije?’
Tace ‘Karfe takwas.’
‘Idan nazo 7:30am ai kin gama shiryawa ko?’
‘Eh Baffa.’
‘To ki shirya idan na karaso zan yi miki waya ki fito na kaiki makarantar sai na wuce office.’
Cike da girmamawa kamar wadda zata tsuguna a wajen tace ‘To Baffa na gode, Allah ya kara lafiya.’
Ta ajiye wayar bayan ya amsa, kafin tayi wani abu Mustapha yace ‘Lafiya kalau dai naga Baffa yana kiranki da safe.’
Ta mikawa Habib shayinsa da ta hada masa tana cewa ‘Uhm zai zo ya kaini school ne shine yake tambayata karfe nawa zai zo.’
Habib ya karbi shayinsa ya fice yayinda Mustaphan ya matsa kusa da ita cike da kulawa da damuwa yana cewa ‘Makaranta kuma? Ba nace zan dinga kai ki ba? Yanzu ke saboda rashin tausayi sai ki taso shi da wannan safiyar kawai don ya kai ki makaranta? Ke abu ba zai wuce a wajenki ba?’
Ta juya cikin halin ko in kula tana cewa ‘Shine ya karbi timetable dina yace zai dinga zuwa yana kaini ko? Ai a gabanka ya fada.’
‘Kuma a gabanki na bashi hakuri ai; wannan wanne kalar abin kunya ne ina nan kuma ina da abin hawa amma zaki taso Baffa ya zo ya kai ki makarnta don Allah?’
Daryace take son ta kwace mata saboda yanda duk ya muzanta kamar ma Baffa yana tsaye yana kallonsa. Kafin ta bashi amsa ya dauki wayar tata ya dannawa Baffa kira ya mika mata waya yana cewa ‘ki gaya masa zan kai ki ba sai kin yi min wulkanci ba.’
Kafin tayi magana har Baffan ya dauka, don haka ta kara a kunnenta tace ‘Um Baffa ka bari ma Abban Afaf zai kai ni makarantar.’
Yace ‘Ah, kin tabbata dai ko?’
‘Eh Baffa, gasu ma tare zamu fita gaba daya shiryawa muke.’
Ya zare wayar daga hannunta kafin ta sake magana ya kara a kunnensa cike da girmamawa yace ‘Baffa zamu tafi tare in sha Allahu, zan dinga kaita. A yi hakuri.’
PAGE 118
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid
Yace ‘To, to babu laifi. Allah yayi muku albarka.’
Ya ajiye wayar yana harararta yana cewa ‘Yanzu zan je na shirya, kema ki shirya sai mu fita gaba daya ko kuma idan na kaisu sai na dawo kafin nan kin karasa sai mu wuce.’
Tace ‘Um, ka ga babu komai fa, zaku iya tafiya ma sai na wuce kawai ba sai na gayawa Baffan ba.’
Ya kakkafeta da ido yana harararta har sai da ta sunkuyar da nata idanun, ya juya yana cewa ‘Ki shirya nace.’
Ya fice ya barta a nan.
Tayi dariya ta cigaba da aikinta.
Bata da zabi haka ta shirya suka fita tare, kuma daga wannan lokacin ya zama ko da wanne lokaci zata makaranta haka yake barin abinda yakeyi ya zo ya kaita. Sai dai idan ta gama abinda takeyi kawai sai ta hawo motar haya ta dawo.
.......
A zaune yake a parlor din Ahaji, yayinda Hajia take zaune a kusa da Alhajin. Zuwa yayi musu da labrin auren yana son ya kara don har ma yana gaya musu sati me zuwa yake so aje a kai kudin aure.
Cikin walwala Alhaji yace ‘Ai kwanaki da mukayi magana da kai da na jika shiru na zata ka fasa.’
Yayi ‘yar dariya ‘Ba fasawa nayi ba Alhaji, na dai dan tsaya ne na kara shiryawa, na gaya maka zan sayi gida ai. To dama tsayawa nayi a samo gidan, kuma yanzu an samo, cinikin ne ma bai fada ba saboda ina so su dan yi min ragi. Amma in sha Allahu ina sa ran zamu daidaita shi yasa nake son yanzu a kai kudin auren.’
Murmushin Alhaji ya kara fadi, ya dubi Hajia sannan ya dubi Mustapha yace ‘To ma sha Allahu. Wannan ai sai dai mu sa albarka kawai. Kaje ka sami babanka Safiyanu kayi masa bayanin ita yarinyar idan ya gama bincikensa ya tabbatar gidan mutunci ne ai sai suje su kai kudin. Allah ya sa albarka, Allah ya kara budi.’
Suka hada baki shi da Hajia suka ce ‘Amin.’
Hajia tace ‘To ka gayawa Khadeejan ko? Me tace?’
Ya shafa kai yana murmushi ‘Ban gaya mata ba tukunna, amma in sha Allahu zan gaya mata. So nake sai an gama magana tukunna idan ya zama saura kamar sati uku ko hudu sai na gaya mata ko don saboda gudun fitina. Kafin nan na siya gidan mun koma.’
Alhaji yace ‘Eh, to hakan ma yayi. Sai dai kuma Allah ya sa kada mata su rigaka gaya mata.’
PAGE 119
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Hajia tace ‘A’a babu wanda zai gaya mata, kayi abinka a hankali idan ka shirya ka gaya mata.’
Nan suka kare hirarrakinsu daga baya yayi musu sallama ya kama hanya.
……….
Abu daya ne yake ciwa Khadeeja tuwo a kwarya rashin haihuwa, domin har yanzu tun bayan cikin da ta samu ya bare bata sake ko da batan wata ba. Gashi yanzu har sun shiga final year amma babu wani labari. Duk lokacin da tayi yunkurin zuwa asibiti Mustapha sai ya nuna halim ko in kula ko kuma yace lafiyarta kalau zata je ta fara neman fitna, don haka ta tattara ta hakura. Sai dai ta yanke kanta hukuncin cewa da zarar ta gama final exam zata je asibiti a dubata a tabbatar mata da abinda ya hanata samun ciki; ko babu komai itama tana so taga ta haifi dan cikinta. Tunda idan ta gama karatu bata san lokacin da zata sami aiki ba.
Haka ta hakura ta mayar da hankali a kan karatunta tana addu’a.
Zamanta da yaran Mustapha kadai ya isa ya sa ta ji tana son haihuwa; domin yanzu yaran sun girma tunda Shukra auta ma tana primary 1 yayinda Afaf take SS. Kusan gaba daya yaran yanzu ba dadinsu take ji ba, domin abinda suka ga dama sukeyi. Habib ne ma kawai wanda ya damu da rayuwarta kuma yake neman shawara a wajenta kamar uwa, amma Afaf da Nasreen ma bata san wanene yake basu shawara ba. Ta dai san duk wani abu na wulakanci da sukeyi mata da sa hannun Yaya Jidda. Ga wani mahimmanci da Musttapha yake bawa Afafa ta yanda ko da sun gama magana da Khadeejan Afaf tana iya saka shi ya canza. Duk abinda ya shafi yaran kuma ko da Khadeeja ce ta gaya masa to a karshe da Afafa din zai yi shawara. Hatta kitchen din gidan ya zama kamar na mata biyu; domin a lokuta da damam sai ta gama girka abinda kowa zai ci ta fita daga kitchen din sai Afaf ta shiga itama ta dafa abinda ta ga dama tace bata cin wanda Khadeejan ta dafa. Tayi magana har ta gaji, tunda Mustaphan ya fara nuna tana so ta takurawa Afaf ne saboda ba ita ta haifeta ba.
………
Tana kwance a dakinta tana jiyo hayaniyar yaran a parlor; Afaf ta shigo ta sameta ta mika mata waya tana cewa ‘Anti Abba ne yake waya yace yana kiran wayarki bata shiga.’
PAGE 120
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Ta tashi zaune ta karba ta dan kalli wayar taga whatsapp call ne, sannan ta kara a kunnenta.
Yace ‘Ina kika shiga ne anke kiran wayarki ana ta cewa not reachable?’
Tayi yar dariya tace ‘Sai dai ko idan network ne don ga wayar ma a hannuna.’
‘Kin san Ali Ahmed ko? Abokina da muke zuwa zance tare.’
‘Eh na san shi mana.’
‘Yauwa da Allah shine ya shigo gari nan da kamar awa daya zamu zo gidan, me zaki iya dafa masa sai muyi dinner tare. Yana dai son tuwo’
‘Ok, to sai ayi tuwon ai. Amma dai ka bari na duba freezer tukunna naga yawan kazarmu yada za samu kuma ayi muku peppersoup ko?’
‘Eh, kwarai kuwa da zobo ma please. Duba idan babu kazar sai na bayar a kawo miki yanzu, rike wayar ki duba ki bani amsa.’
Ta mike ta dubi Afaf da take tsaye tana jiran wayarta ta nufi kitchen. Suna fitowa parlor Afaf din taga Nasreen ta canza channel ta mayar Disney Junior, da sauri tayi kanta tana cewa ‘Wane mara kunyan ne ya canza min channel ban gama kallo. Anti idan kin gama wayar ina nan.’
Ta shige kitceh ta barsu.
Tana shiga ta karasa ta bude freezer ta duba sannan ta ce masa ‘Zata isa ma, amma dai idan zaka dawo sai ka siyo wata don gaba daya zan kwashe na dafa muku yanzun.’
Suka yi sallama ta katse wayar.
Sunan da ta gani a jerin chats din kan wayar shi ya ja hankalinta ta fasa fitowa daga kitchen din tana karewa sunan kallo; Anti Naja aka rubuta da alamar zuciya ta emoji. Daga haka da take kallon hoton da yake kan sunan kuma tabbas Naja ce sakatariyar Abbansu. Ba tare da tayi wani tunani ba ta danna kan sunan ya bude mata chats din, har zata yi sama sai kuma wani sako da yake cikin jerin sakunan dake kasa ya ja hankalinta. Afaf ce ta turawa Naja sakon kamar haka
“Congrats Anti, Abba ya ce min an kawo kudin auren ko?”
“Eh my girl, sun kawo harda sadaki ma. Saura kawai ya gama gyaran sabon gida mu shikenan.”
“I can’t wait to have you here with us Anti.”
“Soon my girl. Amma dai ta daina baki matsala ko?”
“Ta daina, tunda ta ga babu riba. Yanzu ba sosai ma take kulani ba dama ni haka nake so. Habib ne kawai sarkin rawar kai ya manne mata.”
PAGE 121
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
“Kada ki damu kwanan nan zan zo na gyara mata zama.”
Motsin da Khadeejan ta jiyo ne ya sa tayi sauri ta rufe sakinnin ta dire wayar a kan teburin da yake kusa da freezer din ta kama murfin freezer din ta daga kamar a lokacin ta rufe.
‘Anti ina wayar?’ Afaf ta fada bayan da ta karasa shigowa kitchen din.
‘Kin ganta nan a kan tebur, dauki.’
Ta karasa ta dauki wayarta ta fice ta koma parlor din.
Cikin sanyin jiki Khadeeja ta tsaya a ta jigina da freezer din ta kafa tagumi. Kusan wata takwas da suka wuce Mustapha ya kalli tsabar idon Baffa da Mommy yace musu ba auren Naja zai yi ba, amma gashi daga wadannan chats din da ta karanta yanzu har an kai kudin aure da sadaki. Wato ma Afaf ta san komai itace kawai bata san mijinta zai kara aure ba kenan; kuma kamar dai bashi ma da niyyar gaya mata. To me ta yiwa Mustapha ne? me yake tunanin zata yi a akna kara aurensa da yake boye mata? Ita dama da ya kai ta gidan da ya siya yanda taga gidan ta san sai ya kara aure, kawai dai bata zata Naja zai auro ba don kwata-kwata bata sake ganin wata alama da take nuna yana tare da Naja ba tun bayan da suka je wajen Baffa. Wato dama da take zargin Yaya Jidda ce take hure mata kunnen yara ashe Naja ce, tunda gashi nan ta gani har tana gayawa Afaf cewa zata shigo ta gyara mata zama. Ta jijjiga kai, ta goge gumin da ya fara tsattsafowa daga goshinta sannan ta tuna ce mata fa yayi nan da awa daya zasu zo.
Jikinta a sanyaye ta koma cikin gidan ta kirawo Rashida sannan suka fito suka kama aiki. Haka ta hadiye duk wani bacin rai tayi ta haba-haba da abokinsa, sai bayan sallar isha’i sannan yayi musu sallama ya tafi.
Ta san cewa ya kula da yanayinta yanda ya sauya, amma bai yi mata magana ba. Duk da dai ko da yayi mata maganar ma zata gaya masa gajiya ce kawai. Haka dai suka kwana shi yana baccinsa ita kuma Khadeeja duk lokacin da tayi juyi sai ta kalleshi tana tambayar kanta wai me tayi masa ne yake mata abubuwa kamar wata wadda aka aura ba don soyayya ba?
Haka ta hakura tayi ta danne zuciyarta har gari ya waye
PAGE 122
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Sai karfe biyu na rana take da lecture amma haka ta shirya da wuri lokacin da Mustapha ya shirya zai tafi office tace ya wuce da ita ya kaita gidan Mommy, in ya so daga can sai ta wuce makarantar ta kuma dawo gida. Haka kuwa aka yi.
Tunda ta shiga gidan Mommy ta karanta damuwa a fuskarta, ta dai kyaleta har Baffa da Nabila suka gama shirinsu suka fice. A nan parlor din inda suka barsu Mommy ta zuba mata ido na dan lokaci, har ta ji a jikinta Mommy din kallonta take. Tana juyowa kuwa suka hada ido; ta danyi dariya tace ‘Mommyy.’
Itama tayi dariyar tace ‘Ya aka yi ne? kamar dai kina da damuwa. Ko kuma ba kya jin dadi ne?’
Ta jijjiga kai tace ‘Mommy Mustapha aure zai yi.’
Ta dan zaro ido ‘Aure? Ikon Allah.’ Sai kuma ta saki fuskarta ta cigaba ‘Ko da yake wannan ba abin mamaki bane ai don haka kada ma ki sakawa kanki damuwa.’
Ta sunkuyar da kai cikin damuwa tace ‘Mommy nima ba damuwa nayi ba, kawai dai yayanyin abun ne.’
‘Ban gane ba.’
Nan ta sanar da ita wadda zai aura sannan ta sanar da ita a inda taga labarin auren da kuma irin sakonnin da Afaf take turawa Najan da kuma yanda take fama da Afaf din a ‘yan kwanakin nan.
Duk da Mommy bata yi mamaki ba amma dai ta ji babu dadi, musamman yanda Afaf ta zama ‘yar rahoton Naja. Tace ‘Ikon Allah, to shi me yasa yake boye miki auren?’
Tace ‘Wallahi ban sani ba, ko da wasa bai taba gaya min ba kuma danginsa ma babu wanda ya gaya min. Amma kin ga yaran har sun sani, tunda gashi har ana gaya musu za a zo a gyara min zama.’
‘Lallai mutum sai a barshi.’
‘Dama na gaya miki Mommy tunda naga gidan da ya saya nace miki gidan nan ba na mace daya bane, kin ga maganata ta tabbata.’
Sukayi shiru na dan lokaci, jimawa kadan Mommy tace ‘To da ce mata aka yi baki zauna daidai ba da take cewa zata gyara miki zama ko me? Amma kafin ta gyara miki zama ke ce zaki bi dare ki gyara zama ta hanyar addu’a, idan gari ya waye kuma ki dora da sadaka.’
PAGE 123
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Ta sunkuyar da kai tana koakrin boye kwallar da ta gangaro a kwarmin idonta; wannan kalmar ta za a gyara mata zama ta tsaya mata a rai. Domin dai kalma ce da zata iya daukan kowacce ma’ana. Amma kamar yanda Mommy ta fada hakan zata yi tunda ta san bata da gatan da ya wuce Allah.
Haka suka cigaba da hira Mommy tana ta bata baki kuma tana yi mata alkawarin daga nan ma zata dinga yi mata addu’a kuma da sadaka, ta tabbatar mata ba za tayi nasara a kanta ba.
Da wuri Mommy ta sauke abinci saboda Khadija taci kafin ta tafi makaranta, tana daga kitchen din ta kwalawa Khadeejan kira. Tana shiga kitchen din ta fara gatsina fuska tana cewa ‘Mommy wannan wane irin kifi ne kika dafa me azabar karni? Allah ya sa dai ba da shi kika yi abincin ba.’
Mommy ta kare mata kallo na dan lokaci sannan tace ‘Wane kifi da aka dafa tun jiya da daddare aka cinye, ni shinkafa da wake ma na dafa.’
Nana da nan fara’arta ta karu, ta dauki plate ta matsa tana mikawa Mommy tana cewa ‘Yauwa Mommy zuba min na fice don wallahi kitchen din nan karni yake.’
Ta karbi plate din tana cewa ‘Cikine da ke ko?’
Ta kalli Mommy da baki a bude, suka dan zubawa juna ido sannan ta rufe bakin tace ‘Anya kuwa Mommy, tunda dai ni ban ji wani sauyi na azo a gani ba.’
Ta zuba mata abincin ta mika mata tana cewa ‘To ki dai bincika tukunna kafin kiyi saurin cewa a’a, don tunda kika shigo nake kula da ke gaba daya ma na dauka abinda ya kawo ki kenan.’
‘To ban sani ba gaskiya Mommy, amma zan duba yau din nan kuwa.’
Bayan ta gama cin abincin tayi sallah sanna ta fice ta kama hanyar makaranta. Sai da ta tsaya a chemist ta sayi abun pregnacy test sannan ta wuce. Ta riga ta san su Rahma suna jiranta a hostel don haka kai tsaye can ta wuce, tana ajiye jakarta a dakin ta fice ta fada toilet. Tana tsoma abin nan a fitsarinta ya nuna radau positive; wato tana dauke da ciki. Tayi murmushi tana ji kamar ta daka tsalle saboda murna, nan da nan idonta suka ciko da kwalla saboda jin dadi. A take kuma jikinta yayi sanyi da ta tuna cewa Mustapha ne yayi mata ciki kuma shine yake shirin auro matar da ta ke ikirarin zata shigo ta gyara mata zama.
PAGE 124
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Ta sunkuyar da kai ta saki takardar a kasa sannan ta fito daga bandakin cike da damuwa.
Yanayin da ta shiga dakin ya tabbatar musu da akwai matsala, don haka tun kafin ta Zauna farida ta mike ta tareta tana cewa ‘Ya na ganki haka, lafiya dai ko?’
Ta zauna a kan gado Rahma kamar wadda aka jefa, ta kalli farida suka hada ido sannan ta saki murmushe wanda yake hade da takaici tace ‘I am pregnant Farida.’
Nan da nan su Rahma da Amina da ke zaune suka dako tsalle suka fada jikinta sun ihu. Sai da suka fahimci ita bata taya su ihun kamar yanda suka saba sannan suka tsaya suna kallonta.
‘Girl, wannan ai abun murna ne na ga kamar ke baki ni dadi ba.’ Amina ta fada tana rike da hannun Khadeejan.
Ta sunkuyar da kai ta zare hannunta ta goge kwallar da ta fado daga idanunta. Ta basu labarin auren Mustapha da kuma abinda ta gani da ma yanda yake boye mata.
Tace ‘Ban ma san wanne zan yi ba; murna ko bakin ciki? Ni da za a zo a gyarawa zama ina zan mike kafa na fara haihuwa; haihuwar da ni ban ma tabbatar zai yi murna da ita ba. A yanzu ma gaba daya kai na ya kulle. Mommy dai tace kada na kuskura nayi masa maganar kara aurensa, na barshi har sai ya zo da kansa ya ya gaya min, a lokacin sai ayi duk