Showing 57001 words to 60000 words out of 95984 words
kuma gashi can na ajiywmata ita bakuwar tawa, ina ga kamar ai dafa ruwan zafi bai kamata ya zama matsala ba ga wanda aka bawa burodi ko?’
Ya bata rai saboda kwat-kwata bai zata haka ba; a iya saninsa sai sun kwana bakwai da amarya Khadeeja tana yi musu girki sannan sai araba kwana amma gashi tana nema ta kawo masa raini. ‘Ba fa na son raini Khadeeja, duk wanda ya kara aure matarsa ta gidan itace take yiwa amarya girki har sai ta kwana bakwai amma zan zo ina miki magana kina min wani zancen banza. Ai ko bazawara na aura kin san ya kamata kiyi mata abinci na kwana uku balle budurwa.’
PAGE 148
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Ta kalleshi ta kawar da kai; babu yanda za ayi ta yiwa Naja girki sai dai duk abinda zai yi ya yi; ta tsani Naja ta tsani jin sunanta. Watakila da ace ya biyo ta hanyar da ta dace wajen sanar da ita zai kara aure da wadda zai aura da haushin da take ji bai kai haka ba, amma gaskiya babu abinda zai sa ta yiwa wata Naja girki. Ya auro matarsa ya gama more kwanan amarci sanna ita kuma bayan bacci da bata yi cikin nutsuwa ba kuma ita yake so ta tashi da sassafe ta hada musu breakfast na warware gajiya, bata taba ganin rainin hankali irin wannan ba. Ta bata rai sannan tace ‘Ba a biya mana wannan hadisin ba a islamiyya.’
Mamaki ya kamashi ya bude baki amma ya rasa abinda zai gaya mata. Yana kallo ta zame ta gyra kwanciyarta ta juya masa baya. Bai shirya da wannan mahaukacin taurin kan nata ba wanda idan ta fara shi sai duk garin kowa ya ji. Ya dan tausa muryarsa yace ‘Bana son wasa Khadeeja, don Allah ki tashi ki samarwa yarinyar nan abinci. Next week ai zaku raba girkin kowa ta dinga yin nata, amma for now ki tashi ki bamu breakfast.’
Ta sake gyara kwanciya ba tare da tace masa komai ba. Ya kalli kasa yana jijjiga kai don ya san ta gama magana; takaici ya kamashi. To yanzu ya za ayi tana amarya ya bata bread ruwan zafin ma ace sai ta dafa. Haka ya fice daga dakin yana wasi-wasi.
Yana ficewa ta juyo ta harari kofar kamar yana wajen ta ja dogon tsaki tace ‘Dan rainin hankali!’
………
Yana shiga ya tara da ita ta fito daga wanka tana shirywa. Tun kafin ya gama shiga dakin tace ‘Allah ya sa dai an gama abinci don wallahi yunwa nake ji kamar an min sata a ciki.’
‘Akwai dai bread, sai dai idan kin fito ki dafa ruwan zafi da kwai haka sai mu karya.’
Da mamaki ta kalleshi tana cewa ‘Ruwan zafin ma sai na dafa? Yau ne fa kwanana na farko a gidan, haba! Kitchen din ma ban san inda yake ba.’
Cikin damuwa yace ‘To ko order za a yiwo?’
‘Ni ban gane ba, wai ita matar gidan bata girki ne?’
PAGE 149
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Ya karasa kusa da ita yana kokarin kama dogon gashinta da take tajewa yana cewa ‘Ki bar wannan maganar, ki zo muje na nuna miki kitchen dinki sai ki samar mana ruwan zafi mu karya. Idan kuma akwai inda zaki iya yiwo mana order a kawo nan da awa daya haka to sai na tura kudin.’
Ta jijjiga kai ‘Gaskiya babu, sai dai ko na rana don wallahi kwana bakwai din nan sai na yi su ba tare da na dora tukunya ba. Don ni abinda na sani matar gida ko ‘yar gwal ce idan aka yi amarya ita take girki kafin a zauna a raba.
Haka yayi ta bata hakuri yana lallabata, daga karshe ta shirya suka sauko parlor dinta ta dafa musu ruwan zafi sanna ya debo kwai ta soya musu.
Wajen 12pm ya hadasu a parlor dinsa yayi musu introduction; ita naja amarya sai muzurai takeyi tana wata yanga, ita kuwa khadeeja cike da walwala tayi mata maraba suka gaisa babu laifi. Ya sanar da su idan an kwana bakwai zasu raba kwana kowacce kwana biyu.
Ba karamin mamakin Khadeeja yayi ba, ko da yake wannan ba bakon abu bane a wajensa. Tayi masa rashin kunya mintuna kadan kuma ta koma kamar ba ita ba. Shi yasa a lokuta da dama yake kasa fassarata.
Ganin walwalarta ya saka ya sa rai cewa zata yi abincin rana da su, amma gudun kada akuma ya sa ya bita don ya tabbatar. Sai dai ta tabbatar masa da cewa ta figa ta dafa abincin rana tun da safe kuma nasu ne ita da yara, sauce ne kawai a fridge zata dumama ta hada musu salad su ci. Ko amsa bai bata ba ya fice ya barta a dakin, tabi bayansa da harara tana dariya.
Don haka da rana tayi sai akwai ya yiwo order din abinci aka kawo musu har gida, haka ya kirawo yaransa gaba daya suka hadu da Naja suka ci suka koshi. Ita kuma Khadeeja ko damunta abun bai yi ba, taci abincinta ta zubawa hafsa sannan ta bayar da ragowar.
A haka aka karasa wannan amarcin. Kullum Khadeeja zata dafa abincinta shi kuma zai ywo order su ci su koshi tare da amarya da yarasa. Babu wanda ya taba yiwa Khadeeja tayi ita kuma bata taba tambayarsa nata kason ba.
PAGE 150
MIJIN MARIGAYIYA
A HAUSA NOVEL BY SAKINA YAZID (INNAR SU AMAL)
Tayi zaton ranar da kwana zai dawo kanta zata ji tana cikin yanayin murna, sai dai ba hakan ya kasance ba. Yau ne zata karbi kwana amma sai taji kamar ma ba zata iya bari ya kusanceta ba saboda lkamar dai har yanzu kokari take ta saba da cewa su biyu ne matansa. Haka dai ta tashi ta gama duk wata hidima da takeyi. Ya riga ya sanar da su cewa da daddare za adinga karbar kwanan don haka tun yamma ta shirya abincin dare; duk da bata cikin walwala amma haka ta girka baincin da ta tabbatar yana so; tuwo miyar kubewa danya. Ta hada komai ta jera a table din sama. Sai dai ga mamakinta har wannan lokaci Naja tana dakinsa na sama, don haka ma bata ko je kusa da dakin ba tana jiran ya dawo taji ko shine zai biyota dakinta tunda dai kwananta ne.
Da yake bayan ya ci abincin rana ya sake fita sai wajen 8pm ya shigo gidan.
A dakinta ya sameta tana mike a kan gado da Hammad a kwance a kan cikinta yana wutsil-wutsil dinsa. Bayan ya amsa sannu da zuwanta ya karasa ya zauna gefen gadon.
Suka dan taba hira sanna tace ‘Um ga abinci can a dinin fa, idan ka shirya sai mu je mu ci. Yara dai sun ci nasu don yau tun magriba Nas ta fara jin yunwa.’
‘Oh,Ok.’ Ya amsa kamar mara gaskiya.
Tace ‘Kuma na ga amarya har yanzu tana dakin naka fa, ko a nan zamu kwana ne?’
Kamar wanda aka tayar daga bacci yace ‘Umm. No, umm kin gane? Dama ina so nayi miki magana don da na san zaki dafa abincin darem zan ce ki dakata.’
Ta kalleshi da mamaki tana jira taji karashen bayanin, suka hada ido yayi sauri ya kawar da idonsa. Suka dan yi jim sannan ya cigaba ‘Ina ga ya kamata tunda ke kina jego ki bar mata kwnakin naki zuwa lokacin da zaki cika arba’in ko?’
Ta dauke Hamma daga kan cikinta ta tashi zaune tana karewa Mustapha kallo ko zai sauya maganarsa, kamar bai fahimci sakon ba don sai ya kara hade rai yana wasu muzurai. Tayi murmushin yake tace ‘Oh, yanzu kenan kwanan gaba daya na amarya ne har sai na cika arba’in da haihuwar Hammad?’
‘Eh, to ai kinga kina jego. Menene amfanin kwanan?’
Ta sunkuyar da kai, ta dago ta kalleshi sanna tayi gajeran murmushi tace ‘Hakane, Allah ya kai mu arba’in din.
PAGE 151
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Kamar wanda aka tsikara ya mike yana yage baki yana cewa ‘Yauwa, to bari naje sai da safe ko.’
Cikin sauri ya fice daga dakin kamar wanda yake tsoron kada ta rikeshi tace ta fasa.
Tabi kofar da kallo bayan ya fice; wasu hawaye masu zafi suka gangaro kan fuskarta a daidai lokacin da wani malolo ya taso ya tokare mata makogoro take neman kasa numfashi. Sautin rufe kofar ya dawo da tunaninta cikin dakin bayan da ta kifta idonta; tayi murmushi mai ciwo tare da sunkuyar da kai. Wato dai yanzu Mustapha yayi sabuwar amarya har ya fara gudunta, tunda ai lokacin da tayi bari sai da ya nuna bacin ransa a kan tafiyar da tayi gida. To me yake nufi da ita? Wato idan wahal ce taje ita kadai tayi ta sha kenan, lokacin da zai iya morarta shine lokacin da zai bata kwana. Lallai akwai aiki amma dai ba zata fasa addu’a duk da zuwa yanzu duk dan wani karsashin kyautatawa Mustapha da take so tayi ya zirare.
Sai da Hammad ya fara kuka sannan tayi ajiyar zuciya ta sa bayan hannunta ta share hawayenta sanna ta mika hannu ta daukoshi daga inda yake kwance ta saka masa nono. Har ya gama shan non ya saki tana ajiyar zuciya, ta shiryashi ta goya shi sannan ta fice daga dakin. Da yake dare yayi tana jiyo muryarsu kasa-kasa sun hira tunda dakin nasa yana jikin nata dakin. Haka ta wuce da yaje a parlor dinta ta jera musu abincin daren can ta wuce taje ta kwashe ta mayar kitchen tana kwafa. Ta dawo suka kwanta ita da Hammad.
PAGE 152
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Duk yanda take jin bacci a wannan daren kasawa tayi, sai dai da yake bacci barawo ne sai da ya faki idonta ya sace ta; sai ji kawai tayi ana assalatu. Duk da ba sallah zata yi ba sai da ta tashi ta wanke fuska sanna ta zauna tayi azkar dinta sannan ta koma ta kwanta.
Tun kafin a daura aurensa da Naja ya riga ya gaya mata amarci zasu yi na kusan kwana talatin domin lokacin da zata tare zai yi daidai da kwanan Khadeeja goma sha biyu da haihuwa. Don haka ya sanar da ita gaba daya kwanan nata ne har sai Khadeeja ta gama jego kwana arba’in. Ita Khadeejan ce bai gayawa ba shi yasa ma ta zata za ayi yanda aka saba ne ta karbi kwananta bayan kwana bakwai.
Ba karamin dadi yaji ba da Khadeeja ta amsa masa ko da yake dama bai sa ran zata bashi matsala ba tunda dai ta san ba zata biya masa bukatarsa ba wadda a wannan lokacin ko allah ma bai haramta masa ya kaiwa daya matar tasa bukatar ba. Cikin walwala suka kwana shi da amaryarsa, ko da ya fito da asuba zai tafi masallaci ya hango fitila ta kasan kofar dakin Khadeeja don haka ma ya san ta riga ta tashi.
Da sallama ya shigo parlor din bayan ya dawo daga masallaci, kai tsaye ya nufi kitchen din don ya jiyo motsinta a can. Tana tsaye da goyon Hammad tana zuba ruwan zafi a flask. Bayan ta amsa sallamarsa ta gaisheshi; yana ta wani kau da kai yana muzurai kamar yanda ya saba idan yana so ya gwada mata son kai haka ya amsa gaisuwar tata. Ta mayar da kettle din inda take sanna ta bude fridge don ta dauko ragowar peppersoup dinta. Yace ‘Ina yaran? Basu taso ba.’
‘Eh.’ Ta amsa a gajarce ba tare da ta bar abinda takeyi ba.
Ya kula da yanayinta idan ya takurata zata iya birkice masa a safiyar don haka yace ‘Ok, idan sun shitya kice su biga min kofa please.’
‘Ok.’ Ta sake bashi amsa a gajarce.
Ya juya ya fice daga kitchen din.
Ta karasa dumama soup dinta ta juye a flask, ta dauki ruwan zafinta ta hada ta kai daki sannan ta dawo ta dauki kayan shayi duka ta shigar daki. Ta zauna ta ci burodi da soup ta sha shayinta mai kauri sannan ta koma ta kwantar da Hammad itama ta kwanta.
PAGE 153
MIJIN MARIGAYIYA
A HAUSA NOVEL by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Bata dade da kwanciya ba kuwa bacci ya dauketa saboda dama na jiya ba isarta yayi ba.
Kamar a mafarki taji ana buga mata kofa, tayi firgigit ta bude ido. Ko ba a gaya mata ba ta san wannan bugun Habib ne don haka ta tashi zaune ta janyo wayarta ta duba lokaci; 8:25am. Ta janyo zanin goyon Hammad dake kusa ta rufe jikinta sanna tace ‘Shigo Habib.’
Ya turo kofar ya shigo da sallama, tun kafin ta gama amsa sallamar tasa yace ‘Anti yau makara kika yi ne? Yanzu har past 8 fa kinga bamu tafi makaranta ba.’
‘To me yasa baki tafi ba, ni ai na zata kun tafi tuni.’
Ya karasa ya zauna a bakin gadon da mamaki a fuskarsa yana cewa ‘Anti baki tashemu ba fa; nima bayan mun dawo daga masallaci da Abba har nayi wanka fa na dan kwanta don na san zaki tasheni shine bacci ya kwasheni. Su Afaf ma gasu can ko sallah ma basu yi ba sai yanzu na taso su har Hafsan.’
Ta kama haba tana cewa ‘Ikon Allah. To ai ba nice da girki ba Habib, Antin ku ce. Itace zata tashi kowa ta shirya shi yasa ma ka ga ban fito ba.’
Ya tabe baki yana zare ido ‘Tab, to ai kuwa daga ita har Abban babu wanda ya fito.’
‘To Allah ya sa dai lafiya, kaje ka buga musu kofa. Ka murda kofar parlor din a bude take sai ka kwankwasa dakin kaji.’
Ya mike ya fice daga dakin yayinda ita kuma ta zame ta gyara kwanciyarta da niyyar komawa bacci.
……
A tsakiyar parlor din Habib yaci karo da Abban nashi yana fitowa da gaggawa, suka hadu a tsakiya suka yi cirkocirko. Abban nasu yace ‘Kai Habib meye haka? Na cewa Anti ku taso ni idan kun shirya me yasa baku taso ni ba? Kai ko uniform ma baka saka ba.’
Yace ‘Abba ai makara muka yi, Anti Najan bata tashemu mun shirya ba.”
Kafin ya bashi amsa sauran yaran suka shigo kowa da kayan bacci, ya kallesu sannan ya mayar da hankalinsa kan Habib din yana cewa ‘Wace Anti Naja kuma, ko dai Anti Khadeeja?’
‘To ai itama Antin bacci takeyi yanzu naje tashinta tace min ba itace da girki ba Anti Naja ce zata shirya mu.’
Mamaki ya kama shi; ya za ayi Khadeeja ta gayawa yaro wannan maganar? Wane irin wulakanci ne bayan itace ta saba shirya yaran kawai kuma yanzu sai tace Naja ce zata shiryasu?
PAGE 154
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Ba tare da yace komai ba ya wuce yaran ya nufi dakin Khadeejan. Habib ya dubi ‘yanuwansa yace ‘Yau dai mun yi mising school, ni yunwa nake ji ma kuzo muje kasa bread yana can ko shayi sai mu hada.’
Ya wuce suka bi shi suka sauka kasa.
Kusan a fusace ya tura kofar, hangota da yayi a kwance tana bacci ya kara harzuka shi. Sautin bude kofar ne ya farkar da Hammad daga bacci. Ta tashi zaune tana mittsike ido sanna ta mika hannu ta daukeshi. Ta dubi Mustapha cikin halin ko in kula tace ‘Ohhh! Abba ka tayar min da yaro yanzu babu sauran bacci.’
Ta daga shi yayi mika sannan ta saka masa nono yayinda Mustaphan yake cewa ‘Me ya faru naga baki tashi kin shirya yara ba bayan yau akwai makaranta, kuma fa ko da asuba sai da na ce miki idan sun shirya kice suyi min magana?’
Tace ‘Oh! Ai basu zo sun ce min sun shirya ba na zata ma sun gaya maka kun wuce sai da Habib ya gaya min yanzu sannan na sani.’
‘Ban gane ba, wai wace magana kike yi ne? to me yasa baki tashi kin shirya su ba?’
‘Oh to ai wadda take da kwana itace da gida musamman ma da yake ni ina jego. Na zata da kai mata kwanan ka gaya mata abinda aka saba yi na running gidan.’
Mamakin da yake fuskarsa ya karu ya hade da takaicin Khadeeja, yace ‘Ban gane wadda take da kwana itace take da gida ba Khadeeja. Ke kika saba shirya yaran nan kullum kuma kin san haka, shine yau saboda ganin ido zaki ce ita zata shiryasu? Idan kina jin haushina ai sai ki gaya min tunda ba dole nayi miki kika bar mata kwanan ba ko? Zaki fara wulakancin naki ko Khadeeja?’
Tayi dariyar yake tace ‘Wallahi ni duk ban gane ba. Ai ni a yanda na sani duk matar da take da kwana da girki itace take duk wata harka ta kula da gida, nima idan na karbi girki sai na hada gaba daya nayi.’
‘Khadeeja, bana son wulakanci. Yaran nan a hannunki suke kuma da ke suka saba, ya za ayi tana zuwa ki dora mata kula dasu ita da yau zata koma aiki.’
PAGE 155
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
‘Amma dai ba dasu na zo ba a nan na samesu ko? Kuma idan ban manta ba nima daga zuwana aka hada ni da su, kamar ma ita an daga mata kafa. Hidimarsu ta makaranta ma wadda ta riga ta saba yi tun ma kafin ta auri ubansu balle yanzu da ta aureka, ai inaga wannan ma karamin abune.’
Ya gama kulewa har wani huci yake, ya cije lebe sannan yace ‘Khadeeja bana son wulakancinki fa, yanzu me kike nufi da yaran nan?’
‘Alkhairi nake nufi da kowa, kawai dai duk wadda take da kwana ta hada duk har gidan da yaran ta kula da su. Shikenan.’
Har ya juya zai fita ya juyo ya nuna ta da yatsa yana cewa ‘Yanzu shikenan kintura mata yara har tsawon sati hudu?’
Ta dago ta kalleshi cikin halin ko in kula tana cewa ‘Na tura mata mijin ma?’
‘Mtsewww!’ ya ja dogon tsaki ya fice ya maka mata kofar.
Tayi ‘yar dariya ta cigaba da wasa da Hammad.
……..
Har ya koma dakin tana kwance tana baccinta domin office din da zata ta riga tace sai wajen sha daya zata tafi saboda an canza mata branch sakamakon aurensu da Mustapha; ta san tunda yau zata fara reporting tana da damar makara. A hankali ya bude kofar ya shiga saboda kada ya tasheta daga bacci, ya karasa ya zauna a gefen gadon. Ya zuba fuskarsa a tafukan hannunsa yana shafa fuskar,