Showing 54001 words to 57000 words out of 95984 words
yake yi da ita ba tun yau ba. Da bakinsa ya gaya min babu ragowar kaunarta a zuciyarsa…..’
‘Ke rabu da shi, namiji ai munafiki ne. za dai muyi maganinsa tunda mun ga kamun ludayinta.’ Ta katseta tana yarfe hannuwa.
PAGE 140
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Ranar daurin aure tun da sassafe baki suka fara zuwa gidan, zuwan nasu ma sai ya fi mata sauki tunda ya bata dama ta baro Mustapha a sama ta taho wajen bakin. Ba zata iya tsayawa a inda yake ba yana ta faman walwala yana kaiwa da kawowa yana kwalliya, sai ta ga kamar yana yi ne don ya bata haushi. Don haka taji dadi sosai da aka ce mata Yaya Jidda ta zo da mutane.
Nan ta sauko suka gaisa, ta bude musu dakin baki tunda dama a daya parlor din suka sauka wanda ba na amarya ba. Sosai Yaya Jiddan ta so su hau sama amma sam Khadeeja taki bada fuska, don haka suka hakura suka baje zugarsu a nan kasan. Duk wani abu da suke bukata na cefanensu sun taho da shi da mayan tukwanensu, shi kansa Mustaphan bai san a nan zasu yi girkin ba da ya biya an girka musu don baya son a bata gidan nan. Amma haka yana ji yana gani kafin ma ya sauko an sauke kayan aiki an hau kokarin hura wuta; a cewar Yaya Jidda sun bayar a yi musu tuwon shinkafa da masa da shinkafa amma masu yi miyarsu bata dadai don haka su zasu girka tasu miyar. Nan da nan ya ja motarsa ya fice daga gidan suka tafi daurin aure.
Tunda Mustapha ya fita ta dauki Hammad ta haye sama, suka zauna da Nabila wadda dama bata sauko ba ma balle ta ga kalarsu. Hafsa mai aikinta dai ita dole ta zauna ana komai da ita, sannan ga su Afaf wadanda tuni suka shiga cikin dangi ana ta rawar kai.
Can kusan la’asar su Yaya Mama suka zo ita da cousins dinsu mutum biyu da kuma kannen Mommy su biyu. Bayan sun gaisa da Yaya Jidda a parlor din kasa kai tsaye suka haye sama.
Basu dade da hayewa ba kuma Hajia mahaifiyar Mustaphan ta iso da tata zugar, nan da nan gida ya cika ana ta kaiwa da kawowa.
Bayan an gaggaisa Hajia ta dubi Yaya Jidda tace ‘Ina Khadeejan ne? Ban ganta ba.’
Inna Ramla tayi sauri ta amsa kafih Yaya Jidan tace wani abu ‘A’a suna sama benen nan fa ita da ‘yanuwanta, benen da ‘yan gidan ma ban ga suna hawansa ba tunda duk gasu nan tare da mu.’
Ta sake duban Yaya Jidda tace ‘Ban gane tana sama ba.’
Ta tabe baki ‘Toh haka muka gani, tana saman ita da ‘yan uwanta.’
PAGE 141
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Kafin tace wani abu Khadeejan ta sauko sauko parlor din da sallama; Shukra ce ta hau ta gaya mata zuwan Hajia shine tayi sauri ta sauko saboda kada tayi laifi.
Ta ratsa mutanen har gaban Hajia ta tsuguna ta gaisheta cikin girmamawa sanna tayi mata Allah ya sanya alkhairi. Ta dubi mutanen duk suka gaggaisa tana kama sunan wadanda ta sani. Har ta mike Hajia tace ‘Ina Mommyn naki, bata zo ba?’
Tace ‘Eh, bata zo ba, su Yaya Mama ne kawai suka zo.’
‘To madalla.’
Ta mike ta fice tsakar gidan suka gaggaisa da mutanen dake zazzaune, ta kalli wajen da su Yaya Jidda suka yi aikinsu yanda yayi kace-kace ta dauke kai. Har ta juya zata koma ciki Habib ya turo gate ya shiga, daga inda yake ya kirawo sunanta ‘Anti.’
Ta tsaya ta juyo ‘Yaya Habib, ina ka shiga ne tun dazu Shukra take nemanka.’
‘Ina nan Anti, wajen abokina naje. Yanzu na wallahi yunwa nake ji, abinci zaki bamu.’
Tace ‘To ai Anti Jidda zaka yiwa magana ga abinci nan an dafa.’
Ya shafa kai yana cewa ‘Anti ai na gaya mata, tuwo ne fa da masa Anti don Allah ni dai ki bani abinci.’
Tayi dariya don ta san tabbas Habib baya cin tuwo da masa da ma abincin gargajiya da yawa, tace ‘Kaje sama wajen Anti Nabeela ta zuba maka.’
Har ya wuce yace ‘Ni da abokaina Anti?’
‘Eh, ka gaya mata ko ku nawa ne.’
Bai jima da hayewa ba itama ta bi bayansa, kafin taje ya dauko flask Nabeela ta zuba masa shinkafa da kaza ga coleslawa da sauce din dankalin bature wanda duk a nan saman suka dafa shi tunda basu da yawa. Ya dauko kwanukan ya sauko ya fice.
Haka aka yi ta hada-hada ana kaiwa da kawowa. Sai dai zuwan Hajia ya sa babu yanda Khadeeja zata yi dole ta zauna a kasa a yi da ita, don haka Yaya Mama da kuma Anti Innani suka sauko suka gaida Hajia suma suka zauna don tayata zama.
PAGE 142
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Bin mutane kawai takeyi da kallo zuciyarta tana kuna; ji take a ranta kamar da za a bude zuciyarta to da za a tara tana turirisaboda zafin da take ji. Fuskokinsu take kallo daya bayan daya, musamman Hajia wadda ake ta yi mata Allah ya sanya alkhairi ana barka da arziki tana amsawa kamar wadda aka yiwa bushara da kujerar Makka. Haka tacigaba da zama a cikinsu tana jin kamar ta ruga da gudu; sai dai loakci zuwa lokaci ta kan tashi kamar mai duba wani abu ta haye sama, idan ta ja numfashi ta share kwalla sai ta dawo. Haka suka yi ta yi har gefin magriba; abokan ango suka zo da motaci suka debi yan dauko amarya sannan suka tafi dauko amarya.
Hak ta yi sallar magriba zuciyarta tana dukan uku-uku; ta rsa ma abinda yake bata mata ran. Tabbas tana kishi to amma ta fi tsoron rashin adalcin da take ji a jikinta Mustapha zai shimfida; amma tana addu’a kuma za zata fasa ba don ta san tabbas Allah ne gatanta.
Wajen 8:30pm aka shigo da amarya, nan da nan gida ya dau guda mata na ta shewa. A lokaci guda kuma bugun zuciyar Khadeeja ya kara gudu. Tana zaune a kan kafet kusa da Hajia; duk su Yaya Jidda suka mike suna tarbar amaya, aka budawa wadanda suka riko amarya suka karasa gaban Hajia wadda take hakimce a kan 3-seater. Aka zaunar da amarya a gaban Hajia, mata suka cigaba da zabga guda.
Sai da hayaniya ta lafa sannan aka gaisa da masu kawo amarya, suka mikata hannun Hajia. Hajia tace ‘Ma sha Allah, Allah ya sa wannan aure har aljannah. Wannan ai ‘yar uwarta za a bawa ita ba ni ba, ina Khadeejan ne da fa tana nan zaune kusa da ni.’
Wadda take zaune kusa da Khadeejan tace ‘Gata nan fa.’
Mutane ne suka zauna a gabanta suka kareta da aka shigo da amaryar; nan da nan aka buda. Hajiya ta mika hannu yayinda Khadeejan ta matso tna cewa ‘Zo Khadeeja ga kanwarki an kawo miki.’
PAGE 143
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Ta sunkuyar da kanta tana duban cinyarta domin tana tsoron kada idanuwanta su bada ita ta hanyar tunkuda awaye a daidai wannan lokacin. Hajia ta kama hannunta sanna ta kamo hannun Naja ta dora ta hada ta rike tana kallon Khadeejan tana cewa ‘Ga amanar kanwarki nan, ki riketa amana ku zauna lafiya ku samarwa da mijinku nutsuwa. Allah ya hada kayuwanku.’
Mata suka kaure da amshi ‘Amin. Amin.’
Wata cikin iyayen amaryar ta karbe ta cigaba ‘Eh gata nan amana, a yi hakuri uwargida sarautar mata ku zauna cikin amincin Allah domin kayan Alah na annabi ne.’
Aka sake kaurewa da guda.
So take ta zare hannunta amma hajia bata basu dama ba; bugun zucuyarta kara sauri yake yayinda take jin hanunta kamar ta rike wuta. Kokari take ta dafe bakinta saboda kada abinda yake zuciyarta ya fito; Amana! Ita za a bawa amanar matar Mustapha? Ina ruwanta da ita? Ko sunyi mantuwa ne? shi da yaga zai iya da amanar ai yayi gammo ya dauko. Don me zasu ce ita aka bawa amana? Tabbas wanna amana ce da bata karba ba kuma ba zata taba iya karba ba.
Sai da aka gama addu’oi sannan Hajia ta saki hannuwansu, cikin dabara Khadeeja ta faki ido ta goge kwallar da ta taru a kwarmin idonta.
Ba dadewa kuma aka fara mikewa aka kama hannun amarya aka nufi dakinta, a haka ne Khadeeja ta samu ta sulale ta haye sama, yayinda su kuma matan suka bi bayan amarya.
Haka ta koma cikin su Yaya Mama ta cigaba da dagewa, su kuma suna ta bata baki da nasiha. Wajen 9pm gayya ta fara watsewa, aka kirawota ta yi sallama da Hajia, ba dadewa kuma su Yaya Mama suma suka yi mata sallama suka barta ita da Nabeela.
Tana zaune a gefen gadonta tana jiyo yara wajen 11pm suka hawo saman, gaba dayansu sai da suka leka dakinta suka yi mata sai da safe amma banda Afaf, suka wuce dakinsu inda suke kwana tare da Hafsa. Basu dade ba kuma Nabila ta fito daga dakin bakin da yake saman ta turo kofar dakin a hankali ta shiga, ta wuce Khadeejan a gefen gadon ta zagaya ta kwantar da Hammad a gafe ta lullubeshi. Ta zagayo ta zauna a kusa da Khadeejan, bata motsa ba kamar ma bata san an zauna a kusa da ita ba.
PAGE 144
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Ta mika hannu ta dafa nata hannun da yake kan cinyarta tana kallon fuskarta tana cewa ‘Yaya Khadeeja ga Hammad fa na kwantar miki da shi.’
Ta kalleta suka hada ido, ba tare da tace komai ba ta sake kawar da idonta saboda ta tokare hawayen da suke neman kwace mata. Nabila ta dan matsa hannunta tana cewa ‘Ya Khadeeja.’
Kafin tace wani abu hawayen ya fara bin idonta, gaba daya ta sakesu saboda yanda take faman rikesu tana jin kamar an dora mata dakon wani kaya mai nauyi. Gaba daya ta fada jikin Nabeela wadda ta rungumeta gaba daya suka sa kuka. Ita Nabeela auren ma gaba daya ya kara bata tsoro’ kuma ta tabbatar ko da wanne lokaci za a iya daura nata auren; tunda da ba don Ahmad ya tafi UK karo karatu ba da tuni ta shekara a daki. Ita kuma Khadeeja gaba daya komai ma ya tsaya mata; tana dai fatan Allah ya sa Mustapha ya zama mai adalci.
A hankali suka fara lafawa, Khadeeja ta zare jikinta ta kalli Nabeela. Suna hada ido suka tuntsire da dariya duk da hawayen da suke fuskokinsu. Suka rike hannun juna suna murmushi. Khadeeja ta dubeta tace ‘Sorry.’
Itama murmushin tayi mata tana cewa ‘Its’s ok, you will be fine in sha allah. Komai zai wuce kamar ba ayi ba.’
Murmushi ta sake mayar mata sanna tace ‘Kije ki kwanta, na san yanzu Abbansu zai shigo.’
Ta sake rungumeta sannan tayi mata sallama ta fice ta rufe mata kofa.
Ba tare da bata lokaci ba ta mike ta shiga bandaki inda ta yiwo wanka sannan ta fito da alwala, ta shirya ta sa kayan bacinta sannan ta kabbara sallar isha’i.
A nan ya shigo ya sameta tana zaune a kan dadduma tana gyangyadi; kallo daya tayi masa taji zuciyarta ta sake komawa cikin damuwa wadda ta fi ta da. Sai wani faman yage baki yake yana muzurai a lokaci guda; a sanin da tayi masa ta san murnace da doki yakeyi na amarya kuma yana kokarin tabbatarwa ita din bata kawo masa cikas ba. Nan da nan ta danne duk wata damuwa da take ranta ta kakalo murmushi tayi masa sannu da zuwa.
A tsaye ya amsa yayi mata bangajiyar biki sannan yace ‘Um ni bari naje, na ga kema bacci kike ji. In ya so da safe na shigo da kanwar taki ku gaisa.’
‘To Allah ya kai mu.’
PAGE 145
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Ya juya ya fice ya rufo mata kofa.
Ta ji dadi sosai da ya sanar da ita ba zai shigo da atarsa a wannan daren ba, domin gaba daya a gajiye take. Ba jikinta ba har ruhinta ma ji take ya gaji, fatanta kawai wadannan kwanakin su wuce ko kuma ma ta farka taga mafarki takeyi. Taga rayuwarsu ta dawo kamar yanda take a farkon aurensu; ko da yake a farkon auren ma babu wani abun kirki da zata dorar; kamar dai gara ma tace rayuwarsu ta dawo yanda ake kafin aure.
Sai da bacci ya fara dibanta sannan ta tashi ta kwanta a kan ganto ta kashe fitila.
………
Cike da doki ya shiga dakin amaryarsa rike da ledarsa ta kayan ciye-ciye; tana zaune a can a kuryar gado. Ko da ace ta amsa sallamarsa to shi dai bai ji ba, amma ya riga ya san yanda amare suke. Har inda take ya karasa ya sameta bayan ya ajiye ledar hannunsa a kan mudubi. Ga mamakinsa bayan ya daga fuskarta kuka takeyi sosai da hawaye kamar wadda aka yiwa auren dole, don haka nan take ya shiga aikin lallashi. Sai da suka kusan minti talatin sanna ya samu ta goge hawayen ta saurareshi.
‘Wai me ya faru ne kike ta faman kuka haka sai kace wadda aka yiwa auren dole?’
Ta balla masa harara ta dauke kai sannan tace ‘Ni da ka kawo na zabi dakin da nake so a sama kusa da nka dakin shine za a kawoni a ajiye ni a nan, ka sa ina nema nayi musu da masu kawoni.’
Ya yi murmushin yake ya sake kamo hannunta wanda ta riga ta fizge yana cewa ‘Haba ke kuwa? Ai na zata da suka zo kafi sun gaya miki.’
Ta zumbura baki ‘Ni babu wanda ya gaya min, sai da aka kawo ni kawai naga an ajiyeni a kofar gida kamar wata wadda ba a so zuwanta ba.’
Nan ya shiga faman bata hakuri da bayani tana faman fizgewa har dai ya samu ta sauko. Ta kalleshi tace ‘Amma gaskiya ni fa ba zan zauna a nan ba, matarka da yaranka da kai kuna sama. Kenan fa duk ranar da ba kwana na ba ni kadai ce a kasa bakin kofa. Gaskiya wannan tysarin bai yi min ba, ko dai a bani sama ko kuma gaskiya ka nema min wani gidan. Wannan ai duk wanda ma ya zo ya san matsayina.’
PAGE 146
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Ya kara matsawa ya janyota jikinsa ‘Kin ga, kada wannan ya dameki. Ko da ban kama wani gidan ba zaki iya komawa saman in ya so ko ni sai na dawo kasan ku kuma gaba daya kuyi zamanku a saman.’
‘Ni dai ba haka nace ba, amma gaskiya ka cika min alkawari don ba zan yarda wata tana sama ni ina kasa ba.’
Haka yayi ta lallabata har ya samu ta amince masa. Ya tattara musu kayansu suka wuce sama dakinsu wanda da farko ta so ta ki zuwa, sai kuma ta tuna gara itama ta hau saman ta ga yanda Khadeejan zata yi.
……..
Da yake dama Hammad bai saba barinta baccin safe ba yau din ma tun wajen 6am ya tashesu, bata bude dakin ba saida tayi wanka shima ta shirya shi. Ta riga ta ji motsinsu tun dare don haka ta san a dakin Mustaphan suka kwana. tana fitowa ta taso Hafsa suka shiga kitchen. Ya siyo burodi kamar yanda ya saba duk dare, don haka nan da nan ta soyawa kowa kwai ta hada kayan shayi tsaf ta bawa hafsa ta sauko da shi kasa. Kafin karfe takwasa ta jera komai da suke bukata ita da yara na breakfast a parlor din kasa. Tana shirin hawowa bene Hafsa ta biyota da wayarta ta mika mata tana ringing. Tana dubawa taga Baffa ne.
Bayan sun gaisa ya kara yi mata nasiha sanna yace mata nan da awa daya Nabeela ta shirya Ahmad zai zo ya dauketa.
Bata ji wata damuwa ba saboda dama ta san halin Baffa, ba tare da bata lokaci ba ta taso Nabila ta sanar da ita. Nan da nan ta hada kayanta don ko wanka cewa tayi idan taje gida tayi abunta, haka ma breakfast cewa tayi idan taje gida ta ci kosai don tabbatar yau lahadi kosai Mommy tayi.
Wajen 9am suna zaune a dining table ita da yara in banda Afaf wadda bata tashi ba ko kuma bata fito daga dakinsu ba. Breakfast sukeyi suna ta hirarrakinsu Shukra sai labari take basu suna dariya gaba daya. Da sallama ya sauko daga benen ya karasa gaba table din yana cewa ‘Ina can ina nemanki a dakinki ashe kina nan ke da yara kuna ta jin dadinku.’
Tayi murmushi ta kwara da kai. Ita da yaran duka suka gaishehi, bayan ya amsa ya dubeta yace ‘Idan kun gama cin abincin ki zo ki bani nawa breakfast din ni da kanwarki.’
PAGE 147
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Tayi murmushin yake tace ‘Da yake mu ma bread da shayi muka sha ba wani abu ba, amma dama naga bread din da yawa ka siyo gashi can mun bar muku guda daya ka dauka ka haye muku da shi. Ko a nan zaku yi breakfast din?’
Ya kalleta da dan mamaki ya cije lebe don baya son ya ja zancen a gaban yara yace ‘Um, idan kin gama dai kya hawo da shi.’
‘Ok.’ Ta amsa cigaba da cin abincinta.
Sai da suka gama cin abincinsu tsaf sannan ta dauki bread din ta haye sama, tana shiga babu kowa a parlor din don haka ta karasa kan dining table ta ajiye bread din ta shige dakinta.
Kamar tare suka shiga dakin don ko zama bata yi ba ya shigo ya tura kofar, yana daga tsaye a jikin kofar yace ‘Wai ya na ganki a nan ina breakfast din namu ni da kanwarki?’
Ta karasa ta zauna a kan gadon ta jingine ta mike kafarta tana cewa ‘Oh, ga bread din can na ajiye muku ai ko akwai wani abun ne?’
Da mamaki yace ‘Ai na zata zaki dan dafa wani abu ko don saboda ganin ga bakuwa kin kwana da ita a gidan.’
Bata san lokacin da dariya ta kwace mata ba, haka kawai maganar tashi sai ta bata dariya musamman da ta kalleshi kuma yana cewa wai “kin kwana da bakuwa”
Ta dan gintse tana kokarin saita fuskarta sanna tace ‘Na kawana da bakuwa ko ka kwana da ita? Tea and bread muka ci fa