Showing 33001 words to 36000 words out of 95984 words

Chapter 12 - Mijin Marigayiyya Complete Sakina Yazid

18 Sep 2025

9709

mata mukullin gidan? Ai idan muka dawo sai abinda muka gani kenan, za ma ta iya fara shigo da maza gidan ko ayi mata wayo ayi mana barna idan aka gane ita kadai ake bari a gidan.’

‘To yanzu ya kake so ayi? Ka ga dai da ni da yaran ai dole duk muje makaranta ko?’

‘Ni ma ban sani ba, kece zaki san yanda zaki yi. Zaki maiya fita da ita ki rufe gidan in ya so sai ku dawo tare ki dauko yaran, duk yanda dai kuka yi. Amma dai gaskiya wannan tsarin na barinta a gidan bai yi min ba.’

Ranta ya fara baci; me yake nufi ne? so yake yace ta bar makarantarta kawai saboda ta zauna masa da yara ko kuwa mai aikin yake so ya korar mata? Wannan bayanin da yake yi ma sam ba zai yiwu ba gara dai ya sake lissafi ko kuma shi ya dinga baro office yana zuwa yana daukosu.
PAGE 87
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal

Tace ‘Uhm, to ai ka ga ba ni nake rubutawa kaina timetable ba, wani malamin ma sai 1pm yake fara lecture kuma dole nayi attending idan dai ina son na gama degree din. Sai dai ko ka kawo wata dabarar da kai kake ganin za ayi da daukosu in ya so ita Rashida idan zan fita sai na fita da ita duk lokacin da na gama lecture sai mu dawo tare.’

Suka yi shiru na dan lokaci, jimawa kadan ya tashi ya jefar da remote din TV din da yake hannunsa ya shige daki.

Ta bi bayansa da kallo tana mamaki; wai me mutumin nana yake nufi ne? shikenan sai ta jingine rayuwarta ta zauna ta kular masa da yara? To ai ita ko ‘yayan da ta haifa ma haka ko tana so ko bata so zata dinga barinsu da mai aikin ta tafi makaranta tunda dai haka taga masu yaran suna yi. Ko kuwa da yake ta auri tuburarre hakura zata yi da komai ta zauna sai yanda suka yi da ita?

Haka suka kwana a wannan daren kowa da abimda yake ransa.

Ko da gari ya waye tun asuba ta tashi uta da Rashida wadda ta tayata nan da nan suka shirya yara sannan suka hadawa kowa abinci. Kamar yanda ya saba sai karfe bakwai da kwata sanna ya fito, zuwa lokacin sun shirya suna jiransa; ya kwashesu ya kaisu ya dawo.

Sai wajen karfe tara da rabi sannan ya gama shirinsa, lokacin fitowarta kenan daga wanka saboda sai da ta tsaya ta gama abincin rana ta juye a flask sannan ta fara shirin. Ya sameta a daki tana shafa mai rike da mukullin motarsa, yana daga tsaye a bakin kofa yace ‘Ni na fita.’

Ta juyo da sauri tana cewa ‘La! Babe don Allah bari nayi sauri na saka kayana sai ka bani lift.’

‘No ba ta hanyarku zan bi ba, ki wuce kawai sai na dawo. Kada ki manta min da yara.’ Ya fada yana ficewa daga dakin.

Tabi bayansa da kallo da baki bude; lallai ma mutumin nan. Kiri-kiri dai shi baya son ya dauketa a motarsa idan dai makaranta zata, in banda haka ai ko ba hanyar makarantarsu zai bi ba ya sauketa a bakin titi ya rage mata tafiya. Ta juya ta cigaba da shiryawa cikin sanyin jiki tana tunanin son kai irin na Mustapha. Allah ya so ta ma Baffa ya tura mata kudi kuma ya sanar da ita duk wata zai dinga turo mata kudi saboda karatunta, idan tana son wani abu sai ta yi masa magana.
PAGE 88
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)

Tabbas ta san da ace da Mustapha ta dogara da sai dai ta hakura da karatunta ta zauna ta kular masa da yara.

Nan da nan ta karasa shiryawa ta fito ta sallami Rashida wadda ta barsu tare da Shukra bayan ta yi mata duk wani bayani da take bukata sannan ta kama hanya zuciyarta cike da damuwa da wasi-wasi.

Kafin sha biyu ta gama duk wani abu da take yi a makarantar sai dai bata son ta dawo ta dauko yara; ba wai yaran ne bata son daukowa ba amma bata son ta daukosu Mustapha yaga kamar fadansa ne ya sa don haka duk lokacin da zata fita ya zata zai yi mata fada ta dauko masa yara. Don haka suka nemi inuwa ita da kawayenta suka zauna suna hira, sai wajen 1;30pm sannan suka karasa masallaci suka yi sallah kowacce ta kama hanyara gida.
Ko da ta zo gida bata tarar da wata matsala ba, Rashida ta kai Shukra gidan su Ummi ta dauko Nasreen daga makarantar kamar yanda ta bata umarni. Su kuma Afaf da Habib kusan tare da ita suka shiga gidan.

Ko da ya dawo tana jin sa yana tambayar taran wanda ya daukosu daga makaranta suna ba shi amsa, musamman Shukra wadda yake ta tambayarta me suka yi ita da Rashida a gidan bayan Anti ta fita. Haka tayi banza da shi ta cigaba da harkokinta.

Haka suka cigaba da yi, sai ya zama kuma da yake ba a fara lecture sosai ba sati biyun farko kullum Khadeeja bata fita da wuri sanna kuma tana dawowa kafin ya dawo gidan, don haka matsalarsu da sauki tunda zai zo ya tarar da ita tana ta hidimar yara.

…….
Sati daya da komawa aka kafewa su Khadeeja timtable, kuma da yake babu lokaci sosai timetable din a matse take. Haka dai suka cigaba da karatun.

Ranar Alhamis shine take da lecture 8am to 6pm, don haka ta san dole ta shirya ta fita tare da yara. Tun dare ta gama komai, tayi rabin aikin abincin safe sannan ta fitowa da kowa kayansa. Ta yiwa Rashida duk wani bayani da take bukata tunda yaran idan sun dawo daga makarantar boko babu islamiyya don haka nan zasu wuni a gidan.

Tun kafin asuba ta tashi suka fara aiki tare da Rashida.
PAGE 89
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)

Bayan Mustapha ya dawo daga masallaci sallar asuba ya sameta a kitchen, tana ta fama kaiwa da kawowa tsakanin dankalin da take soyawa da kuma hadawa yara abincin makarantarsu a lunch box. Bayan ya amsa sannu da zuwanta yace ‘Wai kin yi sallah kuwa? Na ga kamar a nan na barki fa.’

Tayi ‘yar dariya tace ‘Haba dai, nayi sallah mana. Sauri nake na gama saboda yau 8am to 6pm ne da ni kuma 8am din nan idan Prof. ya rigani shiga aji rufe min kofa zai yi wallahi shi yasa nake ta sauri don kullum sai yayi attendance.’

‘Oh kenan yau sai 6pm zaki dawo gidan?’

‘Eh.’ Ta amsa a gajarce tana kwashe dankalin da ya riga ya soyu.

Ya kara hade girar sama da kasa sanna yace ‘To a ina zaki bar yara wuni guda?’

Bata son hayaniyarsa don bata son abinda zai bata mata rai, ba tare da ta bar abinda take yi ba tace ‘A nan mana gidansu; Rashida zata dauko Nasreen su kuma su Afaf idan suka dawo zasu sameta a gidan sai suyi zamansu kafin na dawo, they will be just fine.’

‘Haba ai dadewar tayi yawa, kenan haka zasu zauna suyi duk abinda suka ga dama ba tare da wata kulawa ba.’ Ya fada a fusace.

‘Kada ka damu Rashida zata kula da su.’

Kafin ya bata amsa suka jiyo ihun Nasreen daga dakinsu tana cewa ‘Wayyo Anti.’

Ta riga ta san rigimar Nasreen, idan dai aka tasheta da sasafe zuwa makaranta sai tayi kuka ko ma waye ya tasheta, shima kuma ya san da haka. Amma ba tare da bata lokaci ba ya nufi dakin da sauri. Ganin haka itama Khadeejan ta ajiye abinda take yi ta bi bayansa, kusan a lokaci daya suka shiga dakin.
Nasreen tana zaune a kan gadonsu da hawaye shabe-shabe a idonta yayinda Rashida take tsugune a gaban gadon tana rike da towel.

‘Me aka yi miki kike kuka Nasreen?’ Ya tambaya kafin ya karasa shiga dakin.

Khadeeja tana shiga dakin ta sauko daga kan gadon ta rungumeta tana cewa ‘Anteee.’

Ya shafa kanta ‘Me aka yi miki?’

Cikin shagwaba tace ‘Rasheeda ce.”

Ya juya ya dubi Rashidan a fusace yace ‘Me kika yi mata?’

Nan da nan jikinta ya hau rawa tana gyara tsuguno, kafin tayi magana Khadeeja ta shafa kan Nasreen tace ‘Nas me Rashida tayi miki?’

‘Tashi na tayi daga barci.’
PAGE 90
MIJIN MARIGAYIYA
A HAUSA NOVEL by Sakina Yazid (Innar su Amal)

‘To ai kin ga shiryaki zata yi ki tafi school ko? Ko kina son ki makara Uncle ya koroki gida ne?’

Yayi tsaki ya fice daga dakin ba tare da ya sake cewa komai ba.

Ta lallaba Nasreen ta tura ta bandaki sannan ta juyo zata fito, kafin ta fito ta jiyoshi yana dawowa dakin yana cewa ‘Dankalin da kika bari a wuta ya kone, kije ki duba na kashe miki wutar.’

Ta wuceshi ta karasa kitchen din da gudu inda ta sami dankalin ya kone, ta kwashe sannan ta sake kunna wutar ta dora. Ya karaso ya tsaya a kofar kitchen din, ya dan dauki lokaci yana kallonta tana zubawa yara abincin rana wanda ta sauke a babban flask. Jimawa kadan yace ‘Kin ga irin abinda yasa bana son ki barsu da yarinyar nan ita kadai ko? Ya za ayi ta iya kula da yara tunda gashi nan bata ma iya tashinsu daga bacci ba?’

Ta kalleshi cike da mamaki tace ‘Nasreen ce fa, ko kaine ma ka tasheta sai tayi rigima, ko ka manta ne? Kuma kaine kace baka son Rashida ta dinga yi maka girki kuma ka ga dole abu daya zan yi a lokaci guda ba zai yiwu ina girka muku abinci ba kuma ina shirya yara.’

Ya juya ya fice ba tare da ya ce komai ba.

Ta ja tsaki ta share kwallar da ta taru a gefen idonta sannan ta cigaba da aiki. Bata ma san me take ji ba, kokari kawai take ta fita daga gidan idan taje makaranta ta samu tayi tunani ta fahimci me take ji.

Bayan ta gama abinci ta wuce daki ta sameshi bayan ta zubawa yara abinci suna ci, yana kwance a gefen gado yana fama latsa waya ta wuce har ta kusa shiga wankan yace ‘Idan na kai yara dawowa zan yi kin sani, sai wajen 10am zan fita, ita wannan yarinyar taki haka zaki bar min ita a gidan daga ni sai ita?’

Cikin halin ko in kula tace ‘Eh, ita da Shukra zasu zauna idan zaka fita kawai ka gaya mata don ta san cewa ka fita ta cigaba da aikinta.’

Har zata shige bandakin yace ‘Gaskiya bana so, kuma kema kin san bai dace ba ki barni a gida daga ni sai mai aikinki mace. Irin hakane kuma idan an ce za a auri mai aikin kuce baku yarda ba.’

Duk bacin ran da take ciki sai da ya bata dariya, duk da dai dariyar takaici ce tace ‘to ai gaka nan gata nan ka aureta mana, ai itama mace ce.’
PAGE 91
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)

‘Ni dai na gaya miki bana son ki barta a gidan idan ina nan tunda ke bakya nan, ki sami inda zaki ajiyeta idan na fita sai ta dawo gidan.’

‘Uhhm!’ Ta amsa sannan ta shige wankan cike da takaicinsa, har ji take kamar zuciyarta tana turiri. Zuwa makaranta lecture kawai ya zama wata drama.

Nan da nan ta karasa shiryawa ta shirya yaran, ta hada tea ta zauna tana sha. A haka Mustafa ya fito ya samesu lokacin 7:15am. ‘Ku tashi muje.’ Ya fadawa yaran.

Ta mike rike da kofin shayinta tace ‘Bari na dauko hijab dina na saka ku rage min hanya.’

‘A’a zaki makarar damu ne fa, gashi ko shayi baki gama sha ba kuma kin san idan suka makara korosu za ayi.’ Ya juaya ga yaran wadanda sun riga sun mike kowa da kayansa a hannu yace ‘Mu je.’

‘Anti sai mun dawo.’ Suka fada sannan suka juya suka fice ya bi bayansu.

Ta bi bayansa da kallo cike da mamaki; ta kasa gane motarsa ce baya son ta dinga shiga ko kuwa tsabar bakin ciki ne a kan zata fita yake hanashi rage mata hanya. To amma kuma yana kaita unguwa, ko da yake wannan fita ce da shi ya ga dama kuma kusan duk inda zata tunda ta aureshi tare yake kaita da yaran suna biye da ita. To me yasa idan dai makaranta zata tafi sai ya san yanda yayi ya tafi ya barta ba tare da ya ko da rage mata hanya ba?

Haka har ta gama shirinta ba tare da ta samo amsar tambayarta ba; ta fito ta sami Rashida a kitchen tace ‘Idan babansu ya dawo ki koma daki ki zauna in ya fita sai ki fito ki cigaba da aikin; idan Shukra ta zauna a wajensa shikenan idan kuma ta taho wajenki to don Allah kada ki bari tayi kuka yaji.’

Tayi mata sallama ta fice tana sauri saboda 7:20am ta riga tayi kuma bata da tabbas din zata iya kaiwa BUK kafin 8:00am.

Ta kusa isa titi Mustapha ya karyo kwana ya shigo layin, ta dauke kanta daga kallon inda yake; bata sani ba ko ya ganta ko bai ganta ba. Ta karasa titi cikin sanyin jiki ta hau Napep tambayoyi daban daban suna ta yawo a kanta; wai ina babe dinta ne? wanda yake son ta? Wanda kafin aurensu har so yake ya daukota daga makaranta ya kaita unguwa ko ya kaita gida don dai tana hanashi ne saboda ta san Baffa ba zai bari ba a lokacin.
PAGE 92
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)

To shikenan soyayya ta kare ko me Mustapha yake nufi da ita? Shekara daya fa kenan da ‘yan watanni da aurensu.

Kwanci tashi cikin wannan rayuwar da Khadeeja take a gidan Mustapha har ta gama level 2 a karatunta ta shiga level 3, kuma shekararsu biyu kenan da Rashida mai aikinta. Zaman dai haka ake yinsa cikin dagewa da dagiya; idan Mustapha yana son bukatarsa a wajenta sai taji kamar ba shi ba saboda yanda yake kwantar da kai ya samu bukatarsa ta biya. Amma kuma da zarar tayi maganar karatunta ko wani abu da zai sa ta fita daga gidan ba tare da ta tafi da yara ba to sai ya nuna bacin ransa. Domin a halin yanzu kowa a danginsu ya santa da ‘yayanta domin tare ake ganinsu ko bikin wa ake yi. Gidan Mommy kuwa sun mayar da shi kamar gidan kakarsu, kuma da yake sun sami karbuwa sai suka sake sakewa.

Karatunta yana tafiya daidai tunda ta saka auduga ta toshe kunnenta daga duk wata mita ta Mustapha, sai dai kawai kullum a gajiye take daga aikin gida da kuma aikin tunanin abinda zata yi Mustapha ya daina nuna mata halin ko in kula. Yaran basu saba bata matsala ba a da, amma zuwa yanzu duk tana neman ta rasa kansu; musamman Afaf da Nasreen. Idan dai aiki ta saka su ba zasu ce ba zasu yi ba amma idan basu ga dama haka za suyi kunnen uwar shegu da ita sai dai ko ta yi aikinta ko kuma ta sa Rashida tayi mata. Sannan kuma yanzu Afaf ta kulla kawance da Samira ‘yar wajen Yaya Jidda, don haka kusan duk wani motsi na Khadeeja Afaf sai ta gaywa Samira wadda take kaiwa uwarta rahoto na kai tsaye; don haka ne ma matsawar da Yaya Jidda takewa Khadeejan ta karu.

Sai dai a yanzu ba wannan ne damuwar Khadeeja ba, babbar damuwarta itace rashin haihuwa. Tun bayan da tayi bari a loakcin corona ko batan wata bata sake yi ba gashi ana neman shekaru biyu. Zaman gidan baya mata dadi, bata jin dadin yanda yaran suke mata, musamman Afaf wadda a da take tunanin sun zama daya. Tana fatan itama Allah ya bata ‘yaya wadanda zasu kalleta a matsayin uwa.
PAGE 93
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)

Ta rigashi kwanciya kamar yanda suka saba saboda yanda ta kula idan ta zauna jiransa su kwanta tare ita ake cuta tunda dole ta tashi kafin asuba ta shirya yara. Sai wajen sha biyu saura sanna ya gama abinda yake ya kwanta a kusa da ita, ta juya ta gyara kwanciyarta. Yana kwance amma ya daga waya yana chattinga kamar yanda ‘yan kwanakin nan ta kula kullum kafin ya kwanta sai yayi chatting. Ta mike taje ta yiwo fitsari, ta sha ruwa sannan ta dawo ta kwanta, zuwa lokacin ya gama chatting din ya ajiye wayar yana azkar. Ta kwanta ta gyara kwanciyarta, bayan da ta kula ya gama azkar din ta lalubo hannunsa ta rike cikin sanyin murya tace ‘Abban Afaf.’

‘Umm.’ Ya amsa yana kallonta duka da hasken da yake cikin dakin bai kai ya kawo ba.

‘Uhm, gaskiya ina son zuwa asibiti naga gynae doctor.’ Ta fada tana wasa da hannunsa wanda ta rike.

Ya rike hannunta a cikin nasa ya kara bata hankalinsa yace ‘Baki da lafiya ne?’

‘No ba wani specific issue. Ka san dai kwanaki nace maka ina son naje a duba aga abinda yasa har yanzu ban sake samun ciki ba, kada naje wata matsala ce nayi ta zama gara naje a duba.’

Ya gyara kwanciya ya kara matsowa kusa da ita ‘Kina dai so ki dorawa kanki damuwa, har yanzu fa ba a yi shekaru biyu da barin ba. Iya wannan ya isa ya sa ki san cewa lafiyarki kalau, kawai Allah ne bai kawo ba tunda wancan din ma ba asibiti kika je kika samo ba ko?’

‘Na sani, amma dai gaskiya ina so naje a duba ni din na sami nutsuwa. Tunda ka ga idan naje aka ce min lafiyata kalau ai dawowa zan yi kawai na cigaba da addua’a, idan kuma matsala ce sa na nemi maganinta.’

‘Babu wata matsala kina dai son tonowa kanki matsalar. Ke yanzu ma da kike neman ciki ido rufe ya zaki yi da karatun? Tunda gashi kin shiga level 3 kuma ke da kanki kina cewa ya fi wahala. Ya zaki yi da laulayi ga karatu? Ko har kin mata ne? ai zai fi sauki idan ma dolene sai kin je asibitin ki bari ki gama karatun kafin ki kwantar da kanki.’

Suka yi shiru na dan lokaci, kowa da abinda yake tunani.
PAGE 94
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)

Jimawa kadan tace ‘Ina son zuwa gaskiya, amma dai ina jin zan bari mu gama

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login