Showing 51001 words to 54000 words out of 95984 words
nashi tana cewa ‘Allah sarki, abun ya zo kenan. Toh Allah ya sanya alkhairi.
PAGE 132
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Bude baki yayi yana kallonta saboda tsabar mamakin yanda ta nuna halin ko in kula da maganr tasa kamar dai wadda yake cewa gobe litinin a ranar lahadi. Ta mike zata fice ya rike hannunta yana cewa ‘Um wani abun kike yi ne kike saurin tashi.’
Ta koma ta zauna tana cewa ‘A’a, na zata ka gama maganar da zaka fada din.’
Ya dan sunkuyar da kai saboda gaba daya ya kasa hada ido da ita, wannan halin ko in kula din da ta nuna yasa duk ya firgice; gaba daya ta goge masa haddar kalaman da ya tsaro don ya bata hakuri. Cikin sanyin murya yace ‘Um baki ma tambayi wacece wadda zan aura ba.’
Ta dan yi dariya tace ‘Oh, Naja ce mana. Ko ka fasa auren nata ne?’
A jigace ya amsa ‘Itace.’
Ta daga gira cikin halin ko in kula tana shirin mikewa tace ‘Allah ya sanya alkhairi.’
‘Um, wai dama kin san zan yi auren ne ko naga kamar kin sani tun tuni.’
Tayi ‘yar dariya ta koma ta zauna tace ‘Na sani mana, ko bai kamata na sani ba?’
Ya jiijiga kai ‘No, ina dai mamaki ne.’
Suka yi shiru na dan lokaci.
‘To don Allah wa ya gaya miki?’ Muryarsa ta katse mata tunani yana tambaya.
Tayi ‘yar dariya tace ‘Oh, ka san fa na dauka kai ka gaya min; ashe ba kai bane. Ina jin dai a cikin wadanda ka gayawa ne kace kada su gaya min aka sami wani ya gaya min.’
Ya sunkuyar da kai domin ya kasa hada ido da ita; wato duk wannan tsawon lokacin ashe kallonshi kawai takeyi duk abinda yake boyewa ta sani. Ba karamin mamaki yayi ba. Kafin yace wani abu suka jiyo kukan Hammad daga cikin gidan, don haka ta dubeshi tace ‘ka ji yarona can yana kuka, bari naje na gani.’
Ta fice ba tare da ta saurari amsarshi ba.
PAGE 133
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Tana fitowa daga dakin ustaphan ta tarar da Anti Binta a parlor tana ta jijjiga Hammad, tun kafin ta karasa wajensu tace ‘Yunwa yake ji, zo ki bashi ya sha.’
Ta karbeshi ta shige dakinta Anti Binta tana biye da ita. Haka ta daure ta hadiye malolon da ya tokare mata makogoro har ta gama bashi nono suna hira da Anti Binta. Sai da ya sha ya koshi sannan ta mikawa Anti Binta shi tana cewa ‘Gashi Anti Binta, bandaki nake son shiga.’
Ta karbeshi ta mike tana cewa ‘To muna can dakin yara muna hira da mutuniyata.’
Ta fice ta ja mata kofa sannan ta mike ta shige bandakin don ta san idan dai tana cikin dakin nan wani sai ya zo nemanta, idan kuma ta rufe da mukulli za ayi ta fama tambaya. Tana shiga bandakin ta turo kofar ta jingina a jikin kofar, take hawayen da take rikewa suka kwace kamar an kunna famfo. Ta hada tafukan hannayenta ta rufe fuskarta tana jijjiga kai, saboda tsabar takurar da zuciyarta tayi har wani daci take ji a bakinta. Yaushe Mustapha ya raina ta haka? Wannan ma ya fi karfin raina ya koma wulakanci. To me yasa yayi mata haka? Daman can baya sonta ne ko kuwa son da yake mata ne ya kare? Bata taba tunanin zata auri miji ta zauna ita kadai ba amma dai ta dauka idan ka auri mutum zai cigaba da girmamaka yana ganin mutuncinka har karshen tarayyarku. A halin yanzu ta rasa wanne zatayi; murna ta haihu itama ta sami yaro ko kuwa jaje zata yiwa kanta tunda ko babu komai wannan yaron da ta haifa zai karawa alakarta da Mustapha tsawon rai. Bata san tsawon lokacin da zata iya dauka tana jure wulakanci irin wannan da Mustapha yake mata ba, amma dai ta san tabbas ba zata iya jurewa har abada ba. Gashi shi ba dukanta yake ko zagi ba, wani irin wulakanci ne yake mata yana nuna cewa komai normal ne, kuma a mafi yawancin lokuta ma idan tayi magana sai a dinga nuna mata haka maza suke. Domin kowa ce mata kawai yake idan dai namiji ne bata ga komai ba. Ta barwa Allah al’amarinta kuma zata jira su tare ta ga yanda yanayin zaman zai kama; amma tabbas idan aka cigaba a haka bata jin zata iya zama da Mustapha.
PAGE 134
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
zuwa yanzu kuma duk wasu alamu sun nuna mata cewa ba zai taba yi mata adalci ba ita da Naja, kamar ma dai yanzu ne yayi aure na soyayya wanda yake sa ran zai more rayuwarsa a ciki; tunda ta gama yi musu wahala ta raini yaransa lokacin da suke tsananin bukatar uwa. Yanzu sun girma sun zama mutane don haka sai ya aure wadda yake so ta zo su more rayuwarsu ita kuma a mayar da ita samiyar ware.
A hankali ta zame a jikin kofar ta zauna ta sake fashewa da kuka. Sai da tayi mai isarta sannan ta bawa kanta hakuri ta wanko fuskarta ta fito daga bandakin.
……..
Duk yanda take cikin damuwa da zarar Mustapha yana waje to sai ta shiga walwalarta da yara, yayinda shi kuma duk wasu shirye-shiryensa na tarbar amarya ne. har ta kai baya iya boye murnarsa; shi da yara kullum hirarsu ta Anti Naja ce. Musamman Afaf wadda zuwa yanzu kusan gaisuwa ce kawai take hadata da Khadeeja.
Lafiya suka tare a sabon gida kuma kamar yanda ta zabi dakin sama haka ya hakura ya bata dakin saman; duk da daga baya yayi nadamar hakan. Domin da ace ya san ta riga ta san da maganat aurensa to da tabbas zai gaya mata amarya zai saka a sama. Sai dai a lokacin tunaninsa bata san da maganar auren ba kuma boye mata yake son ya cigaba da yi.
Tsaf ta gyara dakinta da parlor, dakin su Afaf kuwa tunda taga ra’ayoyinta suna cin karo na da Afaf kuma tana nema tayi mata rashin kunya sai ta hakura. Sosai dakinta yayi kyau, ta tsara musu komai nasu ita da Hammad, don Baffanta ma da Mommy sai da suka kara mata kudi tayi sayayya.
Sati yana zagayowa kuma aka shiga hidimar bikinsa.
Babu yanda bata yi da Mustapha ba a kan ita bata so ayi mata taro amma ya ki amincewa; domin yace Hajia tace dangi basu san sabon gida ba don haka zasu zo su karbi amarya sannan suga gida.
……..
Tun dare ta sanar da shi cewa idan gari ya waye zata bi ‘yan makaranta taje gida wajen Mommy, kuma ba tare da wani musu ba ya amsa.
Bayan ya kai ‘yan makaranta ya dawo suka zauna tare a parlor din sama suna cin abinci yayinda Hammad yake hannun Rashida. Shiru suke cin abincin babu wanda yake magana, kamar ma dai basa cikin walwala.
PAGE 135
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Ya ajiye cokalin dake hannunsa yace ‘Kin ce babu wani abu da kuke bukata saboda taryar baki ko?’
Ba tare da ta daina cin abncinta ba tace ‘Eh. Ni kam mai ai don dai ka hana ne da sai nayi tafiyata wajen Mommy idan aka kawota aka tafi sai na dawo da daddare ko ma da safe.’
‘No, don Allah ki bar wannan maganar. Ai ya kamata dai ace a samu a karbi bakin nan cikin mutunci.’
‘Um.’
Suka cigaba da cin abincinsu, jimawa kadan yace ‘Hajia ma tace a nan zasu zo suyi biki ranar lahadin, in ya so sai su tsaya su karbi amarya sannan su tafi.’
Ta kalleshi suka hada ido sannan ta kawar da kanta, wani malolo ya zo ya toare mata makogoro; su Hajia zasuyi biki a nan? Saboda suna murna za ayi mata kishiya ko me? Ta dauki kofin shayinia mai zafi ta kurba da fatan zafin shayin zai tafiyar mata da abinda ya tokare mata makogoro amma hakan bai samu ba. Ta kalleshi a jigace tace ‘Ka ga shikenan sai na tafi gidan Mommy ko? Tunda ka ga masu karbar amarya zasu zo.’
Ya dan zaro ido yana cewa ‘Haba dai! Hakan kuma ai bai yi tsari ba, kina matar gida kuma azo biki gidan ba kya nan. Ko ba haka ba ma kin san Hajia zata ga kamar kin rainata ne shi yasa zaki tafi ki barsu su kadai suyi bikin. Please kiyi hakuri kawai saboda kada abun ya zama wata fitna kuma. Kin ji?’
Ta daga kai tana cewa ‘Uh.’
‘Yauwa, please kiyi hakuri a gama taron nan ba tare da wata matsala ba.’
Tayi gajeran murmushi tace ‘In sha Allah.’
Ya ture kwanon bayan ya kurbe dan ragowar shayinsa sannan yace ‘Zan saka miki kudi a account dinki saboda na san zaki iya bukatar wani abun ko don baki. Akwai ruwa da lemo wanda zan kawo, abincin kuma dama tunda kika ce ba zaki yi a nan ba na bayar da kudin don haka su Hajia zasu taho da shi.’
‘Ok.’
‘Idan kuma da bukata zaki iya yin wani abincin a nan ko da kadan ne.’
‘Ok, babu damuwa.’
Ya mike ya shige dakin domin ya karasa shiryawa. Nan take itama ta ture kwanon indomie din ta mike ta haye sama. Kuka take son tayi ko zata ji sanyi a ranta, amma bata so ta bata lokaci musamman da yake yana jiranta kuma tare zasu fita.
PAGE 136
MIJIN MARIGAYIYA
A Huasa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Haka tayi sauri ta shirya suka sauko tare, ta karbi Hammad a wajen Anti Binta suka fice suka bar Anti Binta Hafsu wadda kanwar Rashida ce aka kawo mata bayan an yi auren Rashidan tun kafin ta haifi Hammad.
Haka suka zauna a mota babu wanda yake magana da dan uwansa; ya riga ya kula da yanda take nema ta tayar masa da fitna a wajen bikin nan amma ba zai barta ba. Sosai ya ji dadi da Hajia tace zasu zo nan suyi biki don baya so ta bayar da matsala idan an kawo amarya, amma ya san tunda Hajia tana nan babu wata matsala da zata basu. Haka yaje ya ajiyeta a gidansu sannan ya wuce.
………
Tana shiga gidan ta sami Ahmad a parlor yana shan shayi; nan da nan ya mike ya karbi Hammad daga hannunta.
‘Ina Mommy?’ ta tambaya bayan ta amsa gaisuwar da yake mata.
‘Tana dakin Baffa.’
Ba tare da ta bashi amsa ba ta bar masa Hammad ta wuce ta nufi dakin.
A zaune ta hango Mommy a kan dadduma ta mike kafa da waya a hannunta, ta jefar da mayafinta ta karasa gaba daya ta fada jikin Mommy ta rushe da kuka.
‘Inna lillahi wa Inna ilaihi raji’un! Khadeeja me ya faru? Ina Hammad din?’ Mommy ta tambaya cikin tashin hankali.
Da kyar ta bude baki tace ‘Yana hannun Ahmad.’
Ita kanta saida taji ajiyar zuciyar da Mommy din tayi, sanna ta cigaba ‘To me ya faru kike wannan kukan haka? Ko Mustaphan sakinki yayi ne?’
Ta jijjiga kai alamar a’a ba tare da ta dago ba, ta cigaba da kukanta. Kawai sai Mommy ta hakura da tambayar ta zuba mata ido, a hankali ta daga hannunta tana shafa kanta; ta dai san da maganar saura kwana uku a daurawa Mustapha aure don haka watakila wani abun yayi mata wanda ya sosa mata rai shine ta taho nan tazo tana wannan kukan. Saida ta dauki loakci tana wannan kukan sannan ta dan numfasa ta dago ta kalli Mommy, suna hada ido kuma sai ta sake fashewa da kuka.
Cikin sheshekar kuka tace ‘Mommy ba zan iya ba, ba zan iya ba Mommy.’
Ta dago fuskarta tana share mata hawayen tace ‘Menene ba zaki iya ba Khadeeja?’
PAGE 137
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Ta tsagaita da kukan sai dai hawayenta ya kasa daina fita; ta sa bayan hannunta ta goge hawayen ta kalli Mommy suka hada ido na dan lokaci. Ta kawar da kanta tace ‘Mommy ban san me Mustapha yake so da ni ba. Bayan ya gama raina min hankali lokacin da yana neman aure yanzu kuma duk da ban bashi matsala ba amma ba zai barni na zauna lafiya ba.’
Ta share mata hawaye tana cewa ‘Me yayi miki kuma.’
‘Mommy nace masa ina so ranar da za akawo amarya na taho nan idan sun gama kaita sai na koma ya hana ni, na hakura nace zan zauna amma ba zan yi taro ba; su kawo amaryarsu kawai su tafi. Da farko har ya yarda amma yau yake gaya min wai babarsa tace zata zo a nan gidan namu zata yi biki, kuma yace ba zan tafi na barsu ba. Mommy so suke bakin ciki ya kasheni? Dansu zai yi min kishiya kuma suzo suna celabrating a gaba na?’
Da mamaki Mommy tace ‘Ikon Allah, ita mahaifiyar tasa ce zata yi biki saboda zai kara aure?’
Ta sa hannu ta goge ragowar hawayen da yake kan fuskarta sannan tace ‘Eh Mommy, wai zasu zo suyi biki. Kin ga kenan nace ba zan karbi amarya ba amma zasu yi min dole.’
Mommy ta kama hannunta ta kalleta sannan tace ‘Kiyi hakuri kin ji, zaki iya. Kishiya bata kashe kowa ba in sha Allahu kema ba zata kashe ki ba. Ki bi su a hankali, dare daya ne ayi ya wuce. Da an kwana biyu itama zata zama kamar ke kuma yanda yayi miki haka zai yi mata.
Ta jijjiga kai tana murmushi mai dauke da ma’anoni tana cewa ‘Hmm! Mommy ba zai taba yi mana adalci ba. Kina ganin yanda tum kafin ta shigo shi da yaransa da ‘yanuwansa suka karkata wajenta. Gaskiya ban saka rai Mustapha zai iya yi min adalci ni da matarsa, sai dai kawai nace Allah ya bani hakuri ko kuma ya kawo min mafita mafi alkhairi.’
‘kada ki damu, ai ba shi yayi kansa ba, in sha Allahu Allah ba zai bari ya cutar dake ba daga shi har ‘yanuwan nasa gaba daya.’
‘Hmmm!’ ta sunkuyar da kai tana kallon yatsinta da take wasa da su.
Jimawa kadan tace ‘Mommy bana son ayi min biki a gida, bana son a akwo min maryarsa ace za a bani amanarta ko ayi mana fada tare. Amma kinga duk sun shirya hakan zasu yi.’
PAGE 138
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Mommy ta sake kamo hannuwanta duka biyun ta kalleta suka hada ido sannan tace ‘Kada ki damu, kamar yanda na gaya miki na ranar ne kawai. Kuma kema ‘yan uwanki zasu zo, duk da kince kada azo da yawa toh yayayrki zasu zo da kamar mutum hudu haka. Nabila kuma tace gobe zata taho ta tayaki kwana zuwa lokacin da zasu gama bikin. Kada ki damu in sha Allahu omai zai wuce.’
Haka suka zauna Mommy tayi ta bata baki har zuwa yamma. Ta samu zuciyarta tayi sanyi amma dai bata da tabbacin ko zata iya dauka, ta dai hakura taga yanda zata kaya kamar yanda Mommy tace.
Sai da yamma sanna ta shirya ta koma gidan zuciyarta cike da wasi-wasi.
Washegari ‘yan uwan amarya suka zo suka yi kafi. Basu ja fitna ba don haka lafiya aka rabu, ta sa Hafsa ta mika musu kuloloin abincin da ta bayar aka dafa musu; don ita tunda suka shigo gidan ta haye sama kuma har suka gama bata sauko sun hadu ba. Sun tura Hafsa taje ta kirawota sau ba iyaka amma haka hafsan take dawowa tace musu saman a rufe yake. Haka suka gama kafinsu suna ta rangada guda, ga turare da suka bade gidan dashi. Sai da suka kusan gamaw sannan yara suka dawo daga makaranta, nan da nan suka shige cikinsu da yake sun saba da kannenta saboda yawan zuwa gidansu da suke yi.
……….
Dawowarsu daga gidan kafi yayi daidai da dawowarta daga wajen lalle, a zaune ta samesu a farfajiyar gidan ana ta hirarraki. Ta dubi yayarta Ummi tace ‘Yaya har kun dawo daga kafin?’
Ta tabe baki tace ‘Hmmm! Mun dawo’
Ta dan kalleta da alamar tambaya tace ‘Ya naga kina yatsina fuska? Komai dai ya tafi dai-dai ko?’
Salma wadda cousin dinta ce tace ‘Um babu laifi. Amma fa mu a kasa Mustaphan ya nuna mana daki guda daya da parlor yace nan ne naki kuma a nan mukayi kafi. Saman gidan nan ma dai ‘yar mulkin uwargidan taki bata ko bari mun hau ba ta ja kofa ta rufe don bamu ko isa ta sauko mu gaisa ba ta aiko mana da kulolin abinci kamar wasu mayunwata.’
Ta zmburi baki ‘Ban gane a kasa ya baku daki ba? Ai ni sama mukayi da shi kuma ya amsa min a kan haka.’
‘To ai kuwa dai bai isa ba don Hajia Babba ta haye sama, bata ko saukowa idan bata bawa bako mahimmanci ba.
PAGE 139
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Nan da nan idonta ya kawo kwalla, ta mike ta daga waya ta nufi cikin gidan. Ba tare da bata lokaci ba Yaya Ummi ta mike ta bi bayanta. A daki ta sameta har ta lalubo lambar Mustapha zata buga. Ta dafe wayar tace ‘Ba sai kin kirawoshi ba domin karya kawai zai yi miki ya sake bata miki rai, alamu dai sun nuna itace mai gidan. Kada ma ki daga hankalinki a kan wannan maganar balle ki hanaku morar satin amarcinku, don in kika hana muku wannan kwankin to kin yi mata alfarmane don ita zata so haka. Ko da ma kunyi magana da shi din ki nuna masa babu komai.’
Ta kalleta tana zumbura baki tace ‘Yaya babu komai fa kika ce? Ai ba haka muka yi da shi ba. Tun lokacin da ya sayi gidan fa muka je dashi nace sama nake so kuma ya amince, shine zai je kuma ya canja magana.’
Tayi murmushi tace ‘Kika san me aka yi masa ya canza? Wannan mata duk da ban ganta ba amma na san a shirye take, idan bamu dage ba zuwa zaki yi ki zama ‘yar kallo don da alama tana shimfida mulki yanda ranta yake so.’
‘To yanzu ya za a yi?’
Tayi murmushi ‘Kada ki samu zan yi magana da Inna, dama kin ga tunda aka fara maganar bikin nan take faman nemar miki taimako. Kin ga yanzu sai a mayar da hankali ayi aikin da zaki hada kan gidan ki mallake a sauke miki ita daga benen kuma a cireta daga zuciyarsa gaba daya.’
‘Anti dama fa bata zuciyarsa gaskiya, don gaskiya hakuri kawai