Showing 78001 words to 81000 words out of 417803 words
tana mai cije lips ɗinta.
Ita kuwa Khausar kai ta gyaɗa mata tace.
“Eh Mommy karatu nakeyi, gobe Idan Allah ya kaimu zamu fara Exam ɗin First term, lokacin ai ya tafi amma Mommy lafiya na ganki haka?”.
Ta ƙare mgnar tana kafe mata ido.
Ya mutse fuska Mommy tayi tare da lumshe Idanunta still cikin na damƙarta tace.
“Wallahi cikina ke ɗan min ciwo Khausar”.
Cike da tausayawa Khausar tace.
“Cikin ki kuma Mommy?”.
Kai Mommy ta gyaɗa tace”.
“Eh”.
Ita kuwa Khausar ajiye takardan hannunta tayi tare da tsirawa mahaifiyarta ta Ido cikin tausayawa tace.
“Mommy kodai in faɗawa Abba Azo atafi Asibiti ne?".
Kai Mommy ta girgiza kana tace.
“A'a ai beyi tsanani har haka ba”.
Kai Khausar ta gyaɗa tare da sauƙe numfashi tace.
“Toh Allah ya sawwaƙe”.
Mommy da hannunta ke dafe asaman cikinta still Idanunta na lumshe tace.
“Ameen”
Miƙewa Mommy tayi ta koma kan 3sitter ta kwanta kamar minti biyu da kwanciyarta ta sai kuma sake miƙewa ta zauna tana yamutse fuska.
Ita kuwa khausar cikin yanayin damuwa tace.
“Sannu Mommy kode in Kira Abba ne?”.
Girgiza kai Mommy ta kumayi sannan tace.
“A'a tashi ki koma ɗaki nima yanzu zan shiga na kwanta”.
Girgiza kai Khausar tayi tace.
“A'a Mommy Zan zauna dake”.
Lumshe idanu tayi tare da cije laɓɓanta na ƙasa tace.
“Kada ki damu kije ki kwanta na faɗa miki naji sauƙi kuma nima yanzu zan shiga na kwanta”.
Cikin sanyin jiki ta mike kana tace.
“Saida safe Allah yaƙara sauki”.
Mommy ta amsa da “Ameen”.
Ita kuwa Khausar tana shiga ɗaki ta zube akan gadonta tare da faɗa wa duniyar tunanu, a haka bacci ya ɗauke ta kasancewar dare yaja batayi bacci ba ga kuma gajiya.
A ɓangaren Mommy kuwa haka ta kwana cikin mawuyacin hali tare da murƙusoso cikin matsanancin ciwon ciki.
Washe gari.
Da safe bayan Khausar na idar da Sallah tayi Azkhar ta nufi ɗakin Mommy bakinta ɗauke da sallama.
Mommy dake kishingiɗe kan darduma ta ɗago kanta tare da amsa sallamar Khausar.
Kusa da ita Khausar ta tsugunna tare da riƙe hannunta tace.
“Mommy ina kwana ya cikin naki?”.
“Murmushin Ƙarfin hali Mommy tayi kana tace.
“Naji sauƙi Khausar kije ki haɗa muku abin Breakfast kada lokaci ya ƙure”.
Kai Khausar ta gyaɗa kana tace.
“Amma da sauki Mommy kodai daurewa kike yi?”.
Murmushi Mommy tayi tace.
“Eh jeki shirya muku”.
Kai ta gyaɗa sannan ta fice kai tsaye kichen ta nufa.
Tana shiga tasa ruwa kadan atukunya yanda zai wadatar mata bayan ya tafasa ta ɗan zuba mai kana ta zuba Couscous kamar minti goma ta buɗe taga ya dahu yayi sar gwanin kyau, amfanin ɗiga man kenan.
Sauƙewa tayi sannan ta buɗe fridge ta ɗauko miyan stwe da yaji naman kaza ta ɗumama sai kuma ta dauko lunch box din Raudat, Ramadan da Haiydar da kuma nata ta zuba musu, sai kuma ta koma ɗaki tashiga toilet tayi wanka Agurguje ta fito ɗaure da towel mai ɗan girma sannan ta cirewa Raudat kayanta tayi mata wanka bayan sun fito tashafa mata mai kana ta sanya mata Uniform sannan itama ta shirya cikin Uniform da yayi matukar amsar jikinta hannu Raudat taja suka fita dai-dai lokacin da Haiydar suka fito da Ramadan cikin shiri ko wannensu ya nufi inda lunch box ɗin da yake ya ɗauka kana suka fice harabar gidan suka shiga mota.
Kamar ko yaushe motar na parking Khausar ta fito riƙe da hannun Raudat,
Sai da ta kaita ajinsu sannan cikin sauri ta juya ta kama hanyar koma ajinsu daga baya taji ankira sunan ta da faɗin.
“Lelewal ke kullum sai kowa ya riga ki shiga cikin aji ko?”.
Ahankali ta juya tare da sauƙe manyan Idanunta akan Malam Isa dake tsayi murmushi tayi da faɗin.
“Ba haka bane Malam na tsaya kai Raudat ajinsu ne shiyasa”.
Kai ya gyaɗa still Idanunsa akanta hakanan yarinyar ke burgesa ahankali yace.
“To ki tafi kar araba musu questions paper ba kyanan”.
Kai ta gyaɗa tare da juyawa cikin sassarfa da sanin darajar kanta take tafiya har ta isa cikin ajin.
Aɓangaren Amina kuwa koda M Jameel yashiga class da niyyar raba musu questions paper ƙasa tayi da kanta ta amsa batare data kalli fuskarsa ba domin koda gaishesa ne ta dena tunda ta lura da baya buƙata kallon fuskanta, to shima M Jameel Sosai yaji daɗi da yarinyar ta daina gaishesa, dan ko kaɗan baya ƙaunar kallon fuskarta, bare kuma wata magana ta haɗa su.
Acan gida kuwa tun bayan tafiyar su Khausar Makaranta cikin Mommy ya tsananta da ciwo da ƙyar ta yunƙura ta miƙe tana mai rintse Idanunta jini taga yana bin ƙafafunta da sauri ta dafe cikinta da ƙyar ta iya furta.
“Ya Allah wannan ciwon cikin kuma na menene?”.
Da ƙyar taja ƙafanta zuwa jikin beside drawer ta ɗaga wayarta tare da kiran number Hajiya Bunayya, kafin ya katse Hajiya Bunayya tayi picking tare da Sallama.
Mommy kuwa cikin azaban ciwon da cikinta ke mata ta rintse Idanunta kana tace.
“Yaya”.
Da sauri Hajiya Bunayya ta katseta da faɗin.
“Ƙanwata lafiya naji muryanki haka?”.
cike da yarda ta rintse Idanunta cikin yanayin azaban ciwon da cikinta keyi tace.
“Wallahi Yaya cikina ciwo yake tun daren jiya, haka na kwana banyi bacci ba yanzu kuma gashi jini ya ɓalle min!
Dan Allah ki faɗawa Alhj mutafi asibiti”.
Hajiya Bunayya kuwa da damuwa amuryanta tace.
“Subhanallahi! bari na faɗa masa yanzu ma kuwa”.
Sannan ta katse wayar ta nufi ɗakin Lamiɗo ranta fari Sol burinta ya cika abakin ƙofa suka haɗu yana shirin fita.
A take ta wani marairaice fuska kana cikin yanayin damuwa tace.
“Yanzu Mommyn Khausar ta kirani.
Wai jiya da ciwon ciki ta kwana yanzu kuma jini ya ɓalle mata”.
Ai bai ma gama sauraron abinda zata faɗa ba ya ratsa ta ya wuce sashen Mommy cike da damuwa.
Hajiya Bunayya kuwa da harara tabi bayansa kafin taja siririn tsaki ta mara masa baya.
Tana shiga Bedroom ɗin ta samu Lamiɗo tsugunne akan Mommy da sauri ta tsugunna daga gefensa ta riƙo hannun Mommy.
Cike da tausayawa kamar za tayi kuka tace.
“Sannu Aysha ciwon ciki amma baki yi magana ba, gashi har ya tsananta jini na zuba”.
Ta ida maganar zufa na karyo mata wanda in kagani zakayi zaton na tsananin damuwa ce, nan kuwa na tsananin farin cikin burinta ya cika ne.
Lamiɗo kuwa miƙewa yayi tare da naɗe hannun rigarsa zai ɗauke ta Ganin haka ne yasa Hajiya Bunayya tayi saurin miƙewa tare da tallafo Mommy jikinta suka fita,
agidan baya suka zauna Lamiɗo kuma ya shiga gefen mai zaman banza Driver yaja suka tafi Hajiya Bunayya sai faman sannu take yiwa Mommy.
Suna isa asibitin aka karɓe su kai tsaye emergency aka nufa da ita ganin cikin ya riga ya zube yasa likitoci suka nufi wani ɗaki da ita tare da yi mata wankin ciki kana suka yi mata allurai nanda nan bacci wahala ya ɗauke ta Lamiɗo kuwa kasa Matsawa daga kusa da ita yayi ya cike da kulawa ya zauna a bakin gadon tare da riƙe tafin hannunta cike da tausayinta.
Hajiya Bunayya data shaƙa ta cika kuwa.
Wani lalataccen harara ta watsawa ƙeyansa cikin ranta tace, tabbas sai tayi wani abu akan wannan rawan jikin da yake mata.
A zahiri kuwa dafa kafaɗar sa tayi, ahankali ya ɗago kansa ya kalleta da idanunsa dake cike da damuwa amma baice komai ba.
Cike da kirsa ta ƙirƙiri murmushin da bai kai zuciba kana tace.
“Dan Allah ka rage damuwar nan, babu yanda zamuyi da ƙaddara haka Ubangiji ya tsara wannan ɗin ma ba rabo bane, ayanzu addu'ar lafiya take da buƙata awajenmu”.
A hankali ya sauƙe nannuyar Ajiyar zuciya tare da mayar da Kallonsa ga Mommy dake bacci tamkar babu abinda ke damunta.
Lumshe idanunsa yayi yace.
“Ina matuƙar tausayawa Aysha tun bayan haihuwar Haiydar take fama da wannan matsalar sannan ko wanne cikin sai ya wahalar da ita kafin ya fita”.
Da sauri Hajiya Bunayya ta katsesa da faɗin.
“Ya zamuyi da rubutacciyar ƙaddara, ai kaga da Ubangiji yaga dama ai cikin Raudat da Ramadan ya zauna”.
Kai ya jinjina amma baice komai ba.
Ita kuwa cikin ɓoye farin cikinta ta sauƙe ajiyar zuciya da faɗin.
“Zan koma gida kafin ‘yan makaranta su dawo, naga lokaci yaja amma Insha Allah anjima zan dawo”.
Kai ya gyaɗa ba tare da yace komai ba still Idanunsa na kan Mommy.
Hajiya Bunayya kuwa ficewa tayi ranta fari fess kana tasa Driver ya maida ta.
Acan Makarantar su Khausar kuwa koda suka gama Exam ba abasu damar tafiya ba bayan sunyi sallar la'asar suka shiga haddar Alkur'ani sai ƙarfe biyar aka tashe su, kana suka shigo mota suka nufi gida, motar na parking Raudat ta fice da gudu ta nufi sashen su
Tana shiga falo ta fara kiran.
“Mommy! Mommy!! na mun dawo”.
Jin shiru yasa ta nufi Bedroom ɗinta da gudu ta buɗe ta shiga tana kiran.
“Mommy!, Mommy!!, Ina kika shiga”.
Still Bata ganta ba da gudu ta juya ta fito falon dai-dai lokacin Khausar kuma ta shigo ƙara sawa kusa da Khausar tayi ta riƙe hannunta kana tace.
“Addah Khausy Ina Mommy?”.
Kallonta Khausar tayi kafin tace.
“Bata ɗaki ne?”.
Kai Raudat ta gyaɗa mata alamar Eh,
Sake hannunta Khausar tayi kana ta nufi kichen ta buɗe wayam tagani alamar bata nan komawa tayi ta shiga Bedroom din ta ɓude still ba tanan jikin toilet ta nufa ta manna kunnenta ajiki tare da faɗin.
“Mommy Mommy kina ciki kuwa?”.
Jin shiru yasa ta tura ƙofar toilet din still bata nan fitowa tsakiyar falon Khausar tayi tare dasa hannun damanta ta riƙe ƙugunta tana tunanin ina Mommy ta shiga haka, bayan tasan bata fiye fitar yamma ba kuma koda zata fita tun safe kafin su tafi makaranta zata faɗa musu bare kuma yau da suka barta bata jin daɗi.
Da sauri ta kalli Raudat sai kuma tace.
“Jirani anan ina zuwa”.
ta faɗa tare da ficewa kai tsaye sashen Hajiya Bunayya ta nufa bakinta ɗauke da sallama tana faɗin.
“Ummah”.
Shigar ta yayi dai-dai da lokacin da Hajiya Bunayya ke riƙe da waya tana cewa.
“Kedai Hajiya Lami bari buƙata ɗaya ta biya saura ɗaya, tana can kwance a asibiti cikin ya zube yabi makwarari, saura ɗayan daman jira nake inga ya zata kaya ne ki shirya jibi zamu koma”.
Komai Hajiya Lami ta faɗa ohon musu, ita dai Hajiya Bunayya cikin jin dadi ta kece da wata mahaukaciyar dariya mai nuni da tsantsar farin ciki.
Lokaci ɗaya kuma dariyar nata ya tsaya ganin Khausar tsaye, sai kuma ta katse kiran tare da kallon Khausar.
Kafin tace wani abu Khausar tayi saurin cewa.
“Ummah ina Mommy mu?”.
Hajiya Bunayya ta wani langwaɓar da kai kana tace.
“Ayyah Khausar am Mommy ku tana asibiti bata da lafiya wallahi cikinta ya zube”.
Da sauri Khausar da kanta ke ƙasa ta ɗago ta kalli Hajiya Bunayya tana sake maimaita kalmar cikinta ya zube akasan ranta lokacin ɗaya hawaye masu zafin gaske suka cika kwarmin Idanunta.
Sai kuma tayi saurin maida hawayen ta kafin tace.
“Shikenan ɓuƙatar magauta tabiya hankali ya kwanta. Allah ya raya mata wa anda ta haifa. Ubangiji ya tsaresu daga sharrin mai sharrin”.
Ta ida maganar tana ƙoƙarin fita.
Da sauri Hajiya Bunayya tace.
“Ke Khausar zo nan Me kike nufi?”.
Anutse Khausar ta juya tare da sauƙe manyan Idanunta da suka sauya launi zuwa ja ta zubawa Hajiya Bunayya kana tace.
“A'a Ummah babu abinda nake nufi, kawai dai addu'a ce nayi”.
Cikin tsuke fuska Hajiya Bunayya ta watsa mata Harara da faɗin.
“Sannan su waye ne Magautan?”.
Ware hannu Khausar tayi tare da faɗin.
“Nikam ban sansu ba, amma dai nasan Allah Mabuwayi gagara Misali ya sansu kuma zaiyi maganin su, domin ai bahaushe yace rana dubu ta ɓarawo rana ɗaya ta mai kaya, suji tsoron ranan da Ubangiji zai musu kamun talala!”.
Cike da Mamaki Hajiya Bunayya tace.
“Wai Khausar me kike magana kamar habaici kike min ko kuma hannunka mai sanda!?.”
Ware ido Khausar tayi tace.
“Haba Ummah in Miki habaici kuma ayanda kike ƙaunar Mommyn mu kinfi ƙarfin habaici ko hannunka mai sanda kin wuce haka sai dai mgnar ce tazo kamar zaurance”.
Ɓoyeyyen Ajiyar zuciya Hajiya Bunayya ta saki domin tayi zaton yarinyar ta gano lagonta ne.
Khausar kuwa murmushi tayi tare da faɗin.
“Bari na tafi asibitin kar dare yayi”.
Da sauri Hajiya Bunayya ta gyara zamanta Idanunta akan Khausar tace.
“Toh kibari in ƙara sa abinci mana sai ki tafi dashi”.
Kai Khausar ta gyaɗa da faɗin.
“Toh amma bari na shiga gidan Aunty Ruƙayya kafin ki ƙarasa”.
Kai Hajia Bunayya ta gyaɗa tare da faɗin.
“Toh ki gaisheta”.
Kai kawai Khausar ta gyaɗa Sannan ta wuce sashen su.
Tana shiga Bedroom direct toilet ta wuce ta cire Uniform ɗin ta sannan ta watsa ruwa bayan ta fito ta dauki dogon rigar material pinch colour ta sanya, kana ta nufi kichen Agurguje ta dafawa su Haiydar jollof ɗin shin kafa da yaji bushesh-shen kifi da kayan ƙamshi nan da nan kichen ɗin ya ɗauki ƙamshi Warmers ta ɗauka ta juye sannan ta tafasa musu tea kana ta ɗura musushi, sannan ta fita falon dai-dai lokacin da Haiydar ya shigo.
Kallonsa Khausar tayi tare da kiran sunansa tace.
“Haiydar”.
Ya amsa da.
“Na'am”.
Cikin sanyi tayi ƙasa da muryanta tare da faɗin.
“Dan Allah Haiydar ka kwana anan kai da Ramadan, Raudat kuma zamu tafi da ita asibiti sai mu kwana da Mommy”.
Kai ya gyaɗa mata sai kuma yace.
“Nima ai inaso naje na dubata”.
Jinjina kai Khausar tayi tace.
“Ba damuwa kazo mutafi dukan mu amma yanzu zan fara shiga gidan Aunty Ruƙayya in sanar mata, idan yaso kai da Ramadan ku taho tare da Ummah,
In yaso sai ku dawo tare amma kubar min Raudat dan zamu kwana tare”.
“Toh shikenan Allah ya bata lafiya”.
“Ameen”,
Tace kana ta juya ta tafi har ta kusa fita ta sake juyawa ta kalli Haiydar dake tsaye Ahankali tace.
“Dan Allah Haiydar ka kula, bakomai za'a baka kaci ba, akwai abinci na dafa muku sannan duk wani abu da zaku buƙata akwai”.
Da sauri ya dafe kansa tare da faɗin.
“Ke dai jeki da rashin yard
[7/13, 6:07 AM] AMINA KABIR CAPS: 📝✨💫⏰🤴🏻👹❤️❤️❤️🍇
*SAKAYYAH*
_Page 12_
_NA_
*AYSHA ALIYU GARKUWA*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*Littafin SAKAYYAH na kuɗine wannan Free page ne ƴar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276 saura shafi huɗune kacal ana biyar na gama Free page*
Da sauri Modibbo ya rintse idanunsa, tare da shafa sajensa domin, badan glass dake tsakani ba da akan tattausan sajensa sumbatar zata sauƙa.
Shi kuwa M Jameel cikin sauri ya lumshe idanunsa tare da gyara zamansa yana fuskantar ta da kyau.
Ita kuwa Khausar hannu tasa tare da gyara zaman ɗaurin ɗan kwalinta, sai kuma ta canza Baitin da take ji zuwa.
Waƙar Lamba tana marming tamkar zabia kai kace itace ta raira waƙar, bin baitukan takeyi tana jujjuya manyan idanunta, tana mai girgiza jikinta zuwa ƙugunta.
lumshe manyan Idanunta kumayi tare da fitar da sautin zazzaƙar muryanta a fili ta tace.
“Kai zan yiwa kalamaina.
Kai zan baiwa muƙamai na. Ungo makullaina ka riƙe.
Ta ida bautin tare da nuna saitin fuskar Moddibo da yar yatsarta ma nuniya.
Wani irin shu'umin murmushi M Jameel ya sake tare da sa hannunsa ya riƙon hannun Moddibo da ya yunƙura zai ɓalle karfin motar.
Ita kuwa Khausar, cikin azama taci gaba da bin waƙar cike da zazzafan shauƙi tace.
“Ni ban furta da wasa ba, samari dukka basu kai ba, kana nan banganin kowa da ido, dan basu isheni kalloba”.
Tayi mgnar bisa alamu daga ainihin cikin ranta take bin waƙar, M Jameel kam murmushi yakeyi cike da shauƙi.
Modibbo kuwa ya cika yayi fam dan har ransa yakeji yarinyar ta tarainashi gani yake kai tsaye ma dashi takeyi, gashi kuwa M Jameel ya riƙe masa hannunsa ƙam-ƙam.
Ita kuwa Khausar mazari uwar rawa, ƙugunta da ƙirjinta take motsawa a slowly tana mai ci gaba da cewa.
“Kai zaka zauna adamana, kuma ka bani gurin kwana, wannan shine fassarar mafarkin da nake kullum cikin baccina”.
Wani irin yar-yar Moddibo yaji tsikar jikinsa na tashi domin suna jinta ras kasan cewar Glass ɗin bayan motar a suna ƙasa kaɗan.
Ita kuwa Khausar
ida baitin tayi tana mai nuna Moddibo dake kwance jikin kujeran Idanunsa alumshe da yatsan hannunta tana murmushin dake ƙarawa fuskarta kyau.
Shi kuwa Moddibo Cikin fushi ya fuzge hannunsa daga riƙon da M Jameel yayi masa tare da sanya tattauaan tafin hannunsa da niyyan buɗe motar.
Shi kuwa M Jameel cikin sauri ya riƙe tafukan hannunsa da ƙarfi tare da girgiza masa kai alamar ya bari suga iya gudun ruwanta.
Ƙwafa Moddibo yayi tare da jingina bayansa da jikin kujeran ya cigaba da kallonta.
Ita kuwa rawanta ta cigaba dayi tana Girgiza jikinta ganin abin nata ba mai ƙare wa bane yasa Moddibo buɗe motar cike da tsananin fusata.
Kamar walƙiya ko wanda ya diro daga sama haka taga Moddibo a gabanta,
Cikin tsoro, mamaki, da kiɗima kalli fuskarsa cikin zare ido ta tayi ƙasa da kanta,
domin bata tsammaci da mutum aciki ba.
Shikuwa Moddibo cikin nutsuwarsa da kuma kamala ya fito daga motar tare da tsaida idanunsa akanta yana mai ƙara tsananta suƙe fuskarta da ya ƙara razanata.
Ita kuwa cikin tsananin ruɗu da tashin hankali mara misaltuwa ta ɗaura hannunta akai.
tare da zubewa akan gwiwoyinta tana mai girgiza kanta gaba ɗaya ta gaza cewa komai.
M Jameel kuwa gefen Driver ya buɗe tare da fitowa yana dariya mai sassayan sauti,
dai-dai lokacin da Ummi da Asma'u suka fito daga cikin gidan zuwa harabar gidan.
Idanu Ummi ne suka sauƙa akan Moddibo da M Jameel kafin kuma ta maida ganinta kan Khausar dake durƙushe ta kama kai da hannunta duka biyu,
cike da mamaki asaman fuskarta Ummu tace.
“A'a ikon Allah Khausar lafiya ya dai haka!?”.
Kasa cewa komai Khausar tayi, still hannunta na kanta haka zalika ta kasa ɗago kanta banda bugawa da ƙarfi babu abinda zuciyarta keyi da ƙarfi.
Ganin Ummi da tambayar da take yiwa Khausar yasa Moddibo basarwa kamar baisan da ruwan ɗigon Khausar dake tsugunne gabansa ba,
cike da nutsuwa da kuma takun ƙasaita ya janye ƙafarsa da ya ɗaga da niyar zaiyi wasan ƙollo da Khausar ɗin yana mai maida fushinsa ya haɗiye ya juya ya nufi gaban Ummi.
Murmushi Ummi tayi Idanunta akan Moddibo tace.
“Sannun ku da zuwa Babana, dama yanzu nake shirin zuwa unguwa zanje duba jikin Maman Khausar”.
Ta ida mgnar