Showing 3001 words to 6000 words out of 11824 words
zata burge har yayi mararin kaita gidansa matsayin mata.
Tunda Ruƙa'a tayi wannan furucin ga ɗiyarta kuwa ya zamana duk wata dama da Samha take da ita a baya ta ƙwace mata ta rasa masoyin gaskiya, duk wanda zaice yana sonta sai taji bata sonsa, duk kuma wanda taso sai yaji bai sonta haka taketa rayuwa tsayin shekara goma kenan gashi a lokacin sai Allah ya jarabceta da tsananin soyuwar kaɗaici da namiji a babu wands zai kulata babu wanda take burgewa bare ko saɓon ne su aikata ta rage zafi da wannan lokacin da ta gama karatu ta samu aiki sai ta duƙufa wajen binciken hanyoyin kashe sha'awa, bayan tayi nasarar kashewa kanta sha'awane sai ta koma binciken alaƙar jini da sha'awa wanda har yanzu take kansa bata fasa ba kuma bata cimma gaci ba kullum abinda bincikenta yake bayyana mata samun kusanci da me irin wannan damuwar ta sex abuse shine kawai zai bata damar kammala bincikenta, gashi iyakar petiant ɗin da take gani a ɓangarenta bata taɓa katarin haɗuwa dame irin gigitacciyar sha'awar da zata ce irinsa ne zatayi bincike akansa ba, da wannan ta tattara ta aje binciken har Saida Dr Junaid ya nemeta da bincike makamancin wannan sannan ne ta kuma fadaɗa research ɗinta still dai yanzun ma kulleta yayi da cewa sai ta samu namijin da ya kasance cikakken HARIJIN da ya kasance a yini yana iya kwanciya da mace sau goma tsayin dare baiyin bacci, da irin wannan jinin ne zatayi bincikenta ya bata result ɗin da take nema.
Kamar yanda suka saba yau ma basu samu wata karɓa gurin Ruƙa'a ba haka suka gaggaisa a daddafe suka sanar da ita abinda ke tafe dasu tayi musu biris ba tace komai ba har Saida Jadda ta tashi ta fice Samha ta matsa gabanta cikin tsananin tausayin kanta da irin mugun fushin da mahaifiyarta takeyi da ita akan ta bi tafarkin da ta amince shine tafarkin gaskiya, kama ƙafar Mom ɗinta tayi tace “Idan zan rinƙa yin komai babu albarkarki Mom bazan taɓa ganin daidai a rayuwata ba, na roƙeki ki daina fushi dani ki rayu dani kamar yanda kika rayu da mahaifina, Meyesa shi kika yarda dashi kika soshi kuma kika zauna a ƙasansa matsayin mata har kuka samar dani, Meyesa Ni zaki kasa yafemin kuskuren dana aikata Miki zaman ƙuruciya"......
Tureta tayi cikin hargowar bala'i tace kar ki kuma zuwa inda nake Ruth matuƙar baki koma bin addinin da nakebi ba, matuƙar baki koma addinin gargajiya ba to babuni babu ke har abada, Meyesa kowa ɗiyansa na gadonsa amma ke kina bin tafarkin son zuciya, me kike samu a Musulunci shima Abie ɗin naki me ya samu a cikinsa banda mutuwa babu kwarjini....." Miƙewa Samha tayi cikin tsananin zafin zuciya idanunta na zubda hawaye tace “Ko zaki daina amsa sunan Mahaifiyata bazan taɓa yin shirka ba ba kuma zan taɓa bin addinin gargajiya ba" tana faɗin haka ta fice a fusace Ruƙa'a ta biyota tana cewa “Eh naji Nima daga yau Ruth karki ƙara zuwa inda nake kuma karki kuma kallona a matsayin uwar data haifeki kuma a wannan tafiyar da zakiyi Rabat zaki haɗu da ƙaddarar da zata addabi rayuwarki sai kin rayu cikin rashin yanci a matsayin me iko sai kin gwammace ki rayu a yanda nakeso da ki rayu a yanda kika zaɓa"....
Sudai basu kulata ba domin sun fuskanci Ruƙa'a kullum ƙara dulmiya takeyi, haka suka shiga motarsu suka nufi gida, babu abinda yake cin zuciyar Samha kamar sunan Ruth da mahaifiyarta take kiranta dashi, koda sukaje gidan bata da wata walwala duk sanda ta kaɗaice kalaman mahaifiyarta na dawo mata, tunda dake da Mom bata taɓa ma rayuwarta kyakkyawan fata ba.
Idan ya tuna wannan abin sai kuka ya ƙwace mata haka zata tottoshe bakinta don kada kakarta me sonta tajiyota haka a daddafe ta wayi gari da safen juyi tayitayi a gadon tunani da dama suna zuwar mata wasu suna ce mata ta haƙura da wannan tafiyar bakin da Mahaifiyarta tayi wannan tafiya tata mai girma ne wata kuma tana faɗa mata kar ta soma komai yana faruwa ne cikin rubutun Allah, idan Allah bai hukunta mata abinda Mom ta furta ba bazai Sameta ba domin ba zunubi ta aikata ba..........
*👑 HARIJIN SARKI 👑*
*Oum Hairan*
*Regular 500, VIP 1k, V-VIP 2k via 9031307566 Fauziyya Tasiu Umar Opay Evidence of payment 09031307566*
*Ga masu son a tallata musu hajojinsu ƙofa a buɗe take zamu tallata muku kasuwancinku cikin aminci da rahusa, kudai ku tuntuɓi wannan number 09031307566.*
https://arewabooks.com/u/oumhairan1
*Page 5-6*
Wayewar garin tazo mata da wani yanayi na sanyin jiki da mutuwar gaɓoɓi tunda tayi sallah take zaune saman sallaya batasan me takeyi ba addu'a ko kuma zaman banza, 5:45am wayarta ta fara rurin neman agaji Miƙewa tayi cike da zullumi ta sani mutum ɗaya ne me kiranta yanzu domin kuwa shine suke da alƙawari dashi, shi ɗin ne kuwa ta danna accept yace “Ina kofar gidanku jirgin mu zai tashi shida da rabi ne Samha" amsa masa tayi da “to Yallaɓai" ba wani ɓatawa kanta lokaci tayi ba shigar tayi ta gargajiya ta gyara gashinta ta yafa mayafinta a kafaɗarta ta ɗauki jakarta da trolley bag ɗinta ta fito ta ishe Granny zaune bisa sallaya ta rusuna s gabanta ta dafa kanta tare da sanya mata albarka ba tare da tayi furuci ba ta haɗe hannunta alamar fatan alkhairi ta mike ta fito janye da trolley bag, can nesa da farfajiyar gidan nasu ta hangi motar da Dr Junaid yake ciki ta ƙarasa ya fito ya buɗe mata motar ta shiga shikuma yaja trolleyn yasa a but yaja motar suka tafi.
Suna tafe suna yar hirarsu har suka je filin jirgin saman suka zauna a mazauninsu babu jan lokaci jirgi ya ɗaga zuwa Rabat, zuciyar Samha cike zullumin da ta kasa sanin dalilinsa, takas da rabi suka sauka motar asibitin tazo ta ɗaukesu haɗuwa da tsaruwar asibitin shine yafi komai ɗaukar hankalinta ta sauke ajiyar zuciya a hankali lokacin da shugaban asibitin ya miƙo mata hannu sukayi musabiha tare da nuna farin cikinsa da samun ƙwararriya kuma jajirtacciyar ma'aikaciya irinta, wadda ta sadaukar da rayuwarta da lokacin don rayuwar al'umma, da wannan suka rankaya suka isa katafaren office ɗin nata ta kalli office ɗin ta kuma Kallonsa ta ƙara kallo a ranta tace “Barakallah" files files ya ɗebo daga ma'ajiyarsu ya kawo mata gabanta ya zare guda ɗaya ya mayar dashi gurin daya ɗebo waɗancan ya zauna yana mata bayanin komai dalla dalla duk ta gane me yake cewa abinda takeson sani meye dalilin zare wancan file ɗin meshi ya mutu ne ko kuwa akwai wani bayani ne na Musamman a kansa" tambayar da tayiwa Zuciyarta kenan tana me kallon sashen da file ɗin yake.
Dr Razeen ne ya fahimci inda hankalinta ya karkata ya koma ya ɗauko files ɗin yace “Kullum zuciya tana inda aka kangeta da zuwa Dr Samha wannan file ɗin ba na kowa bane face na wani babban mutum a garin nan wanda yake da matuƙar daraja, shi wannan mutumin ya kasance yana fama da wani irin ciwo bauɗaɗɗe kuma ɓoyayye, yana ɓoye ciwonsa a cikin izzarsa yana bayyana ƙarfinsa a cikin rauninsa saidai kuma abin kullum ƙara cin tura yakeyi, wannan mutum Mai daraja ya kasance lamba ɗaya a babbar masarautar nan ta ZIRKAN wato mai Martaba Sarki Rashid Ibn Fayyad Al Zirkan"
Ɗagowa tayi da sauri ƙirjinta na bugawa tace “Sultan Rashid Ibn Fayyad Al Zirkan?" Jinjina kai yayi yace “Ko kinada labarin matsalarsa ne?" Girgiza kai tayi tace “Bansan komai game da duk wani abu daya shafi Rabat da Qasr al-Malik ta Zirkan ba, Ni mutum ce me son bincike akan tarihin masarautu da abinda ya shafi masu madafin ikonta, shin zan iya samun ƙarin sani a wajenka Yallaɓai?"
Numfasawa yayi yace "Ok ki bi a hankali zakisan komai Samha" da wannan ya fice bayan ya maida File ɗinnan gurin daya ɗaukoshi cike da rashin kuzari ta fara duba tulin files ɗin dake gabanta, kowacce damuwa dai irin wacce ta baro a Fess ce babu wata sabuwa, kwantar da kanta tayi bisa kujerar tace “Ya Allah!" Lumshe manyan idanunta tayi taci gaba da juyawa bisa kujerar, sabon gurin aiki sabon bincike sabon labari, tabbas Zuciyarta ta kwaɗaitu da son sanin wani abu game da wannan file da akace mata na Sultan Rashid ne zataso sanin meye abinda yake damunsa wanda yake ɓoyeshi a cikin ikonsa yake lulluɓw rauninsa da isarsa tabbas sai tasan meye wannan.
Da wannan ta tashi tayiwa kofar office ɗin nata key ta zagaya inda file ɗin yake takai hannu ta ɗaukoshi ta koma bisa kujerar ta ta zauna, ruhinta na gargaɗinta buɗe wannan file Zuciyarta na umartarta da buɗewa haka tayi ƙarfin halin yarda da shawarar Zuciyarta ta buɗe file ɗin ta kuwa zabura ta miƙe da sauri ganin wani irin jan haske ya fita daga jikin takardar farko dake bisa file ɗin take taji wata murya tana cewa da ita, "Barka da shigowa Masarautar Zirkan ƙarƙashin mulkin Sultan Rashid Ibn Fayyad Al Zirkan, tunda kika buɗe wannan kundi dole sai kin kai kanki gareshi yake wannan ƙwararriyar likita me karambani, kar kiyi tambaya ki tafi kai tsaye, Masarautar ZIRKAN tana hsmadargudu maso gabashin Morocco, inda rana ke da zafi kuma iska ke kaɗawa da ƙura me ɗauke da danƙo na turare.
Masarautar ta samo asali daga zuriyar Idrisawa, amma yanzu ana mulke da ita da sabon sarki wanda ya fito daga reshen zuriyar da aka manta da ita shekaru aru-aru, Qasr al-Malik ta Zirkan tana tsakiyar birnin Amzir, ta cika da Marmara fitilun zinariya, da fale-falen Andalusian blue tiles.
A cikin fadar akwai zauren manyan baki (Majlis al-kabir) inda akewa mutane jawabi. Gidan Sarki inda iyalansa ke rayuwa fadar Harem wurin matan Sarki da ƴaƴan sarauta, yake wannan Ƙwararriyar likita kiyi sani wannan bayani ina miki shine don haska Miki hanyar tunkarar shafin ƙaddarar da kika buɗo da hannunki, dole Zakije fadar Zirkan zaki haɗu da kaddarori masu kyau da marasa kyau, tunda kika buɗe wannan kundin ƙaddara kin shirya"...........
*👑 HARIJIN SARKI 👑*
*Oum Hairan*
*Regular 500, VIP 1k, V-VIP 2k via 9031307566 Fauziyya Tasiu Umar Opay Evidence of payment 09031307566*
*Ga masu son a tallata musu hajojinsu ƙofa a buɗe take zamu tallata muku kasuwancinku cikin aminci da rahusa, kudai ku tuntuɓi wannan number 09031307566.*
https://arewabooks.com/u/oumhairan1
*Page 7-8*
Shuuuu...... Kamar ɗaukewar ruwan sama taji wannan murya me amon sauti irin na sadaukai ta ɗauke, Zuciyarta taci gaba dayi mata luguden dukan data fara tun farkon buɗe file ɗin, jikinta na rawa irin ta wanda ya haɗu da bazata ta rashin tsammani tare da juyawar kai da tunani a lokaci guda. Daƙyar kamar wacce aka jonawa shorck aka cire ta iya jan jikinta ta ɗaga hannunta cike da firgici ta rufe wannan File ta kai hannu ta ɗaukeshi a ɗan karfafe ta nufi inda yake ajiye tun farko ta ɗorashi ta koma ta zauna bisa kujerarta tayi tsaiii cike da zullumi fargaba da tashin hankalin wannan abu da aka sanar da ita daga buɗe File, ta kasa taɓuka komai duk lakar jikinta ta tsinke haka ta yini a wannan office hatta petiant ɗinta yau gani take musu na wanda yake bukatar a ganshi shima.
Fahimtar idan ta cika takurawa gangar jikinta wani ciwon zai iya ratsa garkuwarta ya sabbaba mata kai juriyarta ƙasa yasata Miƙewa daidai lokacin da agogo ke buga huɗu da kwata, ƙofar ta buɗe tana shirin fitowa ana turo ƙofar tayi baya da sauri jikinta na ɗaukar wata rawa saboda shigar idanunta cikin na wani ƙasaitaccen mutum me fuskar mazan fama wanda yake sanye da kaya irin na Mafarauta fuskarsa a ɗaure tamau kamar tasowar hadari, ta ratse ta bashi hanya ya shiga yana ƙarewa office ɗin kallo Tsaf ya sauke idanunsa a kan Samha da yanayin mutumin ya firgitata, amma ta dake don nuna jarumtarta, takowa yayi a sannu a hankali ya iso gabanta yace “Gaisuwa da fatan alkhairi yake wannan ƙwararriyar likita tabbas ɗazu muna zaman fada Sultan ya ganki cikin idanunsa saƙo yazo masa kamar yanda yazo masa, an tabbatar masa warakarsa na hannunki kamar yanda kema duk ƙasar Morocco shi kaɗai ne zaki samu sakamakon bincikenki a tattare dashi, ya umarceni da na taho dake Amzir yanzu domin ki bashi maganin matsalarsa"
Ja tayi da baya da sauri, wannan mutum yayi murmushi me nuna izza ya shafa gashin bakinsa yace “Sunana Yadam babban hadimin Sultan Rashid muna bukatarki tabbas muna buƙatarki sannan zamu ninka Miki albashinki" janyewa tayi, wasu siraran hawaye na shirin zubo mata tayi saurin tarewa a gun ta kuka rauni ne bata son sakar rauninta ga kowa, da wannan tace “Zan.... Zan iya neman izini a wajen shugabanni na?" Jinjina mata kai yayi ta kuwa fice da sauri yabi bayanta.
Office ɗin Dr Razeen suka shiga yana ganinta ya miƙe idanunsa yayi ja ya nunata da yatsa yace “Meyesa kike da taurin kai da rashin bin umarni? Saida nace Miki Karki buɗe wannan kundin bayanai amma Saida kika buɗe, me zan iya yi Miki Samha? Banda abinyi a gareki, hatsarin dake tattare da wannan file yasa ban haɗa Miki dashi ba ke kuma kikaga hakan baiyi Miki ba tabbas kinyi ganganci kinyi kuskure" rikicewa tayi da kalaman Dr Razeen tace “Wlh banyi tsammanin akwai wani ɓoyayyen duhu cikin wannan file ba, na ɗauka shima Normal rashin lafiya ce, don Allah Yallaɓai....." Ɗaga mata hannu yayi yana kallon fuskar Yadam da ke kallon agogon hannunsa yace “Lokacinki ya ƙare Likita Sultan baison jira" kallon Dr Razeen tayi da yayi ƙasa da kanta hawaye ya shirin zubo mata tace “Dama haka aiki A babban Asibitin ƙasa yake rayuwa da rashin ƴanci rashin zaɓi da rashin makoma, indai hakane Yallaɓai na haƙura da aikin gabaɗaya zan cike takardar barin aiki...."
Murmushi Yadam yayi yace “Idan kikayi hakan zamuji daɗi kuma zamu gasƙata kinsan aikinki dama aiki biyu a lokaci guda bazai yiwu gareki ba" kallon Yadam tayi ta kuma kallon Razeen cike da sallamawa ta juya ta fita da sauri, Yadam ya riƙo hannunta ya nufi wata mota ya buɗe ya sanyata a ciki ya shiga, yana shirin tada motar Dr Razeen ya iso ɗauke da wannan File ya ɗora mata a cinyarta ta ɗago suka haɗa idanu ya ɗaga mata hannu cike da tausayin wannan aiki me wahala data ɗaukowa kanta, koda yake zataji daɗi a lokacin da tsoro ya saketa ta gane ɓangaren da takeson yin bincike akai ne, da wannan Yadam yaja mota suka lula titi Zuciyarta cike da saƙe saƙe tare da kudurcewa a ranta zatayi aikin ne kawai in taga zata iya idan bazata iya ba kuma zata barshi ta kama harkar gabanta.
A hankali sautin Muryar ɗazu ya fara dawo mata cikin ƙwaƙwalwa, zata je ta tunkari ƙaddarar data buɗota da hannunta, zata haɗu da kaddarori mai kyau da mara kyau, to wacce irin ƙaddara ce a cikin duba mara lafiya? Gabanta ne yabada wani dam lokacin da Muryar ta dawo mata tana sanar da ita Yanada matan aure uku yanada Kwarkwara huɗu daga ketowar alfijir zuwa faɗuwar rana yana kwanciya da dukkanin matan nan nasa guda bakwai kuma kowacce mace saita fita daga hayyacinta sannan ake fitowa da ita wata ta shiga, yanzu haka matarsa ta aure ɗaya ta mutu hakama Kwarkwara ɗaya saboda wahalar da sukesha wajen kusanci dashi".........
Shigarsu Emirates Road ya dawo da ita hayyacinta gurin iyakar hasashe bazai fasalta haɗuwarsa ba an ƙawata gefe da gefe da tsakiyar titin da manyan bishiyun dabino masu kyau waɗanda akayiwa kwalliya da fenti kala kala masu burge ido da ƙawata zuciya An zuba shimfiɗun carpert don takawar me tafiyar kafa ga wasu manyan fitilun zinariya da Andalusian tiles sai ɗaukar idanu sukeyi kamar a masallacin Alhambra, iya wannan titi aka Barka da kallo to shakka babu zaka nemi damuwa a zuciyarka ka rasa domin duk wata nau'i na damuwa zai ɗauketa.
Kowacce kusurwa ta wannan Titi soji ne da dukkan wani nau'i na jami'an tsaro suke gadin wannan Daula, wata katafariyar ƙofa da iya bayani bazai wassafawa mai karatu haɗuwarta ba, nan Yadam yayi Horn Sarakan ƙofa suka buɗe suka shiga nan Samha ta tabbatar da ita yar ƙauye ce haihuwarta a Fes ba yana nufin itan wayayyiya bace domin kuwa kanta juyewa yayi saboda kallon wannan alatu da ke narke cikin wannan gida na sarauta.
Sunyi tafiya me tsayin gaske daga farkon wannan get aka kuma buɗe wani suka shiga aka kuma buɗe wani suka kuma shiga, cikin na ƙarshen harda Roundabout haɗaɗɗe wanda aka ƙawatashi da wata haɗaɗiyar takobi, sukayi wani shataletale suka kuma nausawa sannan suka shiga Fadar Harem wadda anan ne Sultan da iyalansa suke zaune, tunda suka shigo wannan area ta Iyalan Sultan suka fara cin karo da Barori bayi da kuyangi sunata kai kawo gashinan gini ne sashi sashi a wajen bayan an wangame musu ƙaton get ɗin sun shiga kenan, nan ma basu tsaya ko ina ba Saida suka dangana da wani ɓangare aka sake buɗe musu get suka shiga wayyoh Allah aljannar duniya.
Tuni Dr Samha ta manta da wata damuwa ta dolen da akayi mata na zuwa wannan fada ta farajin a ranta lallai itan zaɓaɓɓiya ce cikin zaɓaɓɓun bayin Allah da ta kasance a wannan guri, parking Yadam yayi ya kalleta yace “Ma iya shiga likita, babu musu kuwa ta fito domin ta matsu taje ƙarshen gidan. Takawa suka farayi tana rungume da file ɗin da Dr Razeen ya bata da kuma system ɗinta suka fara tattaki abinda ya bata mamaki babu kowa a harabar wannan guri, wata haɗaɗɗiyar ƙofa da aka ƙawata adonta da zallar ruwan gold da Azurfa suka nufa suna zuwa Yadam ya taɓa Bell sau ɗaya ƙofar ta buɗe suka shiga ciki wani irin haske ne me saukarwa da zuciya nutsuwa da kasala haɗe da wani sirrintaccen ƙamshi me kashe zuciya da sanyi me sanya bacci suka ratsa gangar jiki da ruhin Samha ashe ba nan kallo yake ba Saida suka ratsa suka shiga wani parlourn shima yana yafi na baya a haka Saida suka ratsa parlour uku a na huɗun ne Samha ta daidaita nutsuwarta jiyo Muryar wata mace tana ihun neman agaji tana kuka tana faɗin wallahi