Showing 102001 words to 105000 words out of 114909 words
haɗa kansa da sitarin ya rufe ido,
Jikin Ringing ɗin wayarsa yayi yawa yasa ya ɗago ya ciro wayarsa daga aljihu daf da zata katse ya danna picking
“Hello Momy”
Yanayin muryarsa ya tabbatar mata yana cikin damuwa,
“Na'am ya mai jikin?”
“Alhamdulillahi”
“Idan ka fito kazo gida”
“Toh Momy”
Ya daɗe kamin ta kashe wayar, key yayi ma motarsa ya soma tafiya a hankali, lokaci lokaci yake shafa gashin kasa zuwa wuyansa ya sauke ajiyar zuciya, gida ya nufa kamar yadda Momy tace masa, bayan yayi parking ya daɗe cikin motar sannan ya fito ya nufi cikin gidan.
Kallo ɗaya Momy tayi masa ranta ya kara ɓace sam bata son taga ɗanta cikin damuwa dan tafi kowa shiga damuwar,
“Momy ina kwana”
Ya faɗa yana kokarin zama, sai da ta zauna sannan ta amsa basa
“Lafiya kalau dan Allah karka sa kanka a damuwa da yawa zata samu sauki”
Kai kawai ya daga mata yace
“Ina lil Minal?”
“Tana can ɗakin Lubna muje dinning kaci abinci”
“Momy bana jin zan iya cin wani abu”
Bata matsa masa ba ta tashi ta nufi ɗakin Lubna bata daɗe ba ta fito ta nufi dinning. Ba a jima ba Lubna ta fito ɗakinta ɗauke da lil Minal ta nufo shi, lil Minal na ganin Abban ta ta fara zillo
“Pah pah pah”
Haka take faɗa tana kokarin mika kanta ya dauke ta, hannu ya mika ya karɓe ta cike da tausayinta ya rungume ta ya lumshe, wani irin tausayinta ne ya lulluɓeshi,
“Karɓi ga tea ka sha”
Maganar Momy ce tasa ya buɗe ido sai ya sauke su kan kofin tea, daga bisani yasa hannu ya karɓa, kaɗan ya kurɓa ya ajeye, Momy ta zauna kusa dashi cikin damuwa ta kalleshi
“Ita fa rayuwar duniya komai ɗan'hakuri ne jarabawa kala kala akan yi ma bawa da sannu sai kaga komai ya wuce, ni banga abun ɗaga hankali a wannan ciwon nata ba insha Allah zata ji sauki”
Iskar bakinsa ya busar
“Momy baki san yadda nake ji Kairat bane, na rasa Huda na rayu na rasa Minal na rayu Kairat kan dana rasa ta nima za'a rasa ni, Momy tun jiya yarinyar nan bata san inda kanta yake ba gashi su kuma sun kasa gano mi yake damunta”
“Kayi ta addu'a Allah zai bata lafiya”
“Ina fatar hakan amman Momy har fa ciki ne jikinta ina tsoron lamarin nan”
“Ka bar komai a hannun Allah shi zai maka magani zata samu sauki insha Allah”
“Allah yasa”
“Amin”
“Ba zaka ci abinci ba ka daure ka ci ko kaɗan ne”
“Ba zan iya i ba Momy bana jin yunwa”
“Da dai ka daure”
“Ba zan iya ba Momy”
Duk yadda Momy taso ya ci abincin ki yayi dan sam baya jin yunwa baya ma sha'awar wani cin wani abu,
A wunin ranar haka ya wuni in banda ruwa babu abunda ya kai bakinsa, a ɓangaren lil minal ma haka ne dan bata sha komi aka bata sai ruwa sabo da nono gashi ba a koya mata shan komai ba, bai koma asibitin ba sai dare ba kuma komai yasa haka ba sai dan baya son ganin halin da matarsa take ciki. A hankali yake tafiya lil Minal na lafe a kirjinsa tayi lamo kamar wanda tasan abunda yake faruwa.
A bakin kofar ɗakinta ya tararda Doctor tare da wasu, fuskarta ba yabo ba fallasa ya mika ma doctor hannu suka gaisa,
“Idan ka shiga wannan shi ne shiga na karshe da zaka kuyi dan anjima kaɗan zamu fara aikin mu idan kuma mun fara kuda ganinta sai a window”
Likitan ne yake faɗin hakan yana kallon Saif fuska da fuska, kai kawai ya iya ɗaga masa ya sauke ajiyar zuciya ya tura kofar ɗakin ya shiga jiki a sanyaye, Mummy ya gani zauna saman kujera ta saka Kairat a gaba tana kallonta sai hawaye take wasu na bin wasu, Hajiya Suwaiba da Abbah na daga gefe suma ita suke kallon ko wannensu fuskarsa ɗauke da damuwa dan Hajiya Suwaiba kaɗan ya rage hawaye bai zubo mata ba, cikin kararriyar murya ya gaishe su, Abbah kawai ya iya amsawa dan Mummy bata ma shigo ba, Hajiya Suwaiba kan tana buɗe baki tasan kuka ne zai fito,
Karasawa yayi kusa da ita ya zagayo ɗayan ɓangaren, bai kula kowa ba ya mika hannu ya riko hannunta ya ɗago shi yayi masa kiss, sannan ya sake kai hannunsa ya shafa fuskarta, Mummy kan sai surutai take mata kamar wanda ke son zautowa,
“Dan Allah ki tashi Kairat kinji Mummy ba zata iya rayuwa ba ke ba, komai kike so zan miki ke kaɗai kika rage min”
Da kuka ta karasa maganar ta jingina kanta saman gadon, Abbah ɗauke fuskarsa yayi Hajiya Suwaiba kuma ta gumɗe baki kar kuka ya fito mata, Hannu Saif ya kai ya sake rike hannun nata gam tana dantsar baki, lil Minal kan sai bachinta take dan tun yana tsaye bakin kofa bachi yayi gaba da ita daman jikin nata kamar a mace yake, jin ta matsa hannunsa yasa ta kalleta da sauri sai ko yaga idonta a buɗe tana kallonsa, bana jin yasan lokacin daya risina a gurin yana kiran sunan ta, hakan ne ya hankaltarda su Mummy da Abbah suma suka kalleta, kallo Mummy tayi tare da kiran sunan ta murya kasa kasa kamar wanda aka taushe ma sheɗa,
“Mu.. mmy...”
“Na'am Kairat na'am na'am”
Da sauri Mummy take amsawa har bata iya tsayawa ta sauke numfashi, ɗauke kai tayi ta kalli Abbah da Hajiya Suwaiba sai kuma ta rufe ido kamar mai bachi, ta ɗauki kusan minti talatin a haka bata sake yin koda motsifa balle ta sake buɗe idon, ga dai numfashi tana yi amman ba magana ba alamunta, duk sukayi tsit kamar ba kowa ɗakin. Bayan kamar minti biyar likitoci suka shigo ɗakin tare da Nurses, ɗayan likitan ne ya nemi su Abbah da su fita, Hajiya Suwaiba ce ta fara fita Abbah ne na biyu sai Saif, Mummy kan daker ta fita daga ɗakin.
A cikin Mota Saif ya rik'a rusa kuka kamar wani mace, har kukan nashi ya tashi lil minal daga bachi ta soma masa kuka, rarrashinta yayi daker ya samu ta koma bachin,
*** *** ***
Washe gari, bayan ya dawo daga sallah asuba, ya hau gado ya kwanta kasancewar jiya baiyi bachi ba kwana yayi nafisa yana nema ma matarsa lafiya gurin Allah, bachin nasa bai yi nisa ba ya soma jin kukan Lil Minal, kamin yayi wani yinkuri yaji kukan bakin kofar ɗakinsa,
“Wanene?”
Ya tamabaya jin ana buga kofar
“Nice”
Lubna ta amsa tana jijjiga lil minal, tashi yayi ya buɗe kofar ya karɓe ta
“Mi kika mata”
“Ban mata komai ba Momy ce tasa ayi mata ɗure madara tun shekaran jiya ba komai a cikin ta”
Kai kawai ya ɗaga mata ya maida kofar ya rufe ya shiga jijjiga ta saman kafaɗarsa,
“Mah mah mah”
Kawai take kira har bachi yayi gaba da ita, saman gadon sa ya kwantar da ita ya lulluɓeta da bargo, ya ɗauki jacket ɗinsa yasa, yana kokarin fita wayarsa tayi ringing, ya daɗe yana kallon screen ɗin ganin bakuwar number, sai da tayi ringing har ta tsare aka kara bugowa sannan ya ɗauka,
“Gani nan a waje ina son ganinka akwai magana mai muhimmanci da zan faɗa maka”
“Wanene”
“Idan ka zo zaka gani”
Dih dih dih..... Kiran ya katse, ya daɗe yana tunani sannan ya saka wayar aljihu ya fice.
A harabar gate ɗin ya fito yana tunani har ya isa gakin gate ɗin, daker securities suk barshi ya fita wai saboda tsaron lafiyarsa duk da haka sai da wasu sojoji uku suka raka shi cikin farin kaya, ganin ba kowa a waje yasa ya ciro wayarsa ya kira number ana ɗauka yace
“Ina kake gani a waje”
“Ina nesa da gidan ku kasan ba'a bari mutun ya karaso ba tare da izinin ku ba”
Kashe wayar yayi ya fara tafiya suna binsa a baya, ganin tafiyar ba mai karewa bace yasa ɗayan sojan ya shiga gaba dan basu yarda da wanda inda zaije ba, ɗayan ma babu yadda baiso ya ki tafiyar ba wai ya kira mutum ne yace ya karaso amman Saif yaki dole suka kyalesa, a sannu suka fara hango mota fake gefen tt da bakin glass, sai da Saif ya kusa karasowa kusa da motar sannan ya fito daga motar sanye da farin yadi ya dora rigar sanyi a sama, Saif na ganinsa ya ya kalli securityn yace
“Za ku iya komawa nasan shi”
“No Sir just keep walking zamu tsaya a nan amman ba zamu koma ba”
Cigaba yayi da tafiya har ya isa gurin,
“Ya akayi”
Shine abunda Saif ya faɗa yana yi masa wani kallo, sai da ya rungume hannayensa sannan ya kalli Saif yace
“Baka bukatar waɗannan mutanen i won't hurt you”
“Ba shi na tambaye ka mike tafe da kai”
“Kan rashin lafiya Kairat ne”
Kallon tsaf Saif yayi masa,
“Kamar ya me ka sani akan rashin lafiyarta”
“Safiyyah ce musabbabin rashin lafiyarta, adalilin asirin da tayi mata, shin kasan dalilin warke war da Safiyyah tayi ne ya jefa Kairat cikin halin da take ciki yanzu”
Cikin rashin fahimta Saif ya kalleshi
“Ban gane ba ya akayi kasan da hakan?”
“ba zan faɗa maka ba yanzu amman ina son kaje ka samu Safiyyah da Shafa kayi musu wannan tambayar sune zasu faɗa maka hanyar samun lafiyar matarka”
“Safiyyah bata da lafiya bana jin zata iya yi min wata magana a yanzu”
“Ta samu lafiya idan kaje gida ka bincika”
Yana kaiwa nan ya buɗe motarsa har zai shiga sai kuma ya ɗago ya kalli Saif
“Sai dai kuma Kairat na samun lafiya zaka rasa Safiyyah”
“Deen.....”
Saif ya kira shi
“Idan na tararda labarin ba haka bane fa”
“Ka kashe ni”
Kai tsaye Deen ya bashi amsar, Saif ya sake cewa
“Miye dalilin ka na faɗa min wannan maganar?”
“Saboda Minal.....”
Cikin wata irin kalar murya ya karasa maganar ya shiga motarsa ya bar wajen, sai da Saif ya daina hangosa sannan ya juyo cike da Tunani ya nufo gida.
MI KUKE TSAMMANI GABA?
FEW PAGES REMAINING INSHA ALLAH 😊
Keep voting and commenting one heart ♥
56
Part ɗin Momy ya nufo, zuciyarsa cike da sake-sake saman kujera ya zauna yana shafa kansa, wani tunanin yazo masa, wayarsa ya duba ya shiga nema number Safiyyah, ya daɗe yana nazari kamin ya danna calling,
Dauke wayar yayi daga kunnensa bayan sun sanar masa da number tana kashe, Number Lubna ya kira ita kan ta shiga sai dai tayi ta ringing har ta kashe ba'a ɗauka ba, sai a kira na biyu ta ɗauka ta muryar bachi
“Hello Yaya”
“Sauko gani nan parlour”
Yana faɗar hakan ya kashe wayar, yana mai cigaba da nazari, ta ɗaukar kamar minti biyar zuwa takwas sannan ta fito sanye da kayan bachi ta ɗora top sama, kusa dashi ta zauna tana hamma
“Yaya gani”
Kallonta yayi a natse
“Ya za'ayi naga Safiyyah yanzu? Kin san inda Gwaggo ta kai ta gurin magani?”
“A'a amman yanzu ai tana gidan Gwaggo kaje can zaka ganta”
“Sun dawo ne?”
“Eh sun dawo tun jiya ko shekaran jiya oh jiya, oh na dai mata amman taji sauki fa”
Gyara zamansa yayi cike da mamaki yace
“Taji sauki”
“Eh baka sani ba, maybe dan hankalin ka ba kwance ba yasa Momy bata faɗa maka ba amman taji sauki gaskiya”
Shiru yayi yana tunani,
“impossible”
Da karfi ya furta har Lubna ta kalleshi
“Lafiya yaya?”
Kallonta yayi
“Da gaske taji sauki kin ganta da idonki?”
Tashi yayi yana faɗin
“Lafiya kalau i need to see her”
A gaggauta ya fice daga parlour, da kallon mamaki Lubna ta bishi har ya fice sannan ta tashi ta nufi ɗakinta, part ɗin sa ya koma ya ɗauki keys ɗin motarsa ya nufi parking space, yana shiga motarsa ya ɗauki hanyar da zata sada shi da gidan Gwaggon sa, a bakin gate ɗin gidan ya fara tsayawa yqna tunanin idan ya shiga me zai ce mata! Ka fara shiga ka fara gasgata zancen Luban tukuna, a nan ya danna horn, mai gadin ya buɗe masa, har kusa da kofar yayi parking, ya fito ya nufi kofar parlour, bell ɗin gidan ya tsaya bakin kofar yana kallon Windows ɗin parlour,
Sai da ya danna yafi a kirga sannan aka buɗe masa kofar, wata matashiyar yarinya ce sanye da uniform,
“Ina kwana Yaya”
Bai tsaya amsa gaisuwar nata ba ya kunno kai cikin parlour yana faɗin
“Ina Gwaggo?”
“Tana ɗakinta bari na kira ta”
Ta faɗa bayan ta maida kofar ta rufe ta nufi ɗaya daga cikin ɗakunan tana karanta, kamin ta karasa Saif ya kirata
“No Farida zo ba sai kin kira ta ba”
Da wowa tayi tazo daidai shi ta tsaya,
“Gani Yaya”
Dukowa yayi tq yadda ita kaɗai zata iya jin mi yake faɗa yace
“Ina Safiyyah?”
“Tana ɗakin su Husna”
“Taji Sauki?”
“Eh taji sauki haukan ya cire”
Shiru yayi kamar mai nazari, sannan ya sake kallonta yace
“Samo min biro da Paper”
Da sauri ta juya nufi wani gurin da ina jin an tana deshi ne don aje bags dan bags ɗin suna da yawa, wata ja naga ta ɗauko ta nufo inda yake ta zauna ta bude ta fiddo littafi ta ɓalli paper ta ciro biro ya mika masa,
“Thanks”
Ya faɗa yana kokarin karɓa, a nan ya shiga rubutu a paper ya dunkule ya mika mata tare da bironta,
“Ga wannan ki ba Safiyyah idan ta tashi bachi kinji?”
“Toh tafiya zakayi?”
“Eh kice ma. Gwaggo ina gaida ta”
Yana kaiwa nan ya juya ya nufi kofar fita. Ya daɗe zaune cikin mota bayan ya isa gida, sai da lil Minal ta faɗo masa a rai sannan ya fita daga motar ya nufi Part ɗin sa, yadda ko yake tsammani haka ta tashi daga bachin sai kuka take tana kiran
“Mah mah mah”
Tana bursar da yawu, murmushin karfin hali yayi ya mika hannu ya ɗauke ta
“Yeee kin tashi yar mama”
Kara fashewa tayi da kuka, ya shiga jijjiga ta ya fito ya nufo part ɗin Momy, dinning ya nufa gurin da ya hango su Momy suna breakfast, Momy ta mika mata hannu
“Zo ki sha tea”
Juyar da fuskarta tayi ta kara fashewa da kuka, Saif ya ɗanyi Murmushi yaja kujera ya zauna yana faɗin
“Momy ina kwana”
Momy ta amsa cike da jindaɗin ganin yau ran nasa a sake ba kamar baya ba duk da idan ka kalleshi zaka gane yana cikin damuwa,
“Momy ai bata manta ɗorin da kika sa akayi mata ba”
Murmushi tayi, ta shiga haɗa ma Saif tea,
“Momy anjima Safiyyah zata zo ko da bana nan dan Allah a kira ni”
“Miya faru?”
Momy ta tambaya daidai lokacin da ta aje masa tea gabansa,
“Wai Safiyyah tana da hannu cikin rashin lafiyar Kairat shine nake son na tabbatar”
“Inji wa kuma wannnan wace irin magana ce haka”
“Nima haka tazo min sai dai ban tabbatar ba yanzu ne ake son na tabbatar”
Momy ta dafe kai
“Wannan abun har yaushe zai kare tsakanin ka da Safiyyah ne? Yarinyar nan daga samun lafiyar ta sai kuma ka ɓullon da wannan abun”
Bai ce komai ba ya kurɓa tea ya tashi yana faɗin
“Zanje Asibiti sai na dawo”
Momy bata ce masa komai ba har ya fice. Ba shi ya dawo gidan ba sai azahar duk da bai samu ganin Kairat ba dan basu barsu ya shiga ba ya window ya tsaya yana kallonta sannan ya dawo gida har lokacin lil minal na lake dake wanka ma daker ya samu ta sauka yayi, yana fitowa ta rarrafa ya ɗauke ta, ɗauke da ita ya saka tufafinsa mai ma bata barshi ya shafa ba turare kawai ya fesa ya fito ya nufo Part ɗin Momy, Mai aikin Momy ce ta karɓe ta da karfi wai za'ayi mata wanka, Saif ko yabi ya ɓata fuska dan baya son jin kukan lil minal ɗinsa, yana kokarin zama Lubna ya fito ɗaga ɗayan parlour tana leken ɗakin Momy har ta karaso kusa dashi ta zauna tana haki, shi dai kallonta yake har ta fara magana
“Yaya Safiyyah ta kira tace ba zata samu damar zuwa ba wai Gwaggo ta hana ta sai ta kara samun karfin jiki, amman Momy tace kar a faɗa maka”
Fuskar tunani yayi da mamaki, sai kuma ya shi da sauri Lubna ta rika hannunta
“Yaya karka ce nina faɗa maka Momy tace bata son tashin hankali, zata iya yi min faɗa”
“Ba zan bari taji ba”
“Toh ina zaka?”
“Gurin ta sai na tabbatar da abunda nake zargi ki kula min da Lil Minal please”
Bai tsaya jiran mi zata sake cewa ba ya fice.
57
Kai tsaye ya shigo cikin gidan, kana kallon fuskarsa kasan wani abun ne ke tafe dashi, Sama sama ya gaisa da Gwaggonsa yana tambayar ina Safiyyah
“Lafiya?”
Gwaggo ta tambaya ganin yanayinsa
“Lafiya kalau nazo gaishe ta ne naji ance taji sauki”
“Eh taji Sauki bari a kira maka ita”
Tashi tayi ta nufi ɗakinta ba ɗan ta bamsu ba komai ɗin ba, dan tasan Safiyyah bata da matsayin da Saif zaizo gaishe ta ɗan taji sauki duk da tana ganin yana tausayin halin da take ciki, amman kuma miyasa tun lokacin bai zo ba sai yau!
Da wannan sake-saken ta tura kofar ɗakin Safiyyah ta shiga. Kofar ɗakin ya tsura ma ido har sai da yaga fitowar Gwaggo,
“Gata nan zuwa”
Kai kawai ya ɗaga mata ta shige ɗakinta, ya sake maida idonsa kan kofar ɗakin da yake saton Safiyyah na cikin dan ɗakin Gwaggo ta shiga, ta ɗan jima kamin ta fito har ya fara tunanin koya tashi ya shiga ɗakin ne, sai gata ta fito sanye da Abaya fara da farin gyale ta lulluɓe kanta, a hankali take tafiya har ta k'arasa kusa dashi, ko wannen su yana kallon ɗan'uwansa, ita tana masa kallon data saba masa sai dai yau ya ɗan babbanta dana kullum, shi kuma yana mata kallon ta iya zai fara! Shi fa har yanzu bai gama yarda ita ce da hannu a