Showing 108001 words to 111000 words out of 114909 words
bai kaita kunnensa ba sai har sai da mai kiran yayi daf da katsewa,
"Ta ya akayi kasan da wannan labarin?"
"Ta amsa laifinta kenan? Ka tabbatar da gake nake ko?"
Aka amsa masa daga ɗayan ɓangaren, bai damu da ba da amsar tambayar da aka masa ba sai ya a kara jaddada tasa tambayar
"Taya akayi kasan da wannan plan ɗin?"
Shima ya ɗan daɗe kamin ya amsa
"Wata rana ne na fito daga kauyen mu, sai na haɗu da motar Safiyyah ita kuma tana kunna kai cikin kauyen, ganin kamar motar dana sani yasa na juya ya rika bin motar a baya har muka raba hanya,
Ta nan ne na hango fuskar Safiyyah kasancewar glass ɗin motor a sauke yake, a haka nayi ta binsu har naga gurin da sukayi Parking, a bakin kofar gidan wani babban boka dake garin namu,
Nayi mamakin yadda akayi Safiyyah tasan da wannan bokon, tunawa da abunda tayi min ta kuma yi ma Minal sai ya kawar da wacan tunanin nawa,
Bayan naga gidan da suka sauka sai nayi tafiya sai washe gari na dawo gurin bokan na zuba masa kuɗi mai yawa, a nan dake sai ya bayyana min abunda ke tafe da ita da kuma abunda ya aikata mata, ban gasgata hakan ba har sai da naji labarin Kairat ba lafiya,
Dana je gurin Mummy dan sanar mata sai na tarar hankalinta a tashe yake bata ma saurare na balle ta fahimci me nake nufi, nasan kai kaɗai ne mafita wanda zan faɗa ko da ba zaka yarda da ni ba,
Sai dai nasan wata rana zaka gasgata ni ka kuma yarda ada abunda na faɗa"
Lumshe ido Saif yayi, lokacin da Deen ya kai aya a bayanin sa, sannan ya sauke ajiyar zuciya ya tasa leɓensa ya ce
"Thank you"
Deen bai kara ce masa komai ba ya kashe wayar,bayan kamar minti biyar wani kiran ya kara shigowa, ba tare daya duba mai kiran ba ya dannan picking yasa hands free,
"Kana ina Saif?"
Muryar Nasir ce hakan ya tabbatar masa da shine ya kira ko da ba number sa bace, ya ɗn bata lokaci kamin ya amsa
"Ina gida"
Wayar ya tsurawa ido bayan katse kiran, har lokacin zuciyarsa cike take da ɓacin rai.
Sai da Nasir ya kare masa kallo sannan ya zauna kusa dashi yana faɗin
"Lubna tace min kayi faɗa da Momy miya faru?"
Ba tare daya kalleshi ba ya amsa
"Bata faɗa maka dalilin faɗan ba bata ce maka mi nayi ba?"
"Bata ce min ba, ta dai kira ta faɗa min"
Sai a lokacin Saif ya kalleshi ya soma labarta masa abunda ya faru, dan abokin dariya ba'a ɓoye masa kuka, shiru Nasir yayi yana nazarin lamarin, bai ga. Laifin Saif ba ko kaɗan itama Momy ya san zafin rai ne ya haddasa tayi haka, kallon Saif yayi ya sake kallonsa damuwa ce kwanace a fuskarsa wanda ke nuna ta zuciya tafi wannan yawa, koba komai yasan yadda Saif ke gudun zuciyar Momy baya son ganin ɓacin ranta sam, kuma hakan kan iya haifar da ɓacin ran Abbah, Hannunsa kan kafaɗar Saif ya ce
"Ka kwantar da hankali i will talk to her"
"Ba zata saurare ka ba, idonta a rufe yake a yanzu ta kasa fahimta ta saboda Safiyyah, bata dubi halin da nake ciki da kuma wanda zan shiga"
"That's Why nace zan yi magana da ita Just have a faith zamu samu mafita"
Kai ya girgiza masa, shi kuma ya tashi sai shima ya tashi suka fito tare, shi ya ɗauki hanyar gidan Momy shi kuma ya nufi asibiti,
Yana yin parking Lubna ta fito ta tarbershi, sai da suka kawo kofar shiga parlour ta fara masa magana kamar mai raɗa,
"Momy ba zara saurare ka ba Ya Nasir, ko ta saurare ka ba zata fahimci abunda kake so ta fahimta ba, nima ɗazu akan hakan sai da ta tashi mari na"
Ya ɗan zaro ido yana kallonta da yar dariya
"Kece kema dakin samu rabon ki, amman ni nasan zata saurare ni"
"Wallahi wahalar da kanka kawai zakayi kila ma kai ma ta kwaɗa maka marin"
Wannan karon dariyar gaske yayi
"Tana ina ne?"
"Tana nan parlour ta haɗe rai sosai"
Har lokacin magana take masa a raɗa wai kar Momy taji, kumatunta kawai yaja ya kunna kai cikin parlour, bayan kamar mintuna bakwai ita ta rufa masa baya.
Har kasa ya risina ya gaisheta kamar yadda ya saba, sannan ya zauna a kujerar dake facing ɗin na ta, cike da fargaba ya soma magana dan shi ma kansa ya tsorata ta ganin yanayinta
"Momy, bai kamata a ce kina fushi da Saif ba, bashi da laifi cikin wannan lamarin kuma ki daina ganin laifin Kairat ita ma bata da laifi Momy Saif shine kaɗan ɗa namiji da kika haifa, baya da farinciki sai naki ya kamata a ce ke ce kika fi kowa fahimtar sa"
Yawun bakinta ta haɗe ba tare da ta kalleshi ta ce
"Kasan wani abu Nasir?, Safiyyah tana sa gaskiya naso kai ma da yawa, da ace Saif ne yake son ta da duk yadda zanyi sai naga nayi wajen ganin ya aure ta, ko ka nasan ba karamin shiga da fita zakayi ba wajen ganin abokinka ya samu abunda yake so,
Safiyyah Marainiya ce Nasir a hannu na ta tashi ya kamata ace na sama mata duk wani farinciki da take bukata, ban taɓa saka ta abu tayi min musu ba, duk abunda tasan yana faranta min itace kan gaba wajen aikata shi, sam sam sam ban kyautawa Safiyyah ba"
"Amman Momy yanzu.... -"
Hannu ta ɗaga masa,
"Ka aje kalaman ka Nasir, nasan kana kokarin kare abokin ka ne"
Bata tsaya jiran komai ba ta tashi ta nufi ɗakin ta, a sannan ya maido kallonsa ga Lubna ta ɗaga masa kafaɗu
"Ai na faɗa maka ba zata saurare ka ba"
Sumkuyar da kansa yayi kasa yana jinjina al'amarin.
Abu kamar wasa sai gashi Momy ta kusan kwashe kwana biyu babu ruwanta da Saif da duk abunda ya shafe shi, babu yadda bai yi amman taki ta kula shi, saboda har yanzu bata daina ganin laifinta ta, a duk lokacin da ta tuna Saif take ɗorawa laifin, gashi tana son zuwa sake duba Safiyyah amman ta kasa, saboda tunanin abunda zata ce mata. A ɓangaren Saif kan jin yake kamar ace masa rai ya huta, dan abun yayi masa yawa, ga matarsa a kwance, har yanzu ba wani sabon labari ga matsalan Momy shi, Mummy ma ta shirya komai da zata ayi aka kaita waje don duba lafiyar ta amicewar Saif kawai ake jira shi kuma ya kasa aiwatar da komai saboda Momy taki tasa baki cikin lamarin, cikin yan kwana biyu nan duk yabi ya rame abinci kirki baya ci iya kacinsa yan ruwan tea ko juice, ita kanta Momy tana tausayin halin da ɗan nata yake ciki ta dai ki nuna masa ne saboda har yanzu bata daina ganin laifinsa ba, dan iya kuskure tasan yayi, amman kuma ya za'ayi abun duk da ya girma ya riga ya gama girma, kuma tun ran gini tun ran zane.
Babu ani gwari a tare dashi haka ya shiga ɗakinta, sai da ya zauna kusa da ita kasan carpet sannan ya kalleta
"Momy an wuni lafiya"
"Lafiya kalau ya jikin matar taka?"
"Da sauki, Luban tace kina nema na"
"Eh akan maganar matar ka ne, shawarar da zan baka ka bar matarka a nan, da nan da can duka ɗaya ne tunda Allah dai shine yake bada lafiya kawai kasa Allah a gaba kayi ta mata addu'a"
Dagowa yayi ya kalleta akaro na biyu, dan bayi zaton jin wannan maganar daga bakinta ba,
"Ina nan ina yi Momy kuma Insha Allah haka zanyi"
"Allah ya bata lafiya"
"Amin"
Ganin ta kishingiɗa yasa shi tashi ya fito daga ɗakin zuciyarsa cike da tambayoyi, kao tsaye ɗakin Lubna ya shiga, bayan ya baro ɗakin Momy, tana zaune tasa plate ɗin abinci gabanta sai aikawa take tana dannar waya,
"Ke"
Ta juyo da sauri ta kalleshi,
"Yaya shigo mana ka tsaya can ko wani abu kake so ne?"
Shigowa yayi, yayi mata tsaye a ka,
"Mi akace da Momy yau"
Dariya tayi,
"Daman nasan sai ka tambaye ni shiyasa ya shigo ɗaki ai, kaga ta canja yau ko?"
Kai ya ɗaga mata,
"Wallahi Daddy ne ya rufe ta da ruwan masifa, yace shi sam na zai ɗauki wannan a gidan nan ba, akan me zata rika maka haka, yace idan har bata tausayin halin da kake ciki ai ta tausaya ma lil Minal,
Yace kuma Safiyyah ita ta jefa kanta cikin mugun hali, ba kuma ba a cilasla maka yin abunda baka tashi ba, yace kuma Safiyyah itace shi take yar'uwarsa ba Momy dan haka babu ruwanta da abunda ya shafe ta,
Daga karshe yace duk abunda ya same ka ita ce kuma ba zai kyale ba, yace duk kabi ka rame ka fita hayyacin ka da wani zaka ji!"
Shiru ya ɗanyi kamin ya ce
"Ke taya akayi kika ji?"
"Nice ma kai ma Daddy gulmar ai"
"Wai daman Daddy bai sani ba?"
"Eah mana, wacan karon ma ai ɗan yaga Safiyyah ta haukace ne shiyasa kaga yayi maka wannan faɗan kuma Momy ce take faɗa masa wai ai duk kaine da laifi"
"Thank you"
Haka kawai ya faɗa ya juya, yana murmushi ya fice.
*** *** ***
Kamar ko yaushe, yau ma ya daɗe yana addu'a bayan ya kare sallah Nafila ta karfe uku da yake yi kullum, ya faɗawa Allah bukatar sa ya kai kukan sa a inda za a share masa, sannan ya tashi jiki ba gwari ya nufi kujerar dake gefen gadon ya zauna, tsare ta yayi da ido, yana tunano yar karamar rayuwar da sukayi a tare, sannan ya kai hannu ya shafa fuskarta da ta bushe, daga bisani ya tura hannubsa cikin nata ya rike yana murza yatsunta a hankali, ajiyar zuciya ya sauke ya jinginar da kansa jikin gadon, jin ta motsa hannunta bai sashi ya ɗago ba dan ba sabon abu bane a yan kwana ki nan takan motsa hannun, amman ba magana ko kuma wani motsin,
"Sa... I.. F"
Cikin wahalalliyar murya ta kira sunan nasa, aiko ba shi ya ɗago da sauri ganin idonta a buɗe yasa shi gwalo nashi idon ya saki baki yana kallon ikon Allah, ita kan sai kallonsa take da dishi dishin da take ganin, da ba dan kashin turarenta ba da kuma. Sanyi hannunsa ba da ba zata iya gane shi ba, daga kwance ta dake ya rungume ta, kamin ya ɗauke cak ya rik'a waliliya da itar tsakar ɗakin, zuwa can kuma ya ajeta ya faɗi yayi ma Allah Sujadar godiya, sannan ya ɗago ya sake rungume,
Ita kan sai kallonsa take tun tana gani dishi dishi har ta fara gani daidai, tayi kokarin ta tunano abunda ya faru amman ta kasa, iya abunda ta sani shine ta daɗe tana bachi, zaunawa yayi saman gadon rumgume da ita kamar wata karamar baby ya rik'a fuskarta
"Kairat kina iya gani yanzu kina iya jina? Akwai inda yake miki ciwo? Meke damun ki yanzu?"
Hawaye ne ya gangaro daga idonsa, hawayen da ba zan iya tantance na minene farinciki ko akasin haka!. Hannu tasa ta shafe masa hawayen tana kallon idonsa, wanda da ita dashi ban san na waye yafi zurfi ba,
"Saif kuka kake yi? Mi ya faru da ni?"
"Zan faɗa miki komai daga baya kawai ki faɗa min mike miki ciwo a yanzu?"
"Babu"
"Kin tabbata?"
Kai ta gyaɗa masa, ya tashi, ita dai kallonsa kawai take har ya fice, be daɗe ba ya shigo tare da wasu likitoci guda biyu, Mummy ce ta uku, tayi mamakin ganin yadda ake mamakin tashinta sai abun ya koma mata kamar mafarki,
_Miya faru da ni?_ shi ne abunda take ta tunano wa take kuma tambayar kanta amman ba amsa, bayan fitar likitocin Mummy ta rumgume tana kuka, tana yima Allah hamdala,
"Mummy miya faru dani"
"Komai ma ya faru dear na gode Allah da ya dawo min dake daidai"
Tana kallon Saif ya sakar mata murmushi, sannan ya zauna saman gadon yama mai lumshe ido da buɗewa, Mummy ta tashi cikin zumuɗi
"Bari na haɗo miki tea ki sha ko kina son wani abun"
"Tea ma is okey"
Cikin sauri ta fita, sai ita kuma ta kalli Saif da fuskar damuwa
"Miyasa aka kawo ni asibiti? Mi ya faru dani ne wai?"
Murmushi yayi,
"Ni kai na bansan abinda ya faru dake ba, ni dai na dawo ne sai na tararda ke kwace a kasa kin dafe ciki baki iya magana, a nan ne sai na kawo ki asibiti daga lokacin sai hankakinki ya bar jikin ki"
Shigowar Mummy ce tasa duk suka kalli kofa, Kairat sai nazarin maganar take dan har yanzu bata gano musabbabin abun ba, Mummy da kanta ta rika bata tea cikin wani irin jindaɗi, Kairat ta lura da hakan, sai tasa hannunta ta rika hannun Mummy, Mummy kuma ta jimke hannun jinjinjin,
"Da ace na rasa ki Kairat da bansan yadda rayuwata zata kare ba"
"Mummy ba zaki rasa ni ba, ki daina tunanin hakan"
Ta shafi kanta zuwa gefen fuskarta, idonta cike da hawaye ta ce
"Ina fatar haka"
Ta ɗauki lokaci a ɗakin, sannan ta ɗauki cup ɗin tea ta fita, Saif kamar ita yake jira ya dawo kusa da matarsa, ya rungume ta.
A jikinsa ta karasa bachin, duk da ba wani bachi sukayi ba. Hasken asuba na fara fitowa su Hajiya Suwaiba suka iso tare da Abbah, daman tun cikin dare Mummy tayi musu waya ta sanar musu, ganin su ne yasa Saif mika ma Mummy cup ɗin tea dake hanmunsa, ya ɗan matsa ba bada space tsakani su, sai Mummy ta cigaba da bata tea shi kuma yana gaisawa da su, Abbah ya kalli Mummy yana murmushi
"Hankali ya kwanta ko Ummu Kairat?"
Murmushin itama tayi, ta shafi kan Kairat, Hajiya Suwaiba sam bata jindaɗin maganar ba sai dai bata nuna masa ba, dan a yadda ta fahimta a yanzu yana son Mummy fiye da tunanin ta, ganin yadda duk damuwar ta ta zame masa tasa, a halin da Kairat take cikin ta fahimci Mummy yafi tausaya ma sama da ƴarsa Kairat. Hajiya ta murmusa irin murmushin da bai kai zuci ba tace
"Yanzu kuma ai kuka da tunani ya kare ko?"
Mummy dai murmushi kawai tayi ta tashi ta nuna ma Abbah kujera, ita kuma ta tsaya daidai Hajiya Suwaiba still tana murmushin,
"Ga kujera a zauna"
Murmushin yayi mata ya zauna yana yi ma Kairat ya jiki,
"Jiki da sauki Abbah"
Ta amsa tana kallon Hajiya Suwaiba dake kallon Mummy ita kuma tana kallonta. Basu jata da fira sosai ba, suna gurin aka kawo mata breakfast daga gurin Momy kamar yadda aka saba, tara saura Saif ya bar ɗakin ganin basa da niyar fita ya nufo gida da zimmar ya sanar da Momy ya kuma yi wanka ya canja tufafi, a part ɗinsa yayi parking ya fito daga motar da zimmar ya shiga yayi wanka amman sai ya kasa zimuɗin sanar Momy yake, haka ya nufo part ɗinta zuciyarsa cikeda farinciki a fuskarsa ma zaka iya gane hakan, dan tun daga nisa Momy ta gane yau ɗan nata yana cikin farinciki,
"Momy ya na ganki da shiri haka? Kar dai ace kinji?"
Ya faɗa lokacin daya karaso kusa da ita hakoransa a buɗe, Momy ta ɗanyi fuskar mamaki
"Naji me? Da wani labarin ne?"
"Yes Momy ba Kairat ta tashi ba"
Ya faɗa yana wani abu kamar yanzu ya soma jin tashin nata a zuciyarsa, jin yayi ba zai iya ɓoye murnar sa ba har sai da ya rumgume Momy, Momy tayi dariya tare da godiya ga Allah
"Alhamdulillahi amman naji daɗin wannan abun, cuta ba mutuwa ba"
"Wallahi Momy tun jiyada dare fa, kar ki so ganin yadda nake jindaɗi"
"Ai na gani kan, gashi nan ya kasa ɓoyuwa a fuskarka, aiko yanzu shirin nan da nayi ina son naje duba ta ne idan na fito gurin Safiyyah"
"Da banyi sauri ba da kin tararda ni a can ashe"
"Lallai kan, bari naje so nake na dawo da gurin akwai bakin da za'ayi daga Europe"
"Okey Momy nima wanka kawai zanyi na koma"
Murmushi Momy tayi, aka buɗe mata motar ta shiga Saif ya maida ya rufe yana mata Allah ya tsare.
Kamar yadda ta faɗa, a harabar gidan su Gwaggo driver yayi parking wani ya fito daga ɗayar motar da sauri ya buɗe mata cikin girmamawa, sauran suka shiga fito da kayanyakin da dace musu a nan zasu kawo, kayan kwalama ne waɗanda tasan Safiyyah tana so, kamar ko yaushe yau ma da sallama ta shiga parlour fuskarta ɗaukeda murmushi duk da Faɗuwar gaba ne a zuciya wanda ita kanta bata sam dalilin sa ba,
Sallamarta da kuma sautin takun tafiyarta kana da kanshim turaren ta shine ya tabbatar mata Safiyyah Momy ce ta shigo,
"Momy..."
Ta kira sunan nata dan ta tabbatar, kasancewar ita kaɗai ce ke parlour, sai da Momy bata amsa ba har sai da ta zauna kusa da ita,
"Na'am Y'ata"
Hannu ta kai tana shafa jikin Momy har ta kai ga fuskarta,
"Momy kece?"
Shiru Momy tayi tana kallonta jikinta a sanyaye, dan ta kasa gasgata abunda idanunta suke gane mata,
"Momy ke ce amsa min magana"
Ta faɗa muryar tana gaf da kuka, Momy ta rika hannunta
"Ba ki gan ni bane safiya"
"Bana iya ganin ki Momy idanuwana a yanzu rufe suke bana iya bambance baki da fari ko kuma haske da duhu, na kan kane kowa neta hanyar murya ko kuma kanshim turare ne kawai amman ba da ido ba"
Hawaye na mata zuba take magana, Momy bata san lokacin da hawayen idanunta suka fara fita ba, ta sauko daga saman kujerar bakinta na rawa ta ce
"Safiyyah baki gani kike nufi? Yaushe makanta ta same ki?"
"Momy bana gani, a yanzu haka ban gani komai sai duhu"
"Innalillahi wa innaa ilaihi raji'un, yaushe wannan abun ya same ki?"
"An kwana biyu yanzu, Momy rayuwa ta kenan haka Allah ya kaddara min nawa al'amarin"
Duk kan su cikin kuka suke maganar, musamman Safiyyah,