Showing 90001 words to 93000 words out of 114909 words

Chapter 31 - Babban Goro By Khadeeja Candy

03 Dec 2025

6119

ba ko wani abun ya faru ne”

Kai ta girgiza alamar a a, mummy tace

“Toh akan me zaki rika kwana ke kaɗai? wannan ai ba ɗabi'ah bace dole ki rika gane gane”

Talatu tace

“Hajiya karfa kiyi latti kinsan kince tara da rabi zaku shiga meeting”

Mummy ta kalli Kairat

“tashi ki ɗauko abu Talatu zatayi ma Lil Minal wanka, ita zata xauna a nan tana kula da ita kamin ki iya yi mata wanka”

Saif ya ɗauki lil minal ya kalli Talatu,

“Muje na nuna miki ɗakinta”

Ba musu ta tashi suka nufi ɗakin. Bayan sun shige Mummy ta kalli Kairat tace

“Kar na sake jin kun rab gado da mijinki sai kace ba wayayi ya ba idan kika saba masa da hakan ke ce zakiyi nadama nan gaba, baki san babu kyau ba? muharraminki ne fa Kairat ɗan Allah karki sake haka kinji?”

Kai ta ɗaga tana kuka mai kamar na shagwaɓa kuma bana shagwaɓa ba.

“Ki rika addu'ah kinji? I will do something about it”

“Toh Mummy amman ba zaki daɗe ba zaki dawo ko?”

“Eh ba zan daɗe ba”

“Promise”

“I promise”

Rumgume Mummy tayi tana wani narkewa jikin mummy kamar zata shige. Saif ya fito daga ɗakin, karaso kusa da su yana kallon Kairat ya taɓe baki.

“Tashi ki jera abincin ku a dinning”

Mummy ta faɗa tana shafa kanta, tashi tayi ta nufi dinning ɗin tana share hawaye. Mummy ta kalli Saif
“Kairat amana ce a gare ka Saif farincikinta shine nawa ka kula da ita sosai kuma kayi hakuri da ita da sannu komai zai zama daidai”

Kai ya ɗaga mata ya tashi tsaye ganin itama ta tashi ɗin. da sauri Kairat ta karaso gurin ta rika hannun Mummy kamar wata karamar yarinya

“Mummy tafiya zaki yi?”

“Eh sai na dawo kinji ki rika addu'ah”

Wani irin ɓata fuska Kairat tayi taji kamar ta bita Saif dai sai kallonta yake har Mummy ta fice, sannan yayi dariya yaja kumatunta.

“Sagarta ko miyasa baki bita ba?”

Rufe fuska ta ɗanyi tana share hawaye. Hannunta ya rika

“Muje mu ci abinci”

Da kansa ya haɗa mata tea ya tura mata gabanta, sannan ya haɗa nashi.


KARFE UKU DA MINTI GOMA SHA DAYA..........

Safiyyah ta digo gidan, da Sallama ta shigo parlour fuskarta ɗauke da murmushi. haɗa baki sukayi da Talatu gurin amsa mata. kallo ɗaya Kairat tayi mata ta ɗauke kai kamar bata san inda ta fito ba.

“Amary bakya laifi”

Ta faɗa tana kokarin xunawa, Kairat dai bata ce da ita uffan ta sai kallon tv take, Talatu kuma na rumgume da lil Minal. Taɓe baki Safiyyah tayi tana kallon Falon

“Yaya na nan”

“Baya nan”

“Ina yaje?”

“Nima bai faɗa min ba”

A tsatsaye Kairat take amsa mata tambayarta still bata kalleta ba. Talatu na ganin hakan ta tashi ta nufi ɗakin da Saif yace mata shine nata.
  Safiyyah ta tsire baki

“Wai ya kike min magana kamar baki san wacece ni ba?”

Sai a lokacin ta kalleta

“Na san wacece ke mana, sheɗaniya kuma makira”

Tashi Safiyyah tayi tsaye

“Wannan wace irin magana ce haka kardai ace kema shaye shayen kike.”

“Asibiti nake sha, miya kawo ki gida na?”

Kyalkyalewa tayi da dariya

“Gidan ki ko gidan yayana daga ganin sarkin fawa sai miya tayi zaki tun tafiya batayi nisa ba har kin fara kiran shi gidan ki?”

“Akwarai gidana ne saboda ni aka auro aka kawo”

“Karki manta kamin ke am kawo wasu, kuma hakan yana tabbatar miki da ana canja mata ba a canja yar'uwa ba”

“Waɗan can, an canja su ne ta wani dalili, ni ko zama daram dam kujerar karfe fita ki bar min gida makira annamimiya”

Wani irin zaburowa Safiyyah tayi kamar zata mari kairat

“Ni ce makira?”

“Eh sunan ki ne ko kin canja wani?”

Tsaye tayi suna kallon kallo akuya kallon kura, ita Kairat, jin parking ɗin motar Saif yasa ta jindaɗi tana jin motsin taɓa kofar palo ta fashe da kuka. cuke da damuwa ya karaso kusa dasu yana tambayar ba'asi

“Lafiya miya faru?”

“Mari na tayi tana faɗa min maganganun banza”

Kairat najin haka batayi wata wata ba ta watsa mata marin sannan ta nuna ta da yatsa

“Ita giwa tafiyar ta bata ɗaya data saura ni makircina a fili nake yinsa kuma babu yadda za'ayi”

Zaburowa Safiyyah tayi zata rama Saif ya rike ta,

“Wai miye haka ne”

Safiyyah kuma dai sai kunce kuncen ta rama marinta take, can Saif ya warguna ta, ya tura ta

“Tafi gida Safiyyah wuce”

Tsaye tayi tana yima Kairat wani mugun kallon sannan ta juya ta fice cike da jin zafin marin da Kairat tayi mata. bayan ta fice Saif ya kalli Kairat rai a ɓace

“Miye haka dan Allah daga zuwanta sai faɗa?”

“Toh waya ce tazo dole ne sai tazo”

“Dole ne tazo mana tunda ɗan'uwanta kike aure kuma ko bata zo dan ki ba xata zo dan lil Minal”

“Bama bukatar ta ni da lil Minal karta sake zo mana gida, bata da wata alaka da mu”

“Ni tana da alaka da ni Yar uwata ce ke kuma matata ce ko wacce matsayin ta daban, tana da yanci ta shigo gidana kamar yadda kike da yancin zama, beside Safiyyah ma ba wata mafaɗaciya ba ce i know her sai dai idan ke kika taɓa ta”

Hawayen dake makkale a idonta ne suka zubo, ta kalleshi

“You take her side”

Kai ya girgiza mata,

“This is not the right time to take anyone side, Kairat bai kamata a ce kin fara wannan halin yanzu ba, duka duka yaushe kika zo gidan nan?”

Bata ce masa komai ba ta juya ta nufi upstairs. Zaunawa yayi saman kujera yana shafa kansa, baya nufin ɓata mata rai sai dai kuma ba zai bata damar ta raina masa yan'uwa ba duk da shi ma ɗin ba son xuwan Safiyyah yake ba, amman ba zai nuna mata ba dan karta raina masa yan'uwa dan da haka ne wasu matan ke samun kofar rai na yan'uwan miji.

     Da dare tana Zaune parlour tana buga Candy Bom a waya. Saif ya fito daga ɗakinsa rike da waya a hannu ya nufo gurin da take zauna ya ya fisge wayar, tana kallonsa yace

“Coffee please”

Tashi tayi ta shiga cikin ta haɗa masa ta kawo masa kallonta yayi a hankali sannan ya mika hannu ya karɓa yana faɗin

“Mummy ta kira ni yanzu tace kin kirata kina kuka kuma baki yi magana ba kin kashe, miyasa kika kirata?”

Zaunawa tayi tana shafa gefen fuskarta

“Ba komai”

Ta faɗa ta murya kamar ta shagwaɓa. gyara zamansa yayi yana kallonta

“Ita gaskiya dole a faɗe ta Kairat, Bana nufin ɓata miki rai kuma ita dole ne na bata rashin gaskiyarta”

Bata ce masa komai ba ta aje remote ɗin hannunta ta ɗauki lil minal ta kalleshi

“Sai da Safe”

Ta tashi ta nufi upstairs. da ido ya bita har ta haye a maimakon yaga tayi ɗakinta sai kawai yaga ta shiga ɗakinsa, Murmushi yayi ya cigaba da kallon yana kurɓa tea a hankali.

      Ba'ayi minti goma da shigarta ɗakin ba yaji ta fasa ihu ya kalli upstairs ɗin

“Oh my goodness”

Ya faɗa yana kokarin aje tea cup ɗin ya tashi ya nufi ɗakin.
    Wannan karon ya tabbatar da gaske Kairat tana ganin wani abu dan yadda ya tarar ana janta tana jan kanta ta rike gado gam sai uhun take, da sauri ya rikata shima tana janta da dukan karfinsa, janta taji ana kara yi sai dai baya ganin mai jan nata ita. komawa a'kayi gurin Hijab ɗinta ana janta da karfi kamar za a fisge mata fuska, cikin sauri ya cire hijab ɗin ya ɗauke ta kamar jaririya ya mai da gefe ya rumgume ta.

   Hijabin aka fisga ya faɗa ta windon baya, Sai sa kallon ikon Allah yake wai yau a ɗakinsa. ita ko sai kamkamesa take tana faɗin

“Saif fitar da ni daga ɗakin nan”

“Okey okey”

Ya faɗa yana kara rumgume matarsa. saukowa yayi da ita downstairs, har lokacin suna rumgume da juna, a palo suka tararda Talatu sai rabon ido take tana ganinsu tace

“Lafiya nake jin ihunta?”

Kai ya ɗaga mata

“Lafiya kalau Baba jeki ɗakin ki”

Ba musu ta shige ɗakinta ba dan ta yarda ba komai ɗin ba, wayarsa ya dake kan kujera ya ɗauka ya shiga dialing wata number. bugu biyu aka ɗauka,

“Shigo ina neman ka”

Haka kawai ya faɗa ya kashe wayar. ya cigaba da shafa ta, ita kuma sai rera kuka take a hankali.
  bayi mintu biyu ba aka buga kofar parlour Saif yace

“Yes shigo”

Yana shigowa ya kalle shi yace

“Ka zaga kai da mutanen ka gurin ita cen nan ku duba min gurin komai kuka gani ku faɗa min”

“Yes Sir”

Ya juya da sauri ya fice. saman kujera Saif ya zauna still yana rumgume da ita sai tunani yake, daker ya samu ta sake shi ta zauna saman kujera amman bata yarda tayi nisa dashi ba dan kunkurunta na gugar nasa sam ta manta da wani abu wai kunya da kuma gudunsa ta take.
   Bayan kamar mintu na arba'in suka sake jin an buga kofar,

“Yes come in”

Saif ya faɗa, a nan mutunen ya turo kofar ya shigo bayan ya karaso ya aje hijab ɗin Kairat da wani kololon abu kamar fatar damisa. wani irin tuma Kairat tayi kamin Saif ya ankaro har ta haye saman jikinsa ta rumgume shi gam.

“Ga abunda muka gani babu kowa a gurin mun dai samu rame sai muka tona shine muka ga wannan”

Mutunen ya faɗa yana kallon Kairat kamar zaiyi dariya kuma bai yi ba,

“Okey jeka dashi can gurin ka idan an tashi zan neme ka”

Tashi yayi ya fice. sannan Kairat ta ɗago ta sauka saman jikinsa. kirjinta ya kalla yana murmushi, sai tasa hannu ta kare gabanta ta ɗan noce kai. taɓe baki yayi a ransa yana

Ba yanzu kika gama rumguma ta ba

Tashi yayi. tana ganin hakan ita ta tashi. Daren kin yarda tayi su kwana ɗaki a dole palo suka kwana, kuma guri ɗaya jikinta na gugar nasa, da taji ɗan motsi ta shige masa. Shi kuma ya samu abunda yake so an ba kura fiɗa. lil Minal kuma ta kwana hannun talatu.

                           ***        ***    ***
     A tare sukayi sallah asuba, suka koma bachi amman wanna karon a ware sukayi bachi dan taga safiya ce sai ta ware kanta can gefe tana bachinta.
   Ringing ɗin wayarsa ne ya katse masa bachi, ganin number Momy yasa shi saurin ɗauka cikin muryar bachi.

“Hello Momy”

Ban ji me akace masa ba na dai ga ya tashi amman gadon yana faɗin

“Okey gani nan zuwa”

Banɗaki ya shiga bayan ya aje wayar ya watsa ruwa ya fito a gagauce ya shirya, ya fisa turare. har ya kai bakin kofa sai kuma ya dawo ya duka a hankali yayi ma Kairat kiss a goshi ya fice.

     
Cikin yan mintuna ya isa gidan bayan yayi parking ya shiga cikin parlour. Ihunta ne ya amsa masa sallamar da yayi ya kalli Momy da hankalita ke tashe yace

“Wai me ya same ta?”

“Wallahi ba mu sani ba, ni dai ina ɗaki naji ihunta shi kenan fa abun har yanzu kuma bata magana sai kuka da ihun nan da take”

Momy ta faɗa kamar zatayi kuka, Hannayesa ya zuba cikin aljihu yana sauke ajiyar zuciya

“Da yaushe abun ya same ta?”

“Jiya da dare misalin shaɗaya na dare”

Tsaki yaja ya nufi ɗakinta yana girgiza kai.



WHO MISS ME? 😢 PLEASE VOTING AND COMMENTING ON EVERY SINGLE LINE


51


Can karshen gefen gado ya hango ta, ta wani kwalo ido jikinta sai rawa yake idon nata yayi wani zurfi kamar wanda ta shekara bata ci abinci ba. Karasawa yayi kusa da ita ya risina, suna haɗa ido ta fashe da kuka

“Safiyyah”

Bata amsa kiran da yayi mata ba babu ma alamun zata iya magana, dan ko kukan da take idon ne kawai yake hawaye, nan take tausayinta ya rufe sh, ajiyar zuciya ya sauke ya kalli Momy

“Yanzu miye abun yi?”

Cike da damuwa Momy tace

“Ina ganin asibiti zamu kai ta muji ko minene”

Kallonta ya sake yi kamin ya taso shi da Momy, A parlour suka dawo ko wannne fuskarsa ɗauke da damuwa, Saif ya ciro wayarsa dake cikin aljihu ya kara a kunne,

“Ya a'akayi?”

“Kana ina?”

“Ina waje”

“Waje?”

“Eh tare da Lubna ba”

Katse wayar yayi, ba ayi minti biyu ba Nasir ya shigo falon tare da Lubna kusa da Saif ya zauna yana gaisawa da Momy, sannan ya tashi ya leka ɗakin Safiyyah,Bai daɗe ba ya fito ya sake zaunawa a inda ya zauna ɗazun yana faɗin

“Anya ba shaye shaye take ba?”

Momy tace

“Nasir Safiyyah bata shaye shaye ban taɓa gani ba.Kin kira Gwaggon taku?”

Ta karasa tana kallon Lubna

“Eh na kira ta tace ga tana nan zuwa”

Nasir ya girgiza Kai

“Idan aka je asibiti ai maji amman ni nasan babu yadda za ayi haka ya kamata ba tare da dalili ba”

“Bance maka babu dalili ba amman ni nasan Safiyyah bata shaye2”

Cewar Momy. Sako naji alamun ya shigo a wayar Saif yana duba ba ya tashi

“Momy bari naje naga wani, idan kunje asibitin duk yadda akayi sai ki kirani a waya”

Kai kawai ta ɗaga masa ya taso shi da nasir suna tattauna maganar.

     Two Hours Later
Ya nufo gida bayan yayi fakin ya nufi kofar falon, tsayawa yayi yana dannan bell ɗin gidan kamar wani bako, buɗe kofar da tayi yasa ya ɗago kai daga duniyar tunanin da yake ya kalleta. sanye take da katon hijab idonta ya ɗanyi jan, fuskarta kuma ta kumburo alamar tayi kuka. ido ya sakar mata kamun ya kai hannu ta rika fuskarta

“Me kuma ya same ki na kuka? mi ya faru?”

Janye fuskarta tayi ta juyo ya shigo cikin falon,

“Ba komai”

Ta faɗa tana kokarin zama,

“Kinyi breakfast?”

Ya tambaya yayi da ya zauna kuaa da ita shiru tayi ba amsa hakan tasa ya kai hannu ya rika hannunta ya shiga murza yatsun ta

“Na ɗauka ba a baki tsoro sai cikin dare?”

Dayan hannunta tasa ta share hawayenta

“Ba ita na gani ba, wani mafarki nayi marar kyau kuma da na tashi kai na gani tsaye gefen gado kana min murmushi ina unkurin tashi.sai naga kafafunka ba na mutane ba”

Wani dogon numfashi ya sauke ya busar da iskar bakinsa sannan ya soma magana alhankali kamar mai magana da yarinya,

“Kairat yaushe rabon ki da addu'ah?”

Shiru tayi ba amsa,

“Kin dai na ko?”

Ya bukata, ciki ciki ta amsa masa

“Ina yi”

“No Kairat idan kina addu'ah babu abunda zai same ki, Kairat naga kina da karatun ki Suratul Bakara ɗin nan zaki iya karanta ta kuma duk gidan da aka karanta ta sai sheɗan ya kwana arba'in bai leka gidan ba toh ina ga sauran abubuwa masu cutarwa?.
      Idan ma ba zaki iya ba akwai kula uzai irin kulhuwallahu ahad, kul a'uzu birabbi falaq da birabbin nas, ko wanne uku da safe da maraice ce ga kuma a'uzu bikalimatillahi, Bismillahi lazi ta ma uku da safe uku da yamma ko kuma hasbunallahu ɗari huɗu da hansin safe da yamma kinga hasbunallah ɗin nn ba dai abu mai cutarwa ba sannan zaki rika ganin haske cikin lamarin ki kuma duk abunda ya shige miki duhu sai Allah ya bayyana miki shi in kuma damuwace sai Allah ya yaye miki idan kuma ba zaki iya ba ki rika yin bakwai da safe bakwai da maraice ki rike ayatul kursiyu da Amana rasullu wallahi babu abunda zai same ki matukar kina karanta su daidai sannan ki riki istigifari ta salati suma haske ne so sai”

Kai ta ɗaga masa cike da gamsuwa, ɗayan hannunta ya riko

“Ina fatar ba zaki sake cemin Kinga wani abun tsoron ba?”

Kallonsa tayi ya sakar mata murmushin sa mai kyau da tsada,

“Kuma ina fatar za a rage samin hijab ɗin nan dan Allah cikin gida”

Kallonsa ta sake yi ta ɗauke kai ta tashi ta nufi ɗakinta, shi kuma ya jingina da kujera yana lumshe ido, can ya tashi da sauri kamar wanda ya tuna da wani abu ya nufi ɗakinta.
   Tana kokarin ɗaura tawul ya shigo ɗakin da ala wanka zata shiga, da sauri ta ɓoye bayan labule kasancewar ɗan karamin tawul ne jikita kuma bai ɗauru kirjinta sosai ba,

“Lafiya?”

Ta tambaya still tana ɓoye bayan labulen, shiru yayi kamar ba xai ce komai ba wata zuciyar sai ce masa take yaje ya buɗe labulen wata kuma na hana shi,

“Momy tace ki fara girki yau”

Ya faɗa bayan yayi gyaran murya,

“Toh naji”

Ta faɗa irin ta kosa ɗin nan ya fita.Murmushi kawai yayi ya juya ya fice, sai da taji rufewar kofar palon sannan ya leko ganin da gaske ya fita yasa ta fito ta faɗa toilet ɗin a guje kamar wanda aka ce ma dawowa zaiyi.

                         ***           ***            ***
Kairat na zaune palo taji an danna bell, kofar kawai ta kalla ta ɗauke kai, dan wuyar tashi take ji kuma bata da tabbacin mai danna bell ɗin maybe ma tsoro ne ake son bata, sai da aka danna bell ɗin yafi a kirga aka koma buga kofar sannan ta tashi ta nufi kofar. tana buɗewa ta buga ihu

“Oyoyo Kawalli romon jaɓa”

Ture ta matar tayi tana dariya

“Ni dai karki ji min kina fama da amarci”

Hannunta Kairat ya janyo suka shigo cikin parlour tana faɗin

“Ni dai bana son lalata wane irin amarci kuma?”

“Ga shi nan sai wani haske kike na sani ko har kin samu”

Dariya Kairat tayi sosai

“Oh Maman Namra baki raɓo da abun dariya kin fara halin ki ko?”

“Ba wani hali sai gaskiya wanene zai aje ki a gida har na tsawon wannan lokacin ace ba komai”

“A a ni dai ba komai ni dai ya gida ya yara?”

“Lafiya kalau yara suna ƙkaduna ban zo da ko ɗaya ba”

“Aiko dai baki kyauta ba da kinzo mana ko da Namra”

“Yayan naku ne ya hana kinsan halin shi wai dan kar naje na zauna”

“Oh Yaya manya har yanzu ba a daina halin nan ba”

“Haf za a daina abunda aka saba ne? ai kara miyi lokacin mu karya wuce ku ba gashi kuna naku ba”

Kai Kairat ta girgixa

“Oh Wannan matar ba zaki daina wannan halin ba bari naje n ɗora girki tun da kinzo”

Ta ɗan wara ido

“Ba dai girkin rana ba ko?”

“Shi fa yau ma zan fara”

“Kuma kikayi latti haka? ko maigidan naki ba a gida yake cin abinci ba?”

Dariya kawai tayi ta nufi kicin ɗin.
     Bayan ta kare girkin ta zubo musu taliya suka xauna palo suna ci, sai fira suke firar yaushe gamo!
    Bayan sun gama cin abinci taje ta saka hijab

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login