Showing 87001 words to 90000 words out of 114909 words

Chapter 30 - Babban Goro By Khadeeja Candy

03 Dec 2025

6107

kamar ana zooming ɗinta saboda tsoro. Daker ta iya rufe idonta ta furta



"Innalillahi wa innaa ilaihi raji'un"

Ta daɗe a haka kamin ta buɗe idon ta sake kallon bakin kofar, neman ta tayi ta rasa, tayi ko sama ko kasa, da sauri ta maida kofar ta rufe tana haki

Saman kujera ta dawo ta zauna dafe da zuciya,

Toh ko dai gizo idonta yake mata ne?

Shine abunda ta tambayi kanta tana lumshe, toh idan ba gizo ba kan minene tun dai Minal ba dawowa zatayi ba, wannan tsoro ne da kuma rashin sabo da zama ke kaɗai.
Tana haka taji an sake turo kofar a karo na biyu an shigo parlour, kulle idonta tayi gam, har sai da taji sallamar Saif sannan ta buɗe idon tana amsa masa

"Wa'alaikumussalam"

"Sannu da zuwa"

"Yauwa sannu dai ke kaɗai ce a gidan"

Ya faɗa yayin da yake kokarin karasawa kusa da ita, ita dai har lokacin kanta na kasa tana doubting abunda ta gani,

"Bari naje nayi wanka sai muci abinci ko?"

As usual bai tsaya jiran abunda zata ce masa ba ya nufi ɗakinsa ita ɗin bata ce masa komai ba dan abunda take tunani ya isheta. Har yayi wankan ya fito a gurin da ya bar ta ya tararda ita kuma har lokacin kanta a kasa, tsayawa yayi yana kallonta kamar maj karantar abu a fuskarta,

"Kaiyrat"

Ya furta a hankali, zabura tayi ta tashi tsaye kamar wanda ta razana,

"Na'am"

Sai kuma tayi kasa da kanta,

"Ga abincin ka can ni na ci nawa"

Bata tsaya jiran abunda zaice ba ta nufi ɗakinta. Shi dai da kallo ya bita har ta shige sannan ya ɗaga kafadunsa ya taɓe baki ya nufi gurin dinning ɗin.

Cike da zullumi da fargaba Kairat tayi bachin ta na biyu a gidan, har garin Allah ya waye tunanin yadda taga Minal take har yanzu ta kasa yarda ita ɗince zigo ne idona suke mani shine abunda take ta maimaitawa tana kawar da tsoron dake ranta, bayan tayi Sallah asuba ne bachi mai daɗi ya ɗauke ta bata farka ba sai kusan goma na safe,

"Alhamdulillahil lazi'ahyana ba'adama a matana wa'ilail-nushur A'uxubillahi minasheidanin'rajin"

Bayan tayi addu'a tashi daga bachin ta mike tana mika ta nufi banɗaki, bakinta kawai ta wanke sai fuska ta fito ta ɗauki hijab ɗinta ta saka sannan ta nufo downstairs.
Zaune ta samu Saif a dining room yana cin abinci, karasawa tayi ta risina har kasa ta gaishe shi dan abunda Mummy ta faɗa mata kenan cikin jindaɗi ya amsa yana mata

"An tashi lafiya"

"Lafiya kalau"

"Ga abinci nan ki ci ban tsaya jiran ki dan nasan ba zaki ci dani ba"

Ya faɗa yana kokarin tashi tsaye, tana daga duken tace

"Yaushe zamu kawo Lil Minal?"

Tsayawa yayi yana kallonta,

"Wai da cewa nayi sai nan da sati biyu ko uku kinga kamin lokacin kin ɗan saba abubuwa ba zasu miki yawa ba"

Jin tayi kamar ta zaburo masa tayi cikinsa da masifa, amman Mummy ta hana ta dan ta faɗa mata wannan ba ɗabi a bace ta matar kirki, bata ce masa 'Eh' ko 'A'a' sai kawai ta tashi ta nufi ɗakinta.
Binta yayi da ido har ta shige sannan shima ƴa tsaya yana tunani miye yanke wannan hukuncin bayan saboda Lil Minal ɗin ta aure shi? Dan da kula da ita, amman shi kan gani yake kamar abun zai zame mata wani irin idan aka kawo mata ita yanzu ganin shekaran jiya nan aka kawota a gidan. Amman kuma miye ruwansa tunda ita take son haka ɗin!
Dakinta ya nufa yana shiga ya same ta dukunkune can gafen gado kamar marar lafiya, ganin shigowarta yasa ta tashi zaune tana jiran abunda zai ce mata.

"Kaiyrat"

Ya kira sunanta kamar ba lakka a jikinsa, shi dai baya jindaɗin yadda take kin sake jikin nan dashi ko kuma nace da gidan. Ta ɗan kalleshi kaɗan yayin da take kokarin amsawa

"Na'am"

Karasawa yayi kusa da ita, cikin yanayi mai kamar ya na damuwa

"Yaushe kike son na kawo miki ita?"

Shiru ta ɗanyi kamar mao nazari can kuma ta ɗan kalleshi

"Gobe?"

Ta faɗa kamar mai neman amsa,

"Allah ya kai mu"

Ya juna ya fice. Wunin ranar wuni Kairat tayi shiru shiru gashi yau gidan ba kamar jiya ba ba mutane sosai, ga kuma abunda yayi mata tsaye a rai tunanin yadda zatayi rayuwa a gidan da kuma yadda zaman ta zai kasance da Saif.
Kaɗan kaɗan take ɗan taɓa fira da kawarta, tana cin kankanar dake gabansu.

"Sai ɗa kinyi hakuri Kairat ita rayuwar Aure yar hakuri ce musamman irin wannan auren naki, ki kawar da komai da yake ranki ki fuskanci Ubangijinki kisa ni bauta kike ba wai zakiyi rayuwar jindaɗi bane, yadda kake son rayuwa ba zata kasance maka a haka ba baka taɓa samun komai 100%"

Kai kawai Kairat ke ɗaga mata tana sauraren nasihohin da take mata kasancewarta matar aure.
Ana sallah la'asar tayi ma Kairat sallama, wai mai gida yace kar ta daɗe, Dariya kawai Kairat tayi tana girgiza kai ita kuma ta rika zolayarta tana mata maganganu irin nasu na matan aure. Har gurin Mota Kairat ta raka ta bayan ta fice ta tsaya tana kare ma harabar gidan kallo.

Biyar saura kwata, Saif ya shigo gidan ya daɗe a mota sannan ya shigo cikin parlour,

"Ummu Minal fito ga Lil Minal ɗin ki"

Shine abunda ya faɗa yana kallon kofar ɗakinta yayin da ya kai tsakiyar parlour. Lekowa ta fayi kamar wata karamar yarinya wai ta gani indan da gaske yake, aiko da gudu ta karasa saukowa ganin Baby a hannunsa,
A maimakon ya mika mata baby sai kawai yaja baya da sauri yana mata kallon zolaya

"Wa zaki fara tarba ni ko ita?"

Kallonsa tayi da kyau shi kuma ya sakar mata manyan idon shi, kun kuyar da kai tayi tana murza yatsun hannunta,

"C'mon answer me mana idan kina son na baki ita"

Ya faɗa yana kallon fuskarta. Sake ɗagowa tayi ta kalle shi sai ta sake sanda kai, wani wasan yana yi mata ne dan ta sake jikinta, amman ina bata da niyar hakan. A dole ya mika mata yar dan yadda taga ta dake ɗin nan tsaye guri ɗaya yasan ba cewa zatayi ba

"BISMILAHI RAHAMANIN RAHIM"

Shine abunda ta furta sannan ta karɓi lil Minal ɗin, rumgume ta tayi a kirjinta. Daman can Kairat mace ce mai son ɗiya ballan tana wannan da take da dalilai na sonta.

"Na gode"

Ta faɗa tana kallonsa idonta cike da hawaye, murmushi yayi mata yace

"Dr tace idan zaki bata nono ki bata nonokin na dama kuma ki wanke shi kamin ki bata sannan tace karki bata nono yanzu sai nan da awa bakwai ko kuma ma ki bari har sai gobe tace duk ba matsala bane Momy tace gobe zata zo tare da wanda zata rika lura miki da ita"

Kasa tayi da kanta alamar kunya, taɓe baki ya ɗanyi shi kan bai ga abun kunya a maganarsa ba tun da ba wata ɓaran ɓaramar yayi ba, a nan ya barta ya shige ɗakinsa.
Sallah ce kawai take sa Kairat ta aje Lil Minal amman duk abunda zatayi tana rumgume da ita.
Bayan Sallar i'sha tayi shirin bachinta ta saka hijab kamar yadda ta saba ta hau saman gadon ta kara jan lil Minal kusa da ita tana mai jindaɗi sai kallonta take tana murmushi da alama ma idon ta biyu duk da idon nata a rufe suke amman sai motsi take da baki tana motsa baki.
Kamar wanda aka ce ɗago ki kalli windo, tana kallo ta ga Minal da siffar da ta ganta a farko kuma nan ɗin ma ita take kallo, wata razanannar kara da saki ta sauko saman gadon ba shiri ta fisgi lil Minal ta bar ɗakin tana ihu.

Keep voting dears



50

Da sauri Saif ya ɗago kai daga daga gurin da yake zaune ya kalli upstairs,

“Lafiya.?”

Ya tambaya yana kokarin aje magazin ɗin hannunsa ya tashi ya nufi upstairs ɗin yana cigaba da tambayar ta, bata faɗa masa gaskiya ba sai ta canja maganar,

“Wata na gani gurin windo”

Kunna kai yayi cikin ɗakin yana dube dube. ganin bai fahimci abunda take nufi ba

“Ba fa a ɗakin ba ta waje a windo na ganta”

Windo ya nufa ya shiga dubawa, shikan bai ga komai ba sai kawai yaja windon ya rufe, ya juyo yana faɗin

“Ina jin ita cen dake waje ne kika ango iska ne ke kaɗasu kinga garin akwai hadari, kuma kin bar windin buɗe amman ai kinga babu yadda za'ayi wai ya iya haurowa ta wannan windon tun da ba kasa yake ba”

Ita dai tana tsaye a bakin kofa rumgume da Lil Minal,

“Ba komai kiyi addu'ah ki kwanta”

Kai ta ɗaga masa ba dan ta yarda ba komai ɗin ba, har ya fice a bakin kofar take tsaye sai wani abu take da fuska kamar mai shirin yin kuka, can taji ba zata iya jure wa ba, ta juyo ta sauko downstairs.
   Ba kowa parlour sai tv dake ta aikinsa, haka ta zauna sai kalle kalle take kana ganinta kasan babu natsuwa a tare da ita, sai a jiyar zuciya take saukewa, tana haka Saif ya fito sanye da jallabiya dark blue,

“Gate na dawo mikike so a siyo miki?”

Ya faɗa daidai lokacin da ya karaso kusa da ita

“Bana bukatar komai”

Ta faɗa kamar bata son magana. Sai da ya kai bakin kofa sannan ta ce

“Please karka daɗe”

Juyowa yayi yana murmushi,

“Tunda kina jin tsoro ko.?”

Kasa kasa ta kalleshi ta ɗauke kai. Shi kuma ya fice yana cigaba da murmushin.
     Aiko kamar kar ya fita wani irin tsoro ya kara rufeta, ta rumgume Lil Minal a kirjinta gam ta rumtse ido, jin Lil Minal ɗin na motsi yasa ta buɗe idonta ta ajeye ta saman kujera tasan rumgunar ce wata kila bata so, tashi tayi da nufin kashe tv saboda karar da tayi yawa, sai kawai taga an kashe tv ba tare da ta karasa gurin ba, aiko ba shiri tayi baya baya tana haki.

“Ashe ki baki da amana Kairat? saboda zaki aurar min miji? kin yaudare ni cin cuce ni Kairat kuma ba zan taɓa barinki cikin kwanciyar hankali ba matuƙar kina cikin gidan nan”

A gefenta taji maganar tana juyowa ta ganta cikin bakar siffar da ta saba ganinta, wata mahaukaciyar kara ta saki ta faɗi kasa tana ja da baya sai uhun take ba kakkautawa, aiko sai bin ta take tana son kamota Kairat na ganin ta kusa karasowa kusa da ita ta kara sakin wata irin kara. jin an taɓa ta ta baya yasa ta rika numfashin a jure kamar zai ɗauke

“Nine Kairat ni ne”

Ina! tayi nisa bata jin me yake faɗi sai kaiwai ta cigaba da ihun jikinta na rawa, juyowa yayi ta ganta yasa bakinshi cikin nata ya rike kanta gam, sunyi minti goma a haka sannan hankalinta ya dawo ganin hakan yasa ya sake mata kai ya cire bakinshi daga nata ya rika kafaɗunta yana girgizata,

“Kairat”

Bata iya amsawa saboda numfashinta har yanzu rawa yake,

“Close ur eyes”

Da sauri ta rufe idon kamar mai jiran umarni

“Relax, relax ur body”

Ba musu tayi yadda ya umarce ta

“And stop breathing as long as U can”

Dif numfashin nata ya ɗauke ta daƙiƙin tsayar da shi da tayi

“Now breath”

Ya faɗa yana kallon fuskarta. A hankali ta sauke ajiyar zuciya sannan ta cigaba da numfashinta,

“Open ur eyes”

Tana kallonsa ya ce

“I m here its me okey”

Fashewa tayi da kuka, ya rumgume ta yana mata magana a kunne kamar mai raɗa

“Shiiiiiiii ya isa faɗa min miya faru?”

“Minal na gani Saif”

Bata ɓoye masa ba, ta faɗa masa dan a yadda ra ganta yanzu ya wuce misali gashi har da magana tayi mata. Lil Minal ya nuna

“Wannan ?”

“A'a Minal dai margayiya”

Kai ya girgiza,

“Oh no no no Kairat baki ganta ba tsoro dai kike ji kuma kinsa tunaninta cikin ranki”

Dagowa tayi daga jikinsa daman ba rumgumar take so ba dan kawai tana jin tsoro ne,

“Wallahi na ganta Saif da ido na, ba wai ina tunaninta bane kuma tayi min magana”

“No Kairat kin taɓa ganin wanda ya mutu ya dawo?  babu kuma mai rai baya ganin mamace ba ita bace tsoro ne kawai kike ji”

Shiru tayi tana hawaye, daman tasan ba zai yarda ba babu ma wanda zata faɗa ma ya yarda da ita amman ita tasan abunda take gani.
  Unkurin tashi tayi, daker ta mike tsaye kafafunta basa iya ɗaukarta. A nan shima ya tashi ya lakamo hannunshi ya rika kunkurunta

“Let me help you”

Bata masa musu ba dan tasan ba zata iya kai kanta ɗaki ba, da ɗayan hannunsa ya ɗauki Lil Minal ya nufi upstairs. har cikin ɗakinta ya kaita bayan ya zaunar da ita ya kwantar da Lil Minal, sannan ita ya kwantar da ita ya cire mata hijab ya goge mata fuska.

“Ki daina kuka, kiyi addu'ah”

Blanket ya lulluɓa mata sannan ya kashe wutar ɗakin ya fice. Yana fita, taji ita ba zata iya kwana ɗakin ba duk wani rashin karfi da take ji sai taji ya cire mata, da wani irin kuzari ta walkato saman gadon ta sauko ɗaukar lil Minal ne kawai ya zame mata dole aiko tana ɗaukarta ta fice daga ɗakin a guje. ɗakinsa ta nufa ta daɗe tsaye bakin kofar sai tunane tunane take, kamar ta koma kuma taji ba zata iya ba.Sam ta manta da ba mayafi jikinta haka ta faɗa ɗakin tare da sallama.
  yana zaune saman gado laptop na saman kafafunsa yana dannawa ya ɗago ya kalleta

“Again?”

Kai ta girgiza tana karasa shigowa ɗakin,

“A a nan dai zamu kwana ni tsoro nake ji”

Wara ido yayi ya kalli gadonsa sannan ya kalleta yana ɗaga kafaɗunsa

“Zo ki kwanta”

Gefen gadon ta nufa ta zauna kasa rumgume da lil Minal tana faɗin

“Nan ya isa”

Kitson kanta ya tsaya kallo yana mamakin yadda ta zauna aka tsara mata dashi ta kuma wanda ta tsara mata shi, kanana ne kuma an tsara shi cikin waninsa da sarkaki dan wani kan wani akayi shi gashi kuma ya sauko mata har baya gwanin sha'awa. bai ankaro ba yaga ta sulale kasa kwance, Laptop ɗin ya kashe ya aje saman dorowa ya sauka ya zagaya gefenta ya ɗuka ya ɗauki Lil Minal

“Idan ke zaki iya jurar tsayin wannan gurin ita ba zata iya ba, kuma ki tashi ki hau kan gado ko ki koma ɗakin ki idan baki yarda dani ba miya kawo ki ɗakina”

Tashi tayi zaune ta ɓata fuska kamar ta fasa kuka ta kalli gadon. bayan ya kwantar da Lil Minal ya kalleta

“Rufe ɗaki na zanyi”

Tasan me yake nufi ta fita ta bashi ɗakinsa, ita kan har ga Allah ba zata iya kwana ɗakinta ita kaɗai ba dan jin take kamar kara ganinta zatayi, ganin babu sarki sai Allah yasa dole ta hau saman gadon ta takure kanta can karshen gadon ta kundule cikin nayafin rufa kamar wanda aka cilasta.
   Taɓe baki yayi yaje ya rufe kofarsa ya kashe wutar ɗakin, yazo ya kwanta ya lulluɓe shi da Lil Minal.

    WASHE GARI.....
Bayan yayi sallah asuba ya tashe ta tana faɗin

“Tashi kiyi sallah”

Cikin gigin bachin ta tashi, har zatayi mika sai ta tuna ba ɗakinta take ba da sauri ta murza ido ta ɗauki lil minal ta nufi kofar fita. Shi dai kallonta kawai yake har ta fice.

         Bayan ta kare Sallah, ta sake komawa bachi. bata farka ba sai takwas har da kusan rabin, bathroom ta shiga tayi wanka, bayan ta shirya ta sake komawa banɗakin ta wanke nononta kamar yadda Dr tace bayan ta fito tazo ta ɗauke ta ta ɗaga hijab ɗinta da nufin bata nonon sai kuma ta kasa, ta daɗe a haka sai tunane tunane take, ba karamin jihaɗi tayi ba wajen ɗaurewa ta saka mata nonon a baki, kamar mai nema ta kama da karfi tana sha, runtse ido Kairat ta rikayi kamar mai jin zafi tana dantsar baki tsigar jikinta sai tashi take. Jin motsin shigowar mutum yasa ta buɗe idonta tana ganin Saif tayi saurin sakin hijab ɗin tana faɗin

“Sai ka shigo min ɗaki ba Sallama”

“Eh ya ranki?”

Ya faɗa kamar mai jiranta shi daman tun jiya yaga taken taken ta sam bata yarda dashi gani take kamar wani abu zaiyi nata da ya ɗan motsa sai ta tashi zaune tana kallonsa hakan kuma ba karamin kona masa rai yayi ba. Fitar da ita tayi ta aje saman gadon tana ɓata fuska

“Daukarta ki bata nonon”

Banza tayi masa. ganin yadda ya nufo ta yasa ta ɗauke ta dan bata san nufinsa ba, ta mayar cikin hijab ta cigaba da bata nonon,
  Ta ɗai san ba xai doke ta amman kuma zai iya cewa sai ya ba lil minal ɗin nono da kansa. kwafa yayi ya zauna gefen gadon kusa da ita ya tsare ta. ita kuma ba damar tayi masa magana tasan jiraye yake da ita. Jin Sallamar Mummy yasa shi tashi ya nufi parlour yana amsawa,

“Sannu da zuwa Mummy kece da safen nan haka?”

Ya faɗa fuskarsa shimfiɗe da murmushi yana karasa saukowa downstairs, tana kokarin zaunawa ta ce

“Nice break fast na kawo muku ta kuma mai yima baby wanka ina ya ta”

“Tana ciki”

‘Kairat...’

Ya kwala mata kira, sai gata ta fito ɗauke ta lil Minal ɗin, tana ganin Mummy ta sauko da gudu tana murmushi,

“Yi a hankali mana”

Ya faɗa yana kallon Lil Minal, ita dai bata kula shi kula shi ba har ta karasa gurin mummy ta aje Lil Minal ta rumgume Mummy, sai kuma ta fashe da kuka

“Mummy i miss you”

“I Miss you too daughter ya gidan?”

“Mummy gidan ba daɗi ni ba zan iya zama ba”

Mummy ta rika fuskarta,

“Zaki saba Kairat komai da sannu sannu ake dainawa”

“A a Mummy tsoro ake bani”

“Tsoro..?”

Mummy ta faɗa tana kallon Saif. Murmushi yayi Yace

“Mummy tsoro ne take ji, ta cika tsoro wai Minal take gani ina ganin tasa tunanin ta da yawa ne”

Mummy ta rika hannunta suka zauna fuskarta ɗauke ta damuwa,

“Minal kuma mafarki dai kike yi ko?”

“Mummy ba mafarki bane ganinta nake yi har da magana tayi min jiya”

“What .? no Kairat ya za ayi ki ga wanda ta rasu ba zai yiyu ba”

“Mummy idan ina ɗakina take zuwa”

“Toh da Saif ba ganta ba idonki ne Kairat”

“Mummy ba ido na bane ina ganinta a zahiri ai ba ɗaki ɗaya muke kwana da Saif ba”

“Saboda me?”

Shiru tayi ta ɓata fuska,

“Baki san ba kyau raba gado da miji

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login