Showing 114001 words to 114909 words out of 114909 words
yayi yana satar kallon Momy, Momy kan ɗauke kai tayi ta mai da hankalinta gurin Tv,
"Bah ina Momie Aniq"
"Ke ba Momie ki ce ba"
"A a tunda ta haifi Aniq ni ba Momie na bace"
Momy ta juyo ta kalleta tana dariya
"Ai na manta tace na zama Momy ta wai tunda taga bana da yara, wai Aniq ta bar masa wacan yayi ta kaya"
"Har da Ni kin bar masa?"
Saif ya tambaya, she's nodded her head
"A a wallahi ai kai ba kai ka haife shi ba"
Duk dariya sukayi, banda ita data yatsine fuska
"Ina kika shafo wannan?"
Yana taɓa ink ɗin take Hannunta
"Ɗakin Anty Safiyyah"
"Toh je kice ina gaishe ta"
"Toh"
Da gudu ta sauka ta nufi ɗakin, Momy ta kalleshi
"Amman kan ba zaka faɗa mata tafiya zaka yi ba, dan zatayi kuka kuma kaga ba hutu suka. Samu ba balle kaje da ita"
"Aa ba zata sani ba ma, ai kinga tafi son zama nan"
"Eh tace fa ku ba iyayenta bane"
Dariya yayi yana amsa kiran da aka masa a waya.
**** **** ****
Kamar yadda Daddy yace masa Ranar Saturday ya bar kasar zuwa Paris, duk yadda Kairat taso ya barta bai yarda ba a dole ta hakure suka tafi tare, tafiyarsu da wata daya Mummy ta haifi kyakkyawar yarta, aka rada mata suna AMINA sai dai Meena suka kiranta, babu yadda Kairat bata yi ba dan tazo bikin amman Saif ya tsaya kai da fata yaki yarda wai shi ba zata barshi can shi kaɗai ba, sa'arta ɗaya ya kusa kammala abunda yazo yi, bayan suna da sati biyu suka dawo, a gidan Mummy Kairat ta sauka, ta kama jaririyar ta rungume sai zumudi take kamar zata haɗe ta, kamar su ɗaya da Kairat sai dai fari na Mummy ne, Mummy kunya take ji sosai wai tayi haihuwar tsufa ita tana haihuwa Kairat. Na haihuwa, a boye take bata nono ko kuma ta saka hijab,sai dai a can kasan zuciyarta farinciki fal aciki dan gani take kamar Minal ce ta yi dawo.
BAYAN WADANSU SHEKARU
Tsiren gudu suke, kowa so yake ya wuce ɗan'uwansa, daga karshe dai Aniq yayi nasara, aiko da gudu yayi gurin Safiyyah yana faɗin
"Anty. Ni nayi na ɗaya"
"Sai wa kuma yayi na biyu?"
Safiyyah ta tambaya tana tataba kansa,
"Ni nayi ta biyu"
Lil Minal ta faɗa tana smirking,
Dariya tayi,
"Good ina Amir ta nawa yayi?"
"Amir yayi na karshe"
Sweets ɗin dake hannunta ta ɗauko ta tana mika musu, duk suka rungume ta suna dariya da yi mata godiya, kansu ta rika shafawa tana hawaye.
Kairat dake tsaye a windo tayi murmushi tana rungume hannayenta, bata sarar ba taji an jama kumatu, tana juyowa ya ɗaga mata gira ya kashe mata ido, mur tasha
"Zaka fara ko bafa gida muke ba"
"Gida muke kan Da nan da can ai duk ɗaya ne"
Ya faɗa yana kara motsowa kusa da ita,
"Dan Allah ka daina kar fa Momy ta fito ta gan mu"
"Toh idan ta gani fa Haramun nayi? Bari ma ki gani"
Dukawa yayi ya ɗauke ta Cak, ita kuma ta shiga cuku cukun ganin ta bar jikinsa har suka faɗa saman kujera still bai sake ta ba,
Yana kokarin kai hannu ya cire mata ɗankwali yaji alamar motsin fitowar Momy, ba shiri ya sake ta ta nufi kofar fita da sauri, ita kuma ta tashi zaune tana gyara jikinta da murmushi a fuskarta.
ALHAMDULILLAH!!!
Godiya ta tabbata ga Allah madaukaki sarki mai kowa mai komai, wanda ya bani ikon kammala wannan littafin, oh Allah i hope for your mercy don't leave me for myself correct all my affairs for me,
Komai yayi farko zaiyi karshe, na gode sosai da irin bibiyar da kuke ma wannan littafin, ina son so na tsakani da Allah,
Mom shuraim
Naffsy
Sadiya sale
Yar fulani
Da feenah
Suby jukus
Zainab ta House of novel 2
Da duk yan Khadeeja Candy novels da taskar khadeeja Candy,da duk grp ɗin da nake ciki duka ina godiya,
My wattpad readers
Ina godiya sosai da irin kaunar ku, ba zan iya lissafo sunan ku ba, ina son ku fisabilillahi
Kairat
Gaudiya
Onmyyasmin
Da ghosts readers duka thank you
Facebook readers
Ina godiya sosai da sosai Allah bar zumunci,
My writers
Miemiebee
Phartiemaerk
Safiyyah Mrs j moon
Kamala Minna
Thank you all
Nagarta Writers Association
Nagartacciyar kungiya mai Nagartaccen suna daga Nagartattun shugabanin da Nagartaccen aiki Kungiyata abun alfarina, Allah kara haɗa kan mu Amin
Sadaukarwar taki ce
Anty Maijidda musa maman biyu ina sonki fisabilillah
Tukuici ne
Ga duk wanda ya jure karanta wannan littafin daga farko har karshe i love you
daga karshe ni Khadija Abubakar Alkali nace muku saduwar alheri, ina rokon gafarar duk wanda na taɓa ɓatawa rai cikin kuskure ko ganganci ko rashin sani, ku yafe min nice taku Khadeeja Candy 2 +2
Stay bless all the best one heart one love 😍
Khadijacandy44@gmail.com
In case
********************** ⬇ **************************
********** Ai Hausa Novels ****************
*************************⬆ **********************
DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog.
Visit > https://www.aihausanovels.com.ng
Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post.
Email > aihausabooks@gmail.com
******* FOLLOW US ******
Facebook: Ai Hausa Novels
Twitter: Ai Hausa Novels
Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels
WhatsApp Number: 09017242889
Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu.
********************** ⬇ **************************
*************** Ai Hausa Novels ****************
********************** ⬆ **************************