Showing 105001 words to 108000 words out of 134562 words

Chapter 36 - Rubutaccen Alamari... By Aisha Garkuwa

tace, "bakomai".
hannu shi yasa ya ruk'o nata yana d'an murza yatsunta a hankali yace, "To aimin rakiya mana irinta masoya".
nan da nan ta kwab'e fuska ta tayi rau-rau da ido alamar zatayi mishi kuka,
Ganin haka ya sake daburcewa jiki na tsuma mik'ewa yayi sannan ya sunkuyo dai-dai kunnen ta ya tsurawa k'irjin ta ido murya a cushe yace,
"Kiyi baccin ki mai dad'i tare da mafarki na ina lasar wad'an nan lips en na ki masu taushi Ummu na ina begen randa zaki zamo mallaki na".
Fusge hannun ta tayi ta rufe idonta cikin kinda da mamakin ya Usman d'in,
shiko ko ajikinshi dan daman haka yake baya b'oye abinda yakeji,
juyawa yayi har yaje bakin k'ofa yace,
"please ki ajiye wayarki a kusa".
Sannan yasa yatsunshi biyu a kan lips d'in shi yai kissing d'insu ya hura mata da bakin shi sannan ya fice.

Kai tsaye yawuce FCE(T) inda yake koyar da masu koyan computer duk juma a da asabar.

Office d'in Mallam Bashir Bala abokin aikin shi yashige kai tsaye kasan cewar nan yake zama in yaje saboda yakan jene sabida nemanshi da sukai yarink'a taimakawa,
bayan sun gaisa Malam Bashir yace,
"To bari inje kafin ka huta".
Yana fita shiko ya d'aga kafafuwan shi ya d'ora akan kujerar dake kallon wadda yake zaune ya ciro waya yakira number Ummul ya saka a kunne,
saida ta kusan katsewa sannan ta amsa murya can k'asa tai mashi sallama,
"wa alaikissalam Hubby, ykk".
Jin abin tai wani iri sabida ganinta yanzun nan yafita amma yana tambayar ya take,
shiya dawo da ita daga tunanin da take da cewa,
"Allah yasa ba bacci kika fara na tasheki ba, kiyi hak'uri wallahi soyayyar ki ce take d'ibana nake kasa jurewa shiyasa zakiga ina irin wannan abu buwan".
baki ta tura tare da cewa
"hmmm". Kawai shikuma yaci gaba,
"Gaskiya Baby ki dena min rowar muryarki dan Allah ki karb'eni kiban dama nashigo rayuwarki na cika zuciyar ki da farin ciki pls".
Yasan da wuya tabashi amsa dan haka yaci gaba da cewa,
"Kice wani abu dan Allah, indai kinaso nayi aikin danazo yi".
shiru dayajin ne yasa d'an sauke k'afar shi k'asa yazura takalmin shi ya mik'e yana mak'ale da wayar yafara tafiya yana cewa,
"Ganinan dawowa tunda bazaki min magana ba nima babu abinda zan iya yi gwara indawo inta zamana a gida". Dai-dai nan yabud'e murfi motar shi yashiga ya rufe kofar,
k'arar rufe motar yasa ta tabbatar dagaske zai dawo da sauri cikin sanyin murya tace,
"Ya Usman dan Allah karka dawo". Komawa yayi ya jingina da jikin kujerar motar yayi murmushin jin dad'i yace,
"kin barni na fito bakimin addu'a ba kuma yanzu nakira kink'i kimin magana gashi duk a matsa nake wane irin aiki kikeso nayi a hakan?".
Katseshi tai da,
"Kayi hakuri Allah yabada sa'a ya kiyaye ka".
Wani irin sanyi yaji a zuciyar shi yasa hannu yabud'e motar ya fita ya maida murfin ya rufe sannan yace,
"Amin, to ko kefa, yanzu ne zanyi aiki ki kulamin da kanki saina fito".
"Adawo lfy".
tace sannan ta katse kiran tabi wayar da kallo tana jinjina hali irin na ya Usman shi sam ya fiye zalama daga dukkan alamu shi ba irin Hammanta bane mai hak'uri.


Shak'uwa mai k'arfice take shiga tsakanin Ummul da sabuwar Auntyn ta Aysha Aliyu Garkuwa, wanda sukan yi waya sannan suna dadewa suna chat, hakan na debewa Ummul kewa kuma tasami nutsuwa saboda irin rarrashi da shawarwari datake samu daga gareta saidai kusan koda yaushe dukkansu da kuka hirar tasu take k'arewa musamman idan GARKUWAR tayi mata wata tambaya game da rayuwarta ta baya,
ranar wata asabar Ummul ke fad'awa Auntyn nata zasu tafi Saudi dan gudanar da aikin Hajji ita da Ammi da Ya Sadiq kuma zasu tafine ta international air dan haka Dubai zasu wuce sannan daga can su dawo k'asa mai tsarki. Addu'a tayi mata sannan suka rabu.

Kamar yau aikin hajji ya k'are dan haka suka d'unguma sai Dubai inda zasu kwana kafin da safe suwuto gida Nigeria,
Wannan yaba Ummul damar bud'e data ta tayi sa a Auntyn ta tana online taji dad'in ganin ta saboda hakanan taji tana buk'atar su tattauna akan abunda yake damunta,
sallama ta yimata bayan su gaisa sosai ne Ummul tafara tambaya kamar haka, " Aunty dan Allah dagaske ne yanzu idan nasake aure shikenan na rabu da Hamma Umar na rabu da aurensa na tashi a matsayin matar Hamma Umar?". Tambayar ta bawata tausayi duk da tasaba da shirmen Ummul d'in, cikin sigar lallashi data saba da yimata tace, "Meya kawo wannan tambayar dear?". Shagwab'ewa tayi kamar zatai kuka tace, "Ya Usman ne yadameni kan maganar aure nikuma gaskiya banason kowa kuma banaso inzauna da kowa sai Hammana Aunty Aysha wallahi ina son Hamma na duk duniya yanzu shi nake so".
Ajiyar zuciya tasauke sannan tace,
"Haba Ummuna, tun kafin kiyi tafiyar nan muke magana guda d'aya kuma kinga dukkan mu burin mu mu samar maki da farin ciki wannan shiyasa zakiga kowa nada burin kiyi aure saboda auren shine kad'ai hanyar da zaki sami nutsuwa kuma kisamar wa Hamman ki kwanciyar hankali dan in kinyi aure zaki rege zubarmai da hawaye,
kuma ta hanyar auren Usman ne zaki samu farin ciki mai d'orewa, k'anwata auren Usman shine kwanciyar hankalinki dana iyayenki dakuma na yaronki kai harma dana Hamman ki Allah yamai rahama".
"Amin" ta amsa sannan taci gaba,
"Zai kasance cikin farin ciki kina kulamai da d'anshi da k'anin shi sannan iyayenku su kasance cikin farin ciki kuma su manta da duk abinda ya faru a baya da yafe maki kuskurenki na bijire musu da kikayi a baya".
Sannan taci gaba cewa, "Ki d'aure zuciyar ki nasan dole zakiji babu dad'i kuma dole akwai ciwo a zuciyar ki amma ki daure kiyi hak'uri kinji k'anwata ki yarda da auren Usman".
Hannu tasa tashare k'ollah dake zubowa daga idonta sannan ta fara typing amsa,
"To Aunty Aysha insha Allah zanyi hakan sabida farin cikin Hamma na da iyayena, nagode da kulawarki gareni".
hakanan daga nan kuma hirar takoma rarrashi saboda kukan da dukkansu sukeyi.


K'arfe 12 na dare jigin su yasauka a filin sauka da tashin jirage na Aminu kano a cikin birnin kano,
a Tahir guest palace suka kwana sannan da safe suka d'auko hanyar Potiskum, ya Usman da ya Adam ne sukaje d'aukosu haka suka dungumo misalin k'arfe 10:08 suka iso gida,
Sunsami kowa cikin k'oshin lafiya Umar Farouq tunda suka iso ya haye jikin mahaifiyarshi yanata bata labari na abubuwan da suka faru bata nan haka suka wuni cikin nishad'i sai bayan sallah isha'i ya Usman yamaida Halima da yaranta gida shima Adam yamaida Aunty Shuwa da Inna tunda unguwarsu d'aya,
Adam na dawowa yawuce b'angarensu dan yana buk'atar hutu, shiko gogan Ummul daman Allah-Allah yake bak'in su tafi ya gana da masoyiyar shi tun yana mota yakira wayarta tana d'auka yace,
"Ki jirani a palour Nanne baijira amsartaba ya katse kiran.


A parlour ya sameta tana kwance akan kujera yana shiga da sallama tamik'e zaune ta amsamai kusa da ita yaje yazauna yasauke ajiyar zuciya sannan ya kure ta da ido cikin tsananin so yace,
"gaskiya kin rame baby, dama nayita tunanin hakan".
d'an murmushi tayi sannan ta sunkuyar dakai k'asa tace,
"ya Usman tunda naje a wuraren Ibadan nake tarewa ina yiwa Hamma na addu'a da nema mishi rahamar Allah ko cin abinci bana son fita,
ranar na d'an fara gyagyad'i sai nayi mafarkin Hamma na yana nuna min kai yana cemin inje gareka kar in bari ka zubda hawaye".
sai kuma tayi shiru tana zubda k'ollah,
sai kuma tace,
"ya Usman ka gafar ceni".
A hankali ya sake matsota yakamo hannayen ta duka biyu ya rik'e da kasalalliyar murya shi yace, "bantab'a jin b'acin rai akan duk abinda kike fad'a kinyi ba,
nasha fad'a miki komai kikayi birgeni yake kuma komai kyau yake miki nagode da kulawarki ga d'an uwana".

Shiru sukayi dukkansu yanata matsa hannunta dake rik'e a hannun shi ya katse shirun da cewa,
"Fatana ki yarda da aurena".
sai kumu yasa hannu ya d'ago fuskarta tare da cewa,
"Kamar kinada magana ko?".
K'asa tayi dakai murya na rawa a hankali tace,
"inaso ".
da sauri yace,
"kina son me"?.
ido ta lumshe cikin zubda k'ollah tace,
"Ince son ince maka na amince da maganar auren".
Kasa k'arasawa tayi tafashe da kuka,
jiki na rawa ya janyota jikinshi ya had'ata da kirjin ya ruggume ta da k'arfinshi ta yanda har tana jiyo bugawar da zuciyar shi takeyi ido ya lumshe yanajin wani irin yanayi da bai tab'a jiba hakan yasa yakasa daurewa shima yafara k'ollah,
kamar ya tuna wani abu yasa tafin hannu shi ya goge k'ollar idon shi yasake matso ta yace,
"Yi hakuri kinji, kinga narasa mezance maki dan murna amma dai nasan yau matsalata ta k'are".
Sakinta yayi ya sauka daga kujerar ya durkusa yayi sujjada yayiwa Allah godiya sannan ya juyo yazauna gabanta ya d'ora kanshi akan cinyarta kamar k'aramin yaro yasauke nannauyar ajiyar zuciya yace, " inasonki ina k'aunarki". A hankali takai hannun ta d'aya kan gashin kanshi ta tusa yatsun ta ciki tana d'an tureshi, runtse ido yayi da k'arfi yanajin wani irin abu da baitab'a jiba kuma bazai iya kwatan tawaba,
itace ta dawo dashi daga halin dayake ciki dacewa,
"Naji dad'in samun Aunty Aysha Garkuwa domin ko yaushe shawararta irin ta Ammi da Nenne ce kuma in nabi ina jin dad'i".
d'ago kanshi yayi ya kureta da ido hakan yasa tai shiru cikin kunya tafara wasa da yatsunta,
shi kuwa sake tashi yayi ya zauna gefen ta sannan ya ruk'o hanna yenta murya a raunane yace,
"Nasani my life nasan wannan yafaru da ikon Allah da taimakon ta hak'ik'a ni dai GARKUWA tayi min rana".
sai kuma ya d'an fizgota cikin tsananin shauk'i yace,
"inna fad'a miki toh ki rik'e mini duk tsanani da wuya zana sakar miki sona kiyi rik'ona don Allah kar naga kin gajiya,
in dai kikayi haka so zai habaka zamuga kyen tafiyar,
da shak'uwa aka samu yarda har so yassanya muna kama da juna".
shiru tayi tana jin salon son ya Usman d'in ta mai cike da kalamai masu sanyi gaba d'aya ya kashe mata jiki sai k'ara narke mishi takeyi cikin Shauk'i ya tallabo fuskarta ido ya kashe mata tare da kashe murya cikin rad'a yace,
"Bisa dukkan alama an yabamini Kumar nasan zanga kyen yanayi domin kinmin halin mutuntawa duk kin gwada mini su tunda kin amince na zama mijin ki ni kuwa dole na k'arfafa so da k'auna nayi miki rik'on da ba shayi,
gurin zaman auren mu in kyautata miki domin muyi zama na faran tawa juna rai".
cikin jin kunya murya can k'asa tace,
"Ni nace maka kwarai ina so dan haka karka fidda rebo,
me kake so ya zama alamar sona a gareka don akwai sabo a tsaka ninmu inko yarda ta kake buk'ata to ka sanya a ranka ka samu,
dan kai gudane da bani da kamar ka nida Hamma na da Farouq a zuk'atan mu".
Murmushi yayi cikin jin dad'i yace,
"Ummu na ina da matsala fa ban sani ba ko zaki iya d'aukar nauyin yawan buk'atata gaskiya gwara na shaida miki tun yanzu kar sai munyi aure kice na matsa miki ko na fiye

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login