Showing 9001 words to 12000 words out of 249044 words

Chapter 4 - Abokin Rayuwa By Khadeeja Candy

03 Dec 2025

14925

Khadeeja Candy dai taku ta makaranta, da fatan za ku yi patronizing ɗina.

Za ku iya join group dina domin bawa idanuwanku abinci https://chat.whatsapp.com/HGRV2NYIoaCF7SIvPOIv08

Kuma zaku iya saka order ta wannan number 08036126660 WhatsApp.

KHADEEJA CANDY STORE expect more, and pay less...😊



Page 4️⃣


Ragowar cake din dake fridge ta dumama musu, ta dumama madara a microwave sannan ta zuba a plate biyu kowa da cups dinsa sannan ta fito kai tsaye ta nufi dakin London ta shiga da murmushinta sai ta same shi zaune Nannynsa na karanta masa story book. Gefen gadon ta aje masa cup din da cake sannan ta shafa kansa ta sumbance shi.

“How are you My love”

Murmushi kawai yayi mata daman be cika magana ba, sai idan ta dauro. Emily ta kalli Nannynsa Chidimma.

“Ina fatima?”

“Ta shigo amman ganina a dakin ya saka ta fita ina tunanin tana dakinta”

“Okay”

Ficewa ta yi daga dakin ta tura kofar dakin Fadima sai ta ji ta a rufe, cup din da plate din cake ta hade guri daya ta yi knocking da dayan hannunta.

“Baby, bude kofar mana”

“I won't”

“Na kawo miki cake da madara”

“Bana so”

“Na fada miki babu kyau bachi da fushi, me yasa kike da kafiya ne?”

“Ki fadawa Vito ya daina zuwa nan i hate him”

Emily ta daki kofar dakin da karfi.

“Ki bude kofar nan Fatima and kar na sake jin kin fadi wata kalma marar dadi akan V idan ba haka ba zan bata miki rai”

“Ba zan bude ba!!”

Fatima ta amsa mata a tsawace kai kace Fatimar ce uwa Emily ƴa, runtse ido ta yi tana maida numfashi a hankali, sanin halin yarta da kafiya da rashin kunya ya saka bata sake bata second a gurin ba ta juya ta sauka kasa, tana saukowa kwakwalwarta na tuna mata da wasu kalamai na bakin littafin da zuciyarta ta aje.

_Ka yi hakuri karka rabu da ni, ban san kowa anan ba, ba ni da kowa a nan_

Ina rike da kafarsa nake fadin haka sai ya fisge kafarsa ya matsa baya.

_Ina da kafiya akan abun da nake so, da kuma wanda bana so, karki sake nuna kin san ni_

Ina da akan center table ta aje cake da milk din cikin bacin rai, ta zauna a kujera zuciyarta na yi mata babu dadi.

_Ina da mata ina da iyali, kin zo ne kawai ki ruguza rayuwata Aisha_

Jefe jefa kanana da manyan abubuwan da suke faru a rayuwarta ta baya suke dawo mata a duk lokacin da take zaune ita kadai ko kuma rai ya bace. A fusace ta mike tsayeta ture madarar da cake din har sai da suka zube kasa.

“Daman idan baki yi kafiya ba ai ke ba yarsa bace...!!”

Ta karasa da kara sosai kamar mai shirin yin duka sai haki take, windows falon ta nufa da curtain dinsa suke a bude ta tsaya sai ta hango Sarkin nata zauna kishingiden a cikin motarsa gilashin motar yana kasa gaba daya, yana kallon windows din da take tsaye, rufe curtain din ta yi ta nufi kofar falon ta bude ta fita. Hango fitowarta ya saka shi fitowa daga cikin motarsa yana jiran tsorowarta. Tsayawa ta yi a gabansa hasken kwayayen dake cike a gidan suna haska fatarta mai tsananin fari.

“Akwai abun da kake bukata ne?”

Ta ido yana amsa tambayarta, a sa'ilin da bakinsa yayi nauyi furta mata kalamansa.

“You...”

Ya furta bayan ya kwaci kansa.

Babu bata lokaci ta rumgume shi, ta lumshe idonta dake kwance da ruwan hawaye. Da ace tana da wani abun da zata aikata ta biya V da tuni ta aikata, domin shi ne mutumen da ya mayar da ita yadda take a yanzu, shi ne mutumen da be nuna mata kyama ba, ko da yake shi din kistane dan'uwanta da musulmi ne babu tantama da yanzu ya rabu da ita ko ya ci amanarta, amman shi yana nan tare da ita duk kuwa da irin kyamar da yarta take nuna masa.

Slowly ya zagaye bayanta da hannayensa ya rumgume ta comfortably, idonsa a sama yana kallon window Fatima dake rufe cike da bacin rai, domin ya tsani duk wani abu da zai batawa Emily rai idan aka cire shi kansa, a iyakar gidan yasan babu mai yi mata rashin kunya da rashin magana da kokarin bata mata rai ko tuna mata da rayuwar da ta jefar sai Fatima, domin London ba shi da lafiyar damuwa rayuwar kowa sai idan ciwonsa ya tashi.
Ta dago daga cikinsa a hankali ba tare da ta kalleshi ba, sai ya kai hannunsa ya rika pink lips dinta ya dan dagota kadan.

“Karfe nawa zaki tafi aiki gobe?”

“6:30am”

Ya sake kallonta da kyau yana matsawa kusa da ita.

“Wane irin aiki ne ake tafiya karfe 6:30am na safe?”

“Haka matar ta fada min karfe 7 ta yi min a can”

Ta amsa har lokacin bata kalleshi ba. Ya kankance ido kamar zai yi magana sai kuma ya fasa, ya kai hannunsa yana shafa gefen fuskarta.

“Shiga ki kwanta, ki samu bachi da wuri”

Ta kalleshi kadan.

“Good night”

“I love you”

Ya furta ba tare da jiran ta mayar masa ba, domin be taba furta yana kaunarta ta amsa masa ba, tun farkon haduwarsu har zuwa yanzu da take kokarin samun kanta, ya mata uzuri domin ya nutsa a labarinta, yayi rayuwa da ita ya san zahiri da badininta, yana iya jin yadda abun ke tsikarta duk kuwa da kasancewar be wanzu cikin wancan rayuwarta ta ba, sai dai a yanzu ya jiku da kaunarta sonta na hana shi ganin abubuwa da yawa a na laifi akanta.

Tana tafiya rumgume da hannayenta har ta shiga falon ta rufe sannan ta shiga wani bangare na falon ta dauko mopper ta gyara gurin, a falon ta zauna na tsawon lokaci, ba kallo take ba, ba tunani take ba, ba bachi taka ba, wani yanayi take ji wanda rabinsa babu bakinciki, kuma babu kishiyarsa, wani yanayi taka ji na dabam. Motsin saukowar Chidimma ya saka ta juyo tana kallon stairs din har Nannyn ta sauko.

“London yayi bachi, Fatima kuma dakinta a rufe yake, na murda bata bude ba, wata kila ita ma ta yi bachin ne”

Nannyn ta fada cike da ladabi, Emily ta dago daga kishingiden da take a jikin kujerar tana cigaba da kallon Chidimma.

“Kina kokarin da yarana, musamman Fatima, halayenta ba masu kyau ba ne na sani, amman ina fatan zata sauya nan gaba”

Chidimma ta yi murmushi tana jindadin yadda Emily ke karfafa nata guiwa tana appreciating duk wani abu da take yi ma yaranta.

“Zata canja ranki ya dade, a yanzu tana da kurciya ne, she's just 6”

Emily ta daga gira.

“I hope so, Good night Chidimma”

“Good Night Ma'am”

Ta amsa mata da kai sannan ta fice daga katon falon, Emily ta mike tsaye ta rufe kofar falon sannan ta kashe komai na kallo da kuma na'urar sanyaya falo ta haura sama, dakinta ta shiga ta dauke wani makullin ta nufi dakin Fatima ta saka key din ta bude dakin. Turawa ta yi ta shiga sai ta same ta kwance a kasa rumgume da teddy dinta, sanin yarta sikila ce ya saka ta fara kashe ac dakin dake kunne domin akwai sanyi a garin, karamin abu ne ta tashi da ciwo washe gari.
Gefen gadon ta zauna tana kallon Fatima da kamanin mahaifinta suke zube a fuskarta kamar an tsaga kara, ta kai hannunta ta shafa fuskar yarta.

“Ina da tsada a gareki Fatima, amman baki sani ba, saboda kina karama, kina fada min magana son ranki, kina wasu halaye da bana so, ina jin cewar kamar ke ma kin tsane ne kamar mahaifinki”

Ta share hawayen da suka zubo mata.

“Kin yi sa'a kina da ni a raye, a lokacin da nake sa'arki, ina a wani gidan marayu tare da yaran da suka rasa iyaye ko aka tsinta, macen dake kula da ni ta fada min ina jaririya ba a yanke min cibiya ba aka aje ni a gidan, har yau ban san dalilin da zai saka uwa ta aikatawa yarta haka ba”

Ta shafa fuskar Fatima a karo na biyu, sai kuma ta yi murmushi.

“Na san zafin rashi, na san zafin yaudara, na san zafin kiyayya, ba zan yarda ku fuskanci ko daya ba, zan jure zan mutu saboda ku yara, ku ne kawai iyalina”

Ta sumbanci kumatun Fatima ta ďaga daga kan gadon ta gyara mata lullubinta sannan ta fice daga dakin, ta nufi dakin ďanta na fari. Tana kallon fuskarta sai ta yi murmushi ta gyara masa kwancinsa tana zancen zuci.

‘Wata kila ni tawa uwar ta mutu, shiyasa aka kawo ni a nan, amman me yasa yan'uwanta ko yan'uwan mahaifina ba su iya rike ni ba? Haihu ba tare da aure ba a addinin kirista ba abu ne na kunya ba, kamar wasu addinan ba, balle nace ko tana kunyar haihuwata ne’

Ta sauke ajiyar zuciya a hankali, sannan ta fito daga dakin ta koma dakinta, gaban madubi ta zauna tana kallon kanta, sam ba zaka santa a da ka ganta a yanzu kace ita ce ba, sai idan ka yi mata farin sani, domin jikin da take da shi a can da, yanzu babu, ta zama fit da ita like a model, farin fatarta a yanzu ya sauya ya ninku da kaso mafi daraja domin a yanzu ta samu kwanciyar hankali da abinci mai kyau da lafiyayyen gurin bachi, da kwanciyar hankali, abubuwan da ta rasa a baya.
Ta fara tsege kanta tana tuna wani lokaci da Khalifa yake yanke mata gashin kai saboda kawai wulakanci da tozarci, har ta gama tsife kan ta cire gashin dokin dake tsarkafe cikin nata red hair din bata daina hawaye ba.

Kwashe gashin dokin ta yi ta zuba a dusbin sannan ta gyara kanta, idan ba ka taba ba, ko kuma an fada maka ko ka sani babu wanda zai yarda gashinta ne domin jan gashi take dashi ba kamar sauran mata da suke da jan gashi ba, ko da yake blue eyes dinta da farin fatarta ya isa ya fahimtar da duk wani mai kallonta cewar ita ruwa biyu ce ba tare da tantama ba.
Ta canja tufafin jikinta zuwa na bachi, ta gadonta ta jingina, ta dade a haka sannan ta mika hannu ta dauko file din da Amal ta bata a gurin aiki ta bude tana duba dokoki da ka'idodin kamfanin, bayan ta gama ta saka hannu a duk gurin da aka bukata, sannan ta aje ta kwanta ba tare da ta kashe wutar dakin ba, domin bata bachi da wuta a kashe.
Kasancewar a cikin duhu yana firgita kwakwalwarta, ta kan kasa sakewa da rasa natsuwa sa sukuni, sanin hakan da Vito yayi ya saka shi tanadar mata duk wani abu da zai bata haske idan babu wutar nepa.

Bata kwanta da wuri ba, hakan ya saka bachin yayi mata nauyi bata tashi a lokacin da ta so tashi ba wato 4am. Karfe biyar da yan mintuna ta farka tana murza ido, alarm din dake gefen gadon mai hade da agogo ta dauka ta duba. 5:14am ya saka ta zabura da kuzari ta sauka saman gadon ta saka bedroom slipper ta fice da sauri. Tun kamin ta sauko kasa ta soma jin kamshin yana dukan hancinta, tsayawa ta yi ba tare da ta karasa saukowa daga kam stairs din ba tana kallon hanyar Kitchen din da dan tsoro, a iyakar saninta Chidimma ba ko da yaushe take shiryawa yaranta abun karyawa ba, sai idan bata gidan ko kuma ta bukaci ta shirya musu din, and babu wanda ya san kudurinta na son shirya abun karyawa da wuri saboda fita aiki, ita kanta bata shirya musu abun karyawa sai 6am. To waye a kitchen din.

Ta fara bin falon da kallo, har idonta ya sauka akan rigar Vito dake aje a kan kujera, siririyar ajiyar zuciya ta sauke a hankali tana jin kamar hankalinta ya kwanta, daman idan wani abun cutarwa ne ai zata ji hayani ko a tashe ta, tun da akwai mai gadi a gidan. Saukowa ta yi a hankali kamin ta karasa Kitchen sai gashi ya fito rike da plate, dinning ya nufa ya aje plate din sannan ya nufo gurin da rigarsa take ya dauka ta nufota ta rufe mata jiki da rigar ya kai bakinsa saitin bakinsa zai sumbance ta.

“You already know how much i hate physical touch, i hate anything related to love”

Ta fada bayan ta kawar da kanta, sai ya juyo da fuskarta yana kallon cikin idonta zuwa gashin kanta dake red, irin na jajayen turawan nan da ake haihuwa da jan gashi.

“Good Morning”

Ya fada ba tare da murmushi ko sakin fuska ba, daman murmushi da far'a abu ne da suka yi ma fuskarsa tazara, abu ne mai wahala yayi murmushi idan ma yayi kadan ne ko na gefen fuska balle kuma dariya da yake jin bata zame masa dole ba.
Hannayenta ta saka ta sauke nasa hannayen dake rike da fuskarta, ta nufi kitchen tana fadin.

“Me kake dafawa? Me yasa ka zo nan da wuri haka?”

Juyawa yayi yana kallonta madadin ya amsa mata sai ya jefo mata wata maganar da ya saba fada mata a duk lokacin da take kokarin kaucewa kaunarsa.

“Da ace zan yi arba da mutanen biyu da suka saka kika tsani soyayya, suka rikita miki lissafi, da na saka sun tsani kansu, da na rikita kwakwalwarsu”

“Sun dade da mutuwa a gurina, rayuwa ta baya ma na jafar da ita, Emily din da ba ita ce yanzu ba, wacan ta mutu wannan kuma yanzu take rayuwa”

Ya taka ta bi bayanta har cikin kitchen din ya tsaya daga gafe yana kallonta, ita kuma sai duba abincin take, farfesun naman kaza, sai dankali da plantain, dayan cooler kuma samosa ne da zafinsa. Ta daga ta kalleshi da blue eyes dinta masu matukar daukar hankali.

“Meyasa ka shirya duk wannan”

Ya matsa kusa da ita sosai.

“Kin fada min 6:30am zaki tafi aiki, bana son ki tafi da yunwa, kuma na san idan kin farka zaki iya cewa sai kin shiryawa Fadima da Londom abinci zaki tafi, shiyasa na zo tun 4am, na shigo kina bachi”

Kallonsa take cike da tausayawa domin hidimar da yake ta yi da ita, bata san wata hanya da zata saka masa ba.

“Me yasa kake takurawa kanka da yawa saboda ni? A irin wannan lokacin kamata yayi ace kana kwance kana bachi ne, V baka bukatar hidima irin wannan saboda ni”

Hannunsa daya ya kai ya rika fuskarta, kaunarta yake karanta a fuskarta da idonta, da ta san yadda yake jinta a ruhinsa wata kila da bata fada masa magana makamanciyar wannan ba. Be ce da ita komai ba ya saki fuskarta ya gyara mata jacket dinsa dake jikinta ya rumgume ta, ya lumshe ido. Ta jure iya juriyar da zata iya na bashi damar rabar jikinta na second goma ne kawai bayan wannan sai ta fara kokari raba jikinta da nashi.

A tare suka karasa dan abun da ba za a rasa ba, sannan ta shiga ciki ta wanke bakinta ta fito ta yi breakfast din yana zaune yana kallon yadda take jindadin abinci, ba lokacin cin abincinsa ba ne, baya karyawa dai 10am, a yau kuma kallonta kadai da jindadin yadda take cin abincinsa ya wadatar da shi, farincikin fada masa abincinsa yayi dadi da ta yi ya kosar da duk wata yunwa da zai ji a wunin ranar.

Ya daga mata kai yana murmushi kadan, yana jin kamar ace su daure a haka, su yi zama irin na masoya ko ma'aurata, sai dai ya san samun haka a gurin Emily a yanzu ba abu ne mai sauki ba. Kallon agogon falon da ta yi ya saka ta yi hanzarin karasa cin abincin ta mike tsaye.

“Bana son na yi latti, karfe 6:30am zan tafi aiki”

“Wane irin aiki ne za'a tafi karfe 6am? Me yasa kike son takurawa kanki a yanzu Emily kina da komai a nan”

Bata ce masa komai ba, ta cire jacket dinsa ta aje a jikin dayar kujerar, ta kwashe kayan da ta bata ta kai kitchen sannan ta wuce ta haura sama. Mikewa yayi tsaye ya nufi jacket din ya dauka yana kallon stairs din kamar mai jiran fitowarta.







TURHAN POV.

“Baka amsa ni ba”

Ta maimaita da yaren da ita da shi suka fi fahimta, wato Larabci. Lemun dake gefen Laptop din ya dauka ya sha ya aje sannan ya kalleta ta cikin Systems din dake gabansa.

“Ba yanzu ba, akwai wani aiki da ya taso min, ina son sai na karasa shi tukuna?”

“ما طبيعة عملك يا حياتي؟”
“Wane irin aiki ne Hayatie?”

Ya kawar da fuska kaminnya juyo ya kalleta yana shafa kansa, bata jira amsarsa ba ta sake aika masa da wani zancen.

“لا أستطيع تحمل غيابك عني.”

“Ba zan iya jure rashinka a kusa da ni ba”

“Abu mai muhimmanci baki bukatar sani, idan na kammala zan dawo”

“Ka canja min a yanzu”

Ya shafa kansa yana jin wani sabon fushi na kokarin rufe shi.

“Saboda bana haihuwa ne, ko kuma dai ka gaji da zama da ni ne?”

“Zaki iya ba ni ďa? Zaki iya haifa min jinina Jalila?”

Ta yi shiru tana kallonsa kamar yadda shi ma yake kallonta, kamin ya kai hannu ya rufe Laptop din ya kwanta jikin kujerar yana maida numfashi, me yasa ya fada mata haka? Al'adunsu da dokokin sa ake cilasta masa bi ba daga ita ba ne daga masarautarsu ne da kuma mahaifinsa.
Ya tashi zaune yana jin fushinsa yana karuwa tunawa da yayi da yadda Ammy ta yi fushi da shi, saboda yarinyar da bata da ala komai da ita.
Gaba daya an hada masa zafi ta ko'ina, babu wani daki daya da zai laba yaji sanyi. Wayarsa ya dauka ya kira abokinsa har lokacin be sauka daga fushi da bacin rai da yake ji ba.




ALIYU POV.

Yana zaune a kan gado, matarsa na kwance kanta na cinyarsa, ita da shi sun sakarwa plasma dake dakin idonsu, gadon da suke kai kuma ya karbi amanarsu, domin kana kallonsu zaka san hankalinsu a kwance yake basu da wata damuwa ko kadan.
Wayarsa dake can kan karamin tebur ajeye ce ta yi ringing, a take ya ja tsaki domin ya ji

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login