Showing 132001 words to 135000 words out of 178785 words

Chapter 45 - Babu So Complete Hausa Novel

05 Feb 2025

32863

ɓata fuska shima. Sai ta saki dariya da masa gwalo.........✍


*😝😜Za'a koma filin wasa🚴🏼*
        




_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*


YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902

IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇
09134848107


*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
[11/14, 9:00 PM] My Zafafa: *_Typing📲_*




*_❤‍🔥BABU SO....!!❤‍🔥_*
_(Miya kawo kishi?)_



*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

*_BABU SO👉🏻AREWABOOKS_*

https://arewabooks.com/book?id=63447a616580db4ec203d718


*_62_*


.........A waje suka sami aunty Mimi tare da Dr Bilkisu. Khaleel ne yazo ɗaukarta ita gida zata wuce. Anaam ta shiga zazzame jikinta a nasa amma yaƙi sakinta har sai da ya sakata a mota. Ya ranƙwafo zai sumbaceta ta kauce tana faɗin “Kai yaya wai bakajin kunyar aunty mimi”.
Kai ya kaɗa mata da lumshe idanunsa “Ƴar kaɗan”.
“Kake jin kunyar tata?”. Ta tambaya cikin sigar waro masa idanu.
“Eh mana ba mamata bace. Ba buƙartar na ɓoye mata muhimmancin autar mata ai”.
Rufe fuskarta tai da tafukan hannayenta tana murmushi. “Ni dai babu ruwana”
Murmushi yay da sumbatar kunenta. Ƙarasowar Aunty Mimi wajen ya sakashi ɗagowa. Sai lokacin takejin batare da Aunty mimi zasu tafi ba. Fuska ta kwabe da rokonsa zatabi aunty mimi ama yaki. Sai kawai ta kama hawaye.

★Shiru babu mai magana a motar har suka iso gida. Har mai rake ta gani tana so amma ta gwammace tai haƙuri da tace ya tsaya ya siya mata. Itace ta fara fita a motar tun kafinma ya kashe, daga shi har Aysha suka bita da kallo. A ransa ya ayyana (Ni nasan maganinki yarinya).
    Aysha ce ta kwashi kayansu, a dai-dai lokacin Fadwa ta fito daga sashenta dama tana laɓe duk tana kallonsu tun shigowar motar gidan. Tayi ƙyau cikin kwalliya sai baza ƙamshi ake. Tai masa sannu da zuwa Aysha ta gaisheta. Itace ta taya Ayshan kwashe kayan zuwa sashen Anaam ɗin. Sun sameta kwance cikin kujera ido a rufe kamar mai barci, kuka take son tayi akan hanata bin aunty mimi amma yaƙi ya fito, shine tai luff a wajen zuciyarta na suya. Sallamarsu baisa ta buɗe idanun nata ba, har sai da Fadwa tace mata ya jiki. Ciki-ciki ta amsa mata, Fadwan ta nuna kamar bata damuba ta sake mata addu'a sannan ta fice.
     Aysha datai tagumi ta girgiza kai kawai. Tashi tai ta fara gyaran sashen duk da bawani datti bane ba. Harta kammala da falo ta koma bedrooms Anaam na'a wajen kwance, Shareff kuma bai shigo ba. Ayshar ce bayan kammala aikin nata ta fito tace mata ta tashi taje tai wanka ga ruwa can ta haɗa mata. Batare data tanka mata ba ta miƙe. “Ki fara shiga ruwan zafin kamar yanda doctor tace.”
    Kanta kawai ta jinjina mata tai shigewarta. Aysha ta bita da kallo cikin tausayi, dan ita tausayi take bata, saboda ta fahimci abinda Anaam ɗin ke gudu danta jigata a matuƙa a hanun Yaya Shareff ɗin.
Shigowarsa ce ta katse mata tunani, yabi falon da take bazama turare da kallo, sai dai baice komai ba yakai zaune.
     Burner ɗin Aysha ta ajiye da nufar kitchen, babu jimawa ta dawo ɗauke da ruwan. Zata zuba a kofi ya karɓa goran ruwan, murfin kawai ya buɗe ya kafa kai. Bai ajiye ba sai da ya shanyesa tas, da alama ƙishin yakeji dama. Sai lokacin yace, “Tana ina?”.
   “Tana ciki yin wanka”.
Ƙofar ya kalla na wasu ƴan sakanni, sai kuma ya miƙe. “Ki shirya zuwa anjima saina maidaki gida”.
   Da to ta amsa masa. Shi kuma ya shige corridor ɗin bedrooms ɗin Anaam. Tana faman ƙunƙunin ruwan da Aysha ta zuba mata na sit bath yayi zafi da yawa ya shigo, cikin sauri ta juyo kuma a rikice dan babu komai a jikinta. Daburcewa tai gaba ɗaya tama rasa ina zata saka hannu ta rufe, yi yay tamkar bai ganta ba, ya ƙaraso cikin toilet ɗin. Ruwan da take sirkawa ya sakama hannu, ya ɗago yana kallonta. Juyar da kanta tai gefe da ƙara tsuke fuska.
     “Humm”
Kawai yace ya fara ƙara ruwan zafin.
  “Yayi zafi fa da yawa”.
Ta faɗa da sauri kamar zatai kuka. Dai-dai nan ya ɗago dan ya masa yanda yake buƙata, da sauri ta yunƙura zata fice ya damƙota, ƙoƙarin ture hanunsa ta shigayi tana wani ciccijewa ita a dole bata wasa bace. A karon farko ya saki murmushi, hannun nata ya saki ya damƙe towel ɗin, ta ɗago a matuƙar firgice tana kallonsa. Ido ɗaya ya kashe mata da cije gefen lips ɗinsa shima, dole ta kauda kanta dan salon nasa saida tsigar jikinsa ta tashi. Matsota yay tare da ranƙwafowa bakinsa saitin kunnenta.
      “Bakin ya mutu ne ƴammata?”.
Fuskarta ta sake kaudawa gefe da son ƙwace hanunta. Sai kawai jitai ya since towel ɗin nata. Ruɗewa tai, tai ƙasa zata duƙe ya ɗagata cak ya dire a ruwan zafin. Azabar data ratsata ta zafin ruwan ta sakata sakin ƙaramar ƙara mai kama da kukan shagwaɓa. Matso da fuskarsa yay gab da tata, saukar numfashinsa akan tata fuskar ya sata ɗan buɗe idanunta dake rufe, dai-dai lips ɗinsa na sauka kan nata, sai kawai jikinta ya hau rawa. Ya cigaba da binta a wani salo daya saka jikinta saki lokaci guda, sai dai bai samu haɗin kanta ba kamar yanda yake buƙata. Bai damu ba ya cigaba da sarrafata a hakan tunda dai saƙonsa na isa kamar yanda yake buƙata. Nisan tafiyar ya sakata tuna azabar da tasha a daren shekaranjiya, ga gargaɗin doctor na ta kiyaye har sai ciwonta ya warke. Kota warke ɗin ba buƙata take ba balle yanzun. Laushin da gaɓɓansa sukai ne ya bata damar janye jikinta, ta miƙe zumbur jikinta na ɓari. Bashi da zaɓin daya wuce shima miƙewar, ta nane da bango tana girgiza masa kai ganin ya ɗago idanunsa da sukai matuƙar canja launi yana zuba mata.
     Hannayensa duk biyu ya dafe da bangon tana a tsakkiyarsa. Ƙasa tai da idanun nata da sauri tana ƙara damƙe towel ɗin data fisga tun miƙewarta ta suturta jikinta. Ƙasa ya farayi da hanun damarsa a hankali har zuwa kan makunnar shower, sai saukar ruwa kawai taji a kansu a bazata harta ɗan tsorata babu shiri ta ɗago, bazata iya jure kallon cikin idanunsa ba, dan wani irin al'amari daya girmi ƙwanyarta take hangowa a cikinsu da har suke neman sare ƙarfin gwiwarta, faɗawa tai jikinsa kawai ko hakan zai bata nutsuwa. Haka yake buƙata dama, ya saki ɗan murmushi da naɗe hanunsa duk biyu a bayanta ya rungumeta ruwan na cigaba da sauka a kansu. Kusan a tare suka saki nannauyan numfashi, cikin dabara ya janye towel ɗin da taketa faman riƙo yay ƙasa da shi, tsam ta matsesa dan bata buƙatar ya ganar mata jiki. Murmushi mai ƙayatarwa ya sake saki da ƙara matsetan shima yana saki wasu zafafan ajiyar zuciya a jere....

       Gaba ɗaya ya ƙulleta da kunya, tai wuff ta fara fitowa daga toilet ɗin da alama bakin tsuwar dai ya mutu, sai dai ko gaban mirror bata kai ba shima ya fito. Tana ƙoƙarin ɗaukar hijjab dan tasa ya riƙesa, saman gado ya wurgasa tareda ɗaura mata towel ɗin hanunsa saman kai ya fara tsane mata jiƙaƙƙiyar sumarta.
     “Har yanzu fushin ne dai baki huceba?”.
   Tayi kamar bata jisa ba, sai dai taɗan saci kallonsa ta gefen ido fuskarta a kwaɓe.
   Ya ɗan ɗalle mata lips. “Nifa bana son shariya”.
Bakin ta dafe da janye hanunsa da towel dake saman kanta zata bar wajen. “Ni karka sake kulani, kuma matarka ta daina shigomin sashe ban son gulma. Kuje can ku ƙarata kuma cinye kanku tsabar son kai”.
     Dariya sosai taso kufce masa, amma yay ƙoƙarin dakewa sai dai murmushinsa ya ɗan bayyana. Shima ƙarasawa yay gaban mirror ɗin inda takai zaune saman stool tana ƙoƙarin zuba mai a hanunta. Ta bayanta ya ranƙwafa tare da ɗaura kansa a wuyanta ya dafe duk hannayensa akan katakon mirror ɗin.
      “Mi matata kuma tayi? Ko zaki huce haushinnne a kanta. Faɗamin, wai *_BABU SO! MIYA KAWO KISHI?_*”.
   Dakatawa tai daga shafa man datai niyyar farawa, ta ɗago idanunta dake cikin gilashi suka haɗa ido ta cikin mirror. Da sauri ta janye nata tana cuna baki gaba. “Yaya kaima kasan SO ɗin da kishin. Da zaka rarrabe munma wlhy dana biyaka”.
        Murmushi ne ya sake suɓuce masa, yasa hannu ya karɓe man hanunta ya ajiye, sake ƙoƙarin ɗauka tai ya riƙe hannun. Dole ta ɗago tana kallonsa, hakan ya bashi damar da yake buƙata, ya sarƙe idanunta a cikin nasa yanda ya tilasta mata tsaiwa suka kurama juna ido, kallon juna suke irin na tsakkiyar idon nan mai ratsa jinin jiki da bargo ya sunce duk wani ƙwarin laka da jijiyoyi. A hankali lips ɗinsa suka fara motsawa...
       “Kin tabbatar idan na rarrabe mikin zaki biya ni?”.
    Da wani salon zamtowarta jiki a kasalance ta janye idanunta a slowly, shima janye nasan yay da wani salon lumshewa da buɗewa tare da miƙewa da ƙyau ya juyota suna fuskantar juna saboda kujerar na juyawa.
    “Yayaaaa!”.
Ta faɗa a shagwaɓe.
  “Yayoo”.
     Ya bata amsa da sake ranƙwafowa akanta tamkar ɗazun, banbancin kawai yanzu suna fuskantar junane. Turashi ta ɗan farayi amma ko gezau, sai ma hanun daya riƙe ya ɗaura saman fuskarsa daga gefen kunne. “Idan kin isa kalla cikin idona ki maimaita abinda kika faɗa”.
       “Ba buƙatar haka ai Yaya tunda nasan kaji. Aysha fa na gidan nan, kaima kuma matarka nacan na jiranka”.
    “Uhmm Madam pretender ke kuma budurwa tace ko?”.
   “Hu'um nayi me da kai? Kamun tsufa”.
          “Yanda kikai dani daren shekaranjiya mana”.
     Janye hanunta tai da ƙoƙarin juyawa tana faɗin, “Kai dai ka sani”.
   Yanzu kam ƙaramar dariya ya saki mai faɗi da miƙewa sosai akan ƙafafunsa. Yitai kamar bata jisa ba taci gaba da shafa manta yana kallonta kamar ya samu tv. Saukar kiran salla a kunnensu ya sakasa kallon agogon ɗakin, ya ɗan furzar da numfashi dan yasan sai ya sake sabuwar alwala.
      Binsa tai da kallo ta gefen ido, yana shigewa ta taɓe baki da miƙewa tana magana ƙasa-ƙasa. Kaya ta saka sauri-sauri kafin ya fito. Tayi ƙyau sosai dan ƙanan kaya sun zame mata jiki matuƙa, har takai komi ta raɓama ɗan jikinta sai ka ganta kamar ka sace. Kallo ɗaya ya mata ya ɗauke kansa, dan ya tabbata ya cigaba sunan alwalarsa karyayya again. Ita bama tasan yanai ba, powder take ɗan shafama fuskarta da ɗan lipsgloss, dan ko kwalli ba sakawa take ba sai Mamie ta tsaya a kanta. A ransa yake raya da kwalliyar tafi haka daya so, sai dai yasan ita ƴar darun tasa a wajenta hakan normal ne. A haka ɗinma tayi ƙyau sosai.
     Ita ko sanin kaya yake canjawa yasa taƙi juyowa, harya gama shiryawa cikin wandon jeans blue da pitch shirt mai dogon hannu. Jin tsaiwarsa a bayanta ya sata ƙoƙarin barin gaban mirror ɗin, amma saiya riƙota ta hanyar saƙala hanunsa saman cikinta ya manna bayanta da ƙirjinsa duk da bata kai har can sama ba. Ɗagowa tai tana kallonsa kamar yanda shima yake kallonta. Ganin ya ɗago lipstick da dayan hanunsa ta maida idonta akai. Saman lips dinta ya ɗaura, zatai magana yace mata “shiii!”.
     Shiru ta haɗiye abinda take son faɗar, shi kuma ya fara goga mata. Sai da ya gama ya juyota suna fuskantar juna, bakin ta ɗan tunzura gaba ganin yanda yake kallonta.
    “Nifa shanyewa nakeyi shiyyasa bana sawa”.
  “Oh really? To bara na shanye abuna kafimma ki shanye min”.
Idanunta ta waro waje da zaburowa zatai magana ya samu damar sauke lips ɗinsa akan natan. Dole ta koma tai laƙwas dan bai musu kamun wasa ba........✍


_Shareff adai rage cin amanarmu😚🚶🏻🤕._




_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*


YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902

IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇
09134848107


*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
[11/15, 11:40 PM] My Zafafa: *_Typing📲_*




*_❤‍🔥BABU SO....!!❤‍🔥_*
_(Miya kawo kishi?)_



*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

*_BABU SO👉🏻AREWABOOKS_*

https://arewabooks.com/book?id=63447a616580db4ec203d718


*_63_*


.........Tsaf ya shanye jambakin, zaune takai tana sauke numfashi, shima barin wajen yay da ɗan hanzari, tanaji ya buɗe toilet amma bata iya ta ɗago ba. Babu jimawa ya fito da alama wata sabuwar alwalar ya sakeyi. Ƙofa ya nufa batare daya yarda ya sake kallonta ba yana faɗin, “Ki tashi kiyi salla”.
       Iska ta furzar mai ƙarfi da dagowa tana kallon kanta ta cikin mirror, sai kawai ta samu kanta da kai hannu ta shafi lips ɗin nata da sakin murmushi. “Fitinanne”. Ta faɗa a hankali tana mikewa. Itama alwalar ta ɗauro, bayan ta gabatar da salla samun kanta tai da komawa gaban mirror ta sake gyara fuskarta da ƙyau cikin simple kwalliya. Kwalli, lipstick ɗin daya saka mata ta ɗan gyara girarta siririya da ƙara powder. Ita a karan kanta sai da ta tsaya kallon kan nata dan wani ƙyau taga ta kara, tai guntun murmushi da ɗaukar turare ta ƙarama jikinta..

          Ana idar da salla ya dawo gidan, saboda makara salla daya nema yi bai shiga sashen Fadwa ba ya wuce, yanzu kam daya dawo sai ya fara nufar can, wannan ƙa'idarsace, akowace salla in har yana gida sai ya tabbatar da mace tayi hankalinsa ke kwanciya, ko yana office yakan ƙokarta ya kira domin tambayar kinyi salla, hakan ya ƙara ƙarfafa Fadwa domin waya takan ɗauki hankalinta ta kasa tashi yin salla akan lokaci kafin zuwanta gidansa matsayin mata. A bedroom ya sameta ta idar da salla fuskarta duk babu walwala. Ya ɗan tsura mata ido na wasu sakanni kafin ya ƙaraso ciki sosai. Sau ɗaya ta kallesa ta janye idonsa da masa sannu ciki-ciki.
     “Wani abu ya faru ne?”.
Ya tambaya a maimakon amsa mata sannun da tai masa. Batai magana ba, sai dai ta sake ɗan tsuke fuska.
   “Nasan kin jini fa”.
Kamar bazatai magana ba sai kuma ta ɗago idanunta dake tara ƙwalla tana kallonsa, “Soulmate karka juyamin baya dan kayi aure, maƙiya zasu iya yimin dariya”.
     Mamaki shinfiɗe akan fuskarsa yake kallonta. “Juya baya kamar ya? Anyi wani abu ne?”.
      “In ma ba'aiba ga hanyar yi nan an ɗakko ai. Tunfa da matarka ta dawo gidan nan yau baka sake leƙoni ba, kana ganin hakan adalci ne? Yaufa ko zuwa kacemin na tashi nai salla bakayi ba, kuma tun ɗazun kana'a sashenta ita dan daga can ka wuce massallaci, gaka nan harda canja kaya alamar yin wanka”.
   “Dama kin saka a ringa miki gadina ne? Ko kuma shiga sashen nata ma akwai wata ƙa'ida ta mintunan da zanyi na fito? Ni da matata kuma kina tuhumata dayin wanka kamar wanda ya ajiye wata karuwa”.
       “Niba haka nake nufi ba, amma dai koyaya ai sai kana adalci. Jiya yini guda kuna tare a asibiti, hakama yau tun fitar safe da kai kuka dawo tare kana a sashenta”.
  Sosai ɓacin rai ya bayyana akan fuskarsa, idanunsa daya tsareta da su har suna canja launi. “Okay ke da sokike na watsar da ita kenan a asibitin nazo na tare a wajenki bayan nine sanadin zuwanta can. Ko kuma dan kar ranki ya ɓaci bazanyi wanka a sashenta ba?. Look Fadwa idan kikace zaki ɗaukemu zuwa wannan layin bazaki taɓa shan lalai a wajena ba. Idan kin manta bara na tuna miki, Juwairiyya matata ce, idan yanzu na shiga inda take ta rayamin kasancewa da ita zan samar da wannan farin cikin nai wanka na fito koda anjima hakan zai ƙara bijiromin idan ma wannan kikema zagaye-zagaye zargin nayi. K da ita duk abu ɗaya kuke a wajena, ina fatan kuma tsaida adalci akan kowaccenku. Duk wacce take da wani tuggu nason rinjayata gareta ita kaɗai na cutar da ƴar uwarta ALLAH ya hanata wannan damar ko wacece a cikinku. Abu na ƙarshe dazan gaya miki shine daga yau ki sani *_Ina son Juwairiyya!_* bawai cushenta akai minba kamar yanda na fahimci ke tunaninki ke kaiki. Yanda na aureki domin so bisa jagorancin iyaye haka itama na aureta, kuma koda ace iyayenmu basu ɗaura mana aure ba ni da kaina *_Zan nema aurenta_*, dan hakan burina ne, hatta wannan gidan da sunanta aka ginashi itama, kema shaidace tunda sashe biyu kika tarar. Kinga sai ki sakama zuciyarki salama, ki nisanta kanki da zama mai fuska biyu a gareni, dan bazan daina kasancewa da ita ba domin farin cikin. Sannan ita bata taɓa nuna damuwa da kasancewata a wajenki ba abinda ke gabanta takeyi, mtsoww stupid har kina faɗamin wai na dinga adalci”. Ya juya ya fice a fusace.
      Da gaske Fadwa tayi mutuwar zaune tun fara maida mata raddi da yayi, ga wata irin zufa dake jiƙa duk sassan jikinta sharkaf. Buga ƙofar da yay da ƙarfi ya sata zabura ta dawo hayyacinta, rawa lips ɗinta suka fara alamar magana take sonyi amma taƙi fita, sai kuma ta mike zumbur tana rarumar wayarta ta kunna fitila duk da kuwa ɗakin akwai hasken wutar nefa. Tabbas maganin data zuba ɗin gashi nan, sannan ya taka kuma ai kamar yanda Aunty Safarah da Mama suka tabbatar mata idan ya taka babu wani magana da zatai ya musa mata. Hakama zoben da suka bata na mallaka har biyu gashi a hanunta, sun kuma tabbatar mata mata da yawa suna rububin saya kuma yana aiki akan mazajensu. Mi (hakan ke nufi?) ta tambayi zuciyarta ƙirjinta na bugawa da sauri-sauri idonta ƙyam akan zoben mallakar dake a yatsanta tana murzashi da tunanin ko

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login