Showing 123001 words to 126000 words out of 186291 words

Chapter 42 - Halin Yau By Surayyah Dee

18 Dec 2025

9742

masa na ba zai gama da Hajiya lafiya ba, ya Fado masa, ya hassalo sosai.

Cike da ladabi ya ce "Ciwonta ba matsala ba ce ina sonta a haka, zan kuma kula da ita da iyakacin iyawata".

Da'di ya cika zuciyar Alhaji ya ce "Ubangiji ya maka albarka, ya rufa maka asiri duniya da lahira, Allah ya zaunar da ku lafiya"

"Iyayenta mata suna son zuwa yin jere na dakatar da su, akan sai mun tattauna, nasan baka shirya komai na auren ba, dan haka na gyara maka wani karamin gidana da ke LAMIDO crescent"
Ya ajiye mukulli tare da takardun gidan kusa da Mk.

A nutse Mk ya ce " Na gode sosai Alhaji amma ba zan karba ba, domin zan dinga jin tamkar Ina gidan mace ne, ina fatan kalamina ba zai zama laifi ba".

Sosai Alh Nasir ke nazarin Mk, yana jinjina masa, domin samun irin su da zuciyar su bata zarme ba, zai yi wahalar gaske, saboda yau muna cikin wani irin zamani da ake auren jari.

Da murmushi a fuskarsa ya ce "Mukhtar ina da tabbacin ko a gaban Farida na baka wannan gidan ba zai zame maka na'kasu ba, ba a shaidar 'dan Yau amma na shaidi Farida. Balle ma ni a satin nan na siye shi, ba kuma wadda yasan na siya, da sunanka na siye shi, Dan haka mallaka maka na yi ba aro ba".


"Na gode sosai, Allah ya kara arziki, amma ba zan karba ba, abawa masu son zuwa jere ha'kuri, ba zata tare ba, zamu tafi Uk ne, idan ubangiji ya kaddara mun dawo lafiya, Ina da 'karamin gida a gadon kaya sai ayi komai".

Ganin da mahaifin Farida ya yi da gaske Mk yake yi ba zai karba ba, sai ya bar maganar gida yana 'kudire dole ya masa wani abu na alheri komin dadewa.

Ya ce "idan nace ina son na dauki nauyin tafiyar iyalin naka fa, ko shima baka so?"

Kunya ta kama Mk ya sake yin kasa da kansa domin ya gaji da yin musu ya ce "Na gode sosai, Allah ya kara arziki".


Alh Nasir ya mike yana ta musu addu'a da fatan alheri, tare da cewa "Bari na turo maka ita".

Ba a dauki lokaci ba, ta iso cikin tsadaddiyar abaya baka sai walainiya take yi daga hannun rigar an masa ado da shudin duwatsu, dan haka ta yi anfani da shudin mayafi a maimakon na abayar, ba kwalliya a fuskarta tunda ita ba ma'abociyar adon fuska bace, kawai powder ta shafa sai wet lips sai tsadadden turaren ta na amour amour.

Soasai ta masa yi kyau, sai ya dinga tuno sadda yake zuwa zance wurin Iyah yana ce mata ta yi kyau tamkar balabiyar Habasha.

Ya zuba mata idon da suka yi jah tamkar mai fama da ciwon afolo, alhalin bacin ran da Sa'a ta jefa shi ne yake neman kassara shi.

A hankali cikin sanyin muryar ta gaishe shi ya amsa da karsashi.

Ya zuba mata ido sosai, kanta a kasa tana jin yadda kallon ke ratsata.

A hankali ya ce "ya jikin ki? Ko da yake kin warware, irin wannan kyau da kika 'kara yi tamkar balabiyar Yemen"

Kanta na 'kasan ta murmusa tana jin kunyar sa sosai.

Ya dinga janta da hira, har ta dan sake da shi.

"Na fadawa Dadi ba zaki tare ba, Ni Kinga nan da kwanaki biyar zan wuce, ke kuma da zarar visar ki ta fito, sai ki bini, abar maganar jere tukun yanzu".

"Allah ya nuna mana"
Ta fada a hankali.

Suka yi shiru. Na dan gajeran lokaci, Farida ce ta katse shirun ta hanyar cewa "Dadi ya baka aure ba tare da ka ce kana so ba anya ba'a takura ka ba?".

Tausayinta ya sake shiga jikinsa sosai! a hankali ya kira sunanta ta dago suka zubawa juna ido tsawon sakwanni, Farida ce ta yi karfin halin janye idanuwan ta saboda yadda take jin sonsa na sake dafa duk ilahirin jikinta, yadda idanuwansa suke a jirkice da kuma yadda suka yi ja sun sake jefata cikin matsanancin so.

Murya ba amo sosai ya ce "Na yi mamakin da kika yi tunanin aurenki zai zamo mini takura!
Tun yaushe muke soyayya da zaki ce na takura?"

Ta sunkuyar da kai kasa ta ce "kafin shigowar Gogel cikin rayuwar ka nasan muna soyayya, amma bayan ta shigo sai ta kashe tawa soyayyar".
Ta fa'da cike da rauni sosai.

Idan gaskiya zai fa'da yasan ba 'karya ta yi ba, amma dan ya faranta mata sai ya ce "Ba mutuwa ta yi ba dogon suma kawai ta yi, saboda ina ganin bani da halin da zan zo neman aure wannan gidan, Amma da yake ubangiji yasan yadda na ke sonki sai ya 'kaddara mini samun ki a lokacin da na cire rai, idan kinsan farin-cikin da nake ciki da baki yi wannan tunanin ba".

Ya nisa ya ce "tunda da bakinki kika sako maganar Sa'adah bari na fa'da miki wani Abu, kin san yanzu bama tare, amma idan ubangiji bai karar da zaman mu ba, zan dawo da ita, kar hakan ta faru a gaba ki ji a ranki kin gaza ne, sosai nake sonki Farida, sannan ba zan boye miki ba itama ina sonta, kaddara ce ta rabamu, Ina fatan wannan ya zama na karshe da za ki sako mini maganarta mussaman akan ina sonta ko saboda ita na rabu da ke a farko, an 'kadddara mini sai na fara aurenta ne kawai".

Sosai ta fahimice shi ta kuma gasgata shi, duk da ta ji fargabar da ya ce zai dawo da ita, ba dan ba ta so ba, sai dan kishin da kowacce mace ke da shi akan abin da take so, dan ma ta yi sa'ar na ta kishin mai sauki ne saosai.

Ta katse maganar da cewa
"Ya Hajiya da Jawad?"

My 11 amsa mata suna lafiya.

Ta sake fa'din"kun je anyi masa passport din?"

"Anyi masa sai dai da alamu visar ki zata riga tasa samuwa, kawai idan ta ki ta zaama ready, zaki taho ne, shikuma Mahmoud zai taho da shi nan da wattanni uku".

Yana rufewa ta ce "wallahi ba zan iya ba, kafata, kafarsa, sai dai nima na jira shi, ka riga kasa masa rai, sai kuma ya ga shiru, Ni bama zan iya zama da kai babu shi a tsakanin mu ba, ni ka'dai nasan yadda nake jin yaron nan a zuciyata".

Dadin kalaman ta suka kama Mk ya ce "wato saboda Jawad sai ki barni ni ka'dai, baki damu da halin da zan shiga adalilin rashin ki kusa ba?"

"To idan hakane sai ka yi kokari mu samu visa tare da shi".

Sosai suka sha hira mai cike da 'doki.
A ranar ta nuna masa yatsun kafarta guda biyu da suke a tankware , dan kar sai daga baya ya gano ya ji an yaudare shi, sosai ya sake jin tausayin ta, bai san me yasa yake jin tausayin ta ba tun fil'azal, ya yi ammana wannan tausayin ba zai barshi ya zalunce ta ba.

Har wajen harabar Adana motoci ta rako shi, anan ma sun sake bata lokaci suna hira.


Sai da ya koma gida ya kwanta tunanin ciwon Farida ya zo masa menene (Arthritis?).

Da tunanin ciwon barci ya yi awon gaba da shi, yana karyawa kuwa bai zame ko ina ba sai asibitin kwararru na Murtala, ya samu Dr Babangida Bojuwa abokin kaninsa ne Akil, suka gaisa sannan ya nemi alfarmar ya masa bayanin menene ainihin ciwon Arthritics da hanyar da za'a bi a kula da mai fama da wannan ciwon.

Dr Bojuwa ya yi murmushi sannan ya cire gilashin idonsa wadda yake taimaka masa wurin gani sosai sabanin da mutane suke kallon tamkar na ado ne.

Cike da girmama yayan abokinsa Dr Bojuwa ya ce "Zan maka bayanin da harshen Hausa tunda kai Baban turanci ne, gara na adana turancina da bai fi cikin cokali ba".

Da murmushi a fuskar Mk ya ce " kowa a fanninsa gwani ne 'kanina, baka ga takakkiya na yi domin ka sanar da ni abin da ban sani ba?"

"Hakane yayan mu".

Dr Bojuwa ya ce "A likitance an fassara Arthritics (Ga'ba) da mahadar kasusuwa biyu zuwa sama. Ba iya 'Kashi ke bada abin da ake kira ga'ba ba!
Muna da ga'bo'bi da yawa a jikin 'Dan Adam amma anraba su zuwa manya biyu mafi shara wato masu motsi da marasa motsi".

Dai-dai lokacin Dr ya nisa sannan ya zarce da fadin "(osteoarthritis) wannan nau'in shine yafi yawa yana farawa adalilin kokewar shimfidar kawunan kasusuwan(articular cartilage) wacce take hana kasusuwa gogar juna yayin motsi, daga karshe hakan na janyo sidewar kawunan kasusuwan da kuma curewar su zuwa 'Kashi guda daya.
Wannan nau'in na faruwa adalilin jin rauni a ga'ba ko shigar kwayoyin cututtuka".

"Na'aam" Mk ya furta cike da gamsuwa.

Dr ya cigaba da cewa "sai kuma na biyun (Rhematoid arthritis) mai farawa da kumburin shingen gabobi, wannan nau'in yana farawa da kumburin da ya zagaye gabobi wanda ya ke samar da ruwan gabobi. Daga baya kuma ya cigaba har ga kokewar shimfidar kawunan kasusuwan. Wannan nau'in na faruwa ne sammakon rikicewar Garkuwan jiki har ta kai suna yaki tare da lalata shingen da ya zagaye gabobi wato(synovial membrane).

Cikin nutsuwa Mk ya fahimci Farida na fama da ciwon Arthritics nau'i na biyu wato (Rhematoid arthritis). Dan haka ya ce "Na gode sosai Dr! Na gamsu da bayanin ka, amma me yake kawo wannan ciwon?"

Cikin rashin gazawa Babangida ya ce "zuwa yanzu dai an tabbatar tasirin wannan ciwon ya hada da
GADO- ana iya gadar wannan ciwon idan an samu wani a ciki dangi yana da wannan ciwon ma'ana yana bin jini.
SHEKARU- yawan shekaru na tasiri sosai wurin samuwar wannan ciwo.
MATA-Jinsin mata sunfi kamuwa da ciwon Rhematoid arthritis yayin da jinsin maza suka fi kamuwa da (Gouty arthritis).

NAUYI- nauyi fiye da kima na jagorantar kamuwa da wannan ciwon, da kuma buguwa a gabobi".

Kafin Mk ya yi magana Dr Babangida ya sake cewa "kalubalen da masu wannan ciwon suke fuskanta bayana rad'ad'in azabar ciwon, sun hada da Tankwarewar yatsu, hannu ko kafa, ciwo yayin motsa gaba, kumburi sosai a gabobi, dama daina aikin gabobin gaba'daya".


Mk ya ce "Madallah da hazikin Dr! shin wanne shawarwari zaka bani don kulawa da mai fama da irin wannan ciwon?".

"To shawarar da zan baka kasancewar wannan lalura kusan ta dindince, ma'ana za'a tabbata ne ana s!han magani. Mafi soyuwa a inganta abincin marar lafiya, a yawaita masa cin kifi, a karanta masa cin nama mussaman Jan nama.
Da kuma yawan motsa jiki da shan maganin da likita ya 'dora mai lalurar akan ka'ida, sai kuma rage kiba ga masu ita".

Mk ya mika masa hannu tare da cewa"likita na gode sosai da lokacin ka da ka bani tare da mini cikakken bayanin da na gamsu, ina rokon ubangiji ya yiwa rayuwar ka albarka, ya kara maka ilimi mai albarka, ya sa sunanka ya yi fice a cikin 'kasa da waje".

Babangida ya amsa da cewa "Amin Nima na ji 'Da'din yadda ka nemi bayanin likita, baka tafi kanka tsaye siyan maganin rage rad'ad'in ciwo ko kumburi ba, domin yawan shan irin waddanan magagunan na janyo ciwon ulsa da ma gazawar 'koda bagatatan, ubangiji ya bamu lafiya gaba'daya".

Har wajen ofis din Dr Bojuwa ya rako Mk dan karramawa ga yayan abokinsa Akil, Mk yana ta masa fatan alheri da samun mace ta gari, tare da jinjina fasahar Babangida, yana hakaito sadda yake biyowa Akil makaranta, oh rayuwa gaibu ce, ba wadda yasan me gobe zata zo da shi.

Yana tafe yana tunin bashi da matsalar gwajin rukunin jini, tunda tuni yasan Farida A.s ce yayin da ya kasance A.A basu da matsala, kawai fargabar sa daya ciwon da ta ke faama da shi ance ana iya gadarsa kenan akwai yiyuwar ta haifa masa mai irin ciwonta.
Alatilas zai yi auren nan, ko dan ya nuna mata martanin soyayyar da ta wanzu tana masa ba gajiyawa amma a zahirin gaskiya kaso mai yawa na zuciyar sa da gangar jikinsa gaba'daya Sa'adah suke so, da ita suke son su rayu muddin rai, shi da kansa yasan hukunta kansa yake yi da rashinta.

Yana tu'ki yana ayyano cikakken dirin jikinta bata da rama kamar Farida, duk da a yanzu ta tsiyaye, amma ya yi imani da zarar ta dawo hannunsa komai da ta rasa zai dawo mata tunda zata sami nutsuwa, ga iya girkin gargajiya tamkar Innarta, ga ga gayu, kullum tamkar mai Shirin shigaa gasar kyawawa saboda kwalliya. uwa uba ta kasance mace mai lafiya, A.A ce sannan O positive duk wadda ya san darajar lafiya ya san wadda ubangiji ya hada musu wannan nau'ikan ba karamin ni'imomin ubangiji suke ciki ba.

Kalamanta na karshe ya fado masa wai idan ya sake tura mata kudi ba zai gama da uwarsa lafiya ba! Bai taba ganin inda abin arziki ya zama sharri ba sai a gurin Sa'adatu.

Ba 'karamin bata masa rai wannan kalmar ta yi ba, bayan tasan ita mai laifi ce, ya tsani kaifin harshe, umm

Kusan Wannan bacin ran da ta haddasa masa ya rage masa fargabar auren Farida da yake ji.

Washagari asabar dai dai da 17/09 aka daura auren Mukhtar Kabir Bichi, da Farida Nasir Torondi.
Daurin auren da ya samu halarta manyan mutanen na Nijer da Nigeria.

Sosai aka yi hidima ta bangaren amarya, duk yadda Farida ta so ya halarci Dinner da zata yi a harabar gidansu ha'kuri ya bata, bai je ba, yana ji a ransa tunda bai yi irin wannan sha'anin a bikin Iyah ba, to yanzu ma ba zai yi ba da yake da shekaru talatin har da tara.

Bangaren Iyah kuwa sai da aka daura auren ta gane Farida ya aura.
Duk yadda ta so yin jarumtar boye yadda auren Farida ya bugeta kasawa ta yi, ta fito daga dakinta, daidai lokacin Baffanta ya dawo daga wurin daurin auren ya ci sabon dinki tamkar yarsa yake aurar wa.

Tana tsaye tana kallonsa , sai kuma ta fara ganinsa bibbiyu, basu ankaraba suka ji tim ta zube a kasa.

Dukkansu suka kai mata dauki, tsawon lokaci ana kanta har sai da aka kira Maman Ema wata kwararriyar nurse ce har ta kai mukamin metron, ita ta dinga dawainiya da ita har ta farfado, tana fa'da musu jininta ne ya yi kasa sosai adalilin rashin samun barci da kuma damuwa da ta sanya a ranta.
Kwana biyun da suka biyo baya ba karamin tsauri suka yiwa Sa'adah da iyayenta ba, domin ba karamin wahala ta sha ba, har zabura take ta kwasa da gudu, gaba'daya ta gigice ta fita a hankalin ta, ba kuma komai ke damunta ba illah matsananciyar damuwa wato (Desperation).

Yadda take zabura da suratai ya matu'kar tada hankalin ahalinta mussaman Inna da ta ke uwa, ansan kuwa raunin uwa akan danta.
Bayan maganin asibiti har rubutu Baffa yake zama da kansa ya ke mata wadda na dangana ne da samun sukunin zuciya.

A wannan lokacin Inna ta kudiri aniyar Mukhtar ko shine namiji tilo a duniya da ya hallata Iyah ta yi zaman aure da shi, to kuwa ita ta Haramta mata shi, wannan abin da ya yiwa Iyah ta tabbatar ya yi tsauri da yawa ya wuce laifinta, ta yi imanin 'yarta ba zata yi zina ko sata ko wani mugun kaba'irar da zai kasa yi mata afuwa ba, ta lura so yake ya susuta mata yarinya ya sa zuciyarta ta buga, tunda shi bashi da asara ya angwance da 'diyar masu kambun susa.

Asalima Inna sai take ganin tamkar so yake ya shafawa Sa'adah kashin kaji. kuma raina arzikinsu ya yi.


Kwanaki biyu suka ragewa Mk ya wuce, ya dauki Farida da hantsi suka je ta gaida Hajiyar Bichi, duk yadda Hajiya take jin dama Sa'a ya dawo da ita, ta karbi Farida da sakakkiyar fuska, yayin da Jawad ya ke ta murnar Malam ya ce zasu bishi Ingila a jirgi da wannan balabiyar Auntin. Dai dai lokacin shekarun Jawad goma.


Kunyar Farida da sanyin ta yasa Hajiya ta dan rage 'kin data ke yiwa auren na su.

A hanyar su ta komawa gida ta ga ya sauka daga kan titin da zai bi ta unguwar su, ya hau wani daban.

Bata ce kala ba, ta zuba masa ido kawai.
Bai tsaya ko ina ba sai a harabar hotel din Tahir.

Jikin Farida ya yi sanyi sosai, ta shiga cikin rudani da fargaba, amma haka ta bishi, har dakin da ya riga da ya kama a safiyar yau, domin taga a aljihunsa ya fito da mukallin daki mai lamba 008.

A dadare ta shiga ta zauna, shikuma ya juya ya fita, ba'a jima ba ya dawo da leda mai dauke da yougurt da gasasshen kifi, sai lemuka masu sanyi hadi da ruwa.

Ka'dan ta dan ta'ba adalilin matsawar da ya mata, shi kuwa da dama yunwa yake ji sosai ya ci, sannan ya shiga ya yo wanka, ya fito daure da tawul iya kugunsa.

Mk da kansa ya dinga mamakin kansa bai yi zaton zai ji sha'awar wata macen bayan Sa'a ba, bai yi zaton zai yi rawar jiki har ya kasa ha'kuri su isa Uk kafin ya tare da amaryarsa ba, amma abin mamaki jiya kwana ya yi yana juyi, rabon da ya shiga irin wannan yanayin ya manta, bai sani ba ko dan yasan bai da wadda ta halatta a gare shi ne.

Ganin abin na neman kassara shi, shiyasa ya murje kunya ya je har gidansu ya daukota da zummar zai kaita ta gaida mahaifiyarsa sannan sisters dinsa na son ganinta sosai.

Sanin mijinta ne yasa ba a nemi ba'asi ko fargabar fitar su tare ba, asalima kyakkawan shiri aka mata, domin turaren da mahaifiyarta ta dinga bin duk wata ga'ba tana shafa mata na alfarma ne, takanas ake yiwa manyan matan da suka amsa sunansu a sanin duniyar kamshi.
Sannan ta bata wani irin tsumi da tunda aka fara aurenta kullum sai ancika mata ciki da shi, akan Dole Farida ke Sha, saboda kasancewarta masaniyar magaganuwa bata yarda da Shan kowanne irin abu da sunan magani ba.

Wannan kamshin ya sake rikita Mk yana jin tamkar wani maganadisu ke jansa ga Farida, shi ka'dai yasan yaddda ya kosa su kadaice.

Duk yadda Farida ta ke da kunya ta yi iyakcin bakin kokarinta ta bashi hadin kai, duk da yadda ta ke cin kwakwa a hannunsa kasancewar ita din cikakkiyar budurwa ce ta daure ya samu nutsuwa sosai.

Koda ya kammala kifa ta ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login