Showing 51001 words to 54000 words out of 186291 words
takaici sosai Inna ta ce, "To labarin abin da kika aikata ya same shi."
Ganin hawaye ya kwace ma Sa'adah ya sa ta hadiye fa'dan da za ta fara yi mata, sai ta bige da fadin, "Kadan ke nan a cikin sakamakon da mai yin 'karya ya ke fuskanta."
A ranta kuma tana raya dole su yi magana da Baffa akan rashin zuwan MK shirun ya yi yawa.
Washegari Zainab ta kawo mata ziyara, suna zaune kan katifarta, "Sa'adah me yake damun ki haka?" Zainab ta fada cike da mamakin ramar da ta ga Sa'adah ta yi.
Bata boye mata halin da take ciki ba, ta zayyane mata komai.
Cikin takaici Zainab ta ce, "Ai indai kina biye su Safina sai sun kai ki sun baro, ka'dan ke nan."
Tana kuka ta ce, "Ni yanzu ki nemo mini mafita don Allah!"
"E ai yanzu da yake ta kwabe miki za ki neme ni, amma lokacin da kika bi su ai ban sani ba."
Waya ta mi'ka wa Sa'adah tana fadin, "Saka lambar Uncle Mukhtar din mu kira shi da layina." Jikinta na rawa ta karba ta hau jera zababbun lambobinsa, tana fatan Allah ya sa ya dauka tunda har layinta da bai san da shi ba ta sha 'kiran ba ya 'dagawa.
Cikin Sa'a kuwa ya dauka! Zainab ta gaishe shi, ya tambayi wacece?
Ta amsa da gabatar da kanta, sai ta shiga ba shi ha'kuri a madadin Sa'adah, ya yi shiru har ta gama.
Ya yi murmushi mai sauti sannan ya ce, "Ba dan ina ganin hankalinki ba da ba zan saurare ki ba. Ki yi hakuri, ki cire kanki a cikin wannan maganar, ba zan iya da halin yarinyar nan ba, duk yadda nake zaton ta ta wuce nan". Yana fadin haka ya katse wayarsa.
Bugun da zuciyarta take yi ya sake tsananta, a rikice ta ce "Zainab mai yake nufi? Ya fasa yi da ni ke nan?"
Cikin son ta kwantar mata da hankali ta ce, "Ba fasawa zai yi da ke ba In Sha Allah! Kawai ya yi fishi ne sosai, ai kema kin san ba ki kyauta masa ba."
Ta dade tana kwantar mata da hankali, kafin ta mata sallama ta tafi da al'kawarin za ta sake tuntunbar sa.
Kwanaki biyu da zuwan Zainab, Anty Sumayya ta yi waya Sa'adah ta je ta karbo mata sa'ko a karkasara gidan kawarta.
Akan dole Inna ta barta ta fita bayan ta sha jan kunne da nasiha iri-iri akan kar ta biya ko ina, har kunya ta kama Sa'adah ta na jin ita ta janyo wa kanta rashin yarda a idon iyayenta.
Tana karbo sakon ta juyo, duk da yadda Anty Walida ta yi nacin ta zauna ta karasa yi mata yinin, ita kuma ganin biyu da rabi ta yi yasa ta gaggauta fitowa dan ta zartar da kudirinta na son ganin Mk a yau.
Kai tsaye FGC Kano ta sauka, sai dai ba makarantar ta shiga ba, gangare can gefe ta tsaya inda suka ta'ba tsayawa da shi, ta san kullum ta nan ya ke bi. Cikin sa'a kuwa ba ta dade tana jira ba ta hango shi, yana doso inda take, a kafa yake tafiya. Ta ce, "Ko ina ya baro dan mashin 'din?"
Sanye ya ke cikin 'kananun kaya yana rataye da jakar da yake zuba takardun shi, ya mata kyau sosai duk da ta ga ya dan zube kadan.
Sai da ya wuce ta sannan ta bi bayansa, jin ana ta bin bayansa yasa shi jiyowa, ba zato idanunsu suka sarke, ya hade girar sama da ta kasa tamkar bai ta'ba dariya ba, ya juya ya ci gaba da tafiyarsa tamkar bai gan ta ba.
Sai lokacin ta yi magana "Uncle na yi kewar ka, idona sun yi kukan rashin ka!"
Ya ji ta sarai, bacin ransa ya dawo sabo, ya rasa wane matakin zai ajiye Sa'adah, duk inda ya ke ajiye ta, yau ya tabbatar masa ta kere gurin!har ta san ta bi saurayi gun aikinsa?
Ita kuma ganin bai kula ta ba har sun fara hango titi sai ta fara masa kukan da babu hawaye tana kuma fadin "Zuciyata ba za ta iya daukar fishinka ba, ka kalle ni ka ga yadda fishinka ya ramar da ni, ba na iya barci, ba na iya cin abinci, kamin afuwa, don Allah ba don halina ba!"
Ta fada cikin wani irin yanayi mai motsa ZUCIYA.
Ya juyo ya zuba mata ido tabbas ta rame, ta birkice amma hakan bai yi tasiri a zuciyarsa ba, musamman da ya tuno kallon rainin da Khalil ya yi masa, ya sake hango yadda ta fito a gaban motarsa, sai kawai ya juya ya ci gaba da tafiyarsa ba tare da ya ce mata uffan ba.
A kidime ta ru'ko hannun jakarsa murya na rawa ta ce, "Na san na yi ba daidai ba, na ba ka ha'kuri, ka yi hakuri mana!"
Bacin rai sosai a fuskarsa ya dube ta sannan ya ce, "Ke ba na son ballagazanci, a titi za ki ri'ke ni?"
Ba'kin ciki ya kama ta ta fara kukan gaske ta ce, "Ni ka kira da ballagaza?"
Kishi ya rufe mai ido sosai, ba wani ja-in-ja ya ce, "E, idan akwai sunan da ya fi haka muni ma ki hada da ballagazar, don kuwa sunayenki ne, dabi'un da kike yi irin nasu ne. Yanzu kuma kin nuna mini kin saba cu'danya sosai da maza, har kike ganin za ki iya cakuma ta a titi."
Ba'kin ciki ya turnuke ta, ba a taba yi mata tozarci a rayuwarta irin na yau ba, kuka sosai take yi wanda ya matu'kar taba shi, kawai waskewa ya yi. ba tare da ta sake fadin komai ba, ta yi gaba da sauri ba ta ko sanin inda take jefa kafarta saboda tsananin 'bacin rai.
Al'kalamin
*Surayya Dee*
✍🏼✍🏼✍🏼
🌺 *HALIN YAU*! 🌺
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```
```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________
https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_Dokɑr hɑkkin mɑllɑkɑ me lɑmbɑ tɑ 68, tɑ nunɑ cewɑ sɑtɑr fɑsɑhɑ bɑbbɑn lɑifi ne dɑ yɑke dɑidɑi dɑ sɑtɑr dukiyɑ._*
*A guji taba ko sarrafa labarin nan ba tare da izinin mai Hakkin mallaka ba*.
*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*.
*TALLAH*.
_Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number...... 08089965176 domin karin bayani, maganin ya samu lambar yabo saboda ingancinsa, yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k'iba dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka fara amfani da maganin zaki ga sauyi, domin yana gyara mace, zawarawa da 'yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!...ga masu bukatar sari ko sayan d'aya muna KANO muna turawa kowane gari 2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi.......*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya 'kare da ikon Allah._
47-48
A gigice ya ga ta nufi titi gadan-gadan tamkar zararriya, zuciyarsa ta buga, da azama ya bi ta ganin da gaske tsallakawa za ta yi ba tare da ta duba ba. A ki'dime ya fuzgo ta, ganin mota na shirin yin wasan-kura da ita, amsa-kuwwar motoci sun cika gun, har sai da mai motar ya tsaya ya fito ya dinga zazzaga mata sababi, yayin da ita ko kallo bai ishe ta ba illa fizgewa da ta yi daga ri'kon da MK ya yi mata, ta koma gefe tana hawayen ba'kin cikin maganganun da ya gasa mata.
Sai da ya ba wa mai motar hakuri ya tafi sannan ya tsayar mata da Adaidaita Sahu, juyin duniya ta ki hawa, har mai Adaidaitan ya ji haushi ya yi tafiyar sa.
Ya kalle ta ya ce, "Watau da ma zuwa kika yi ki sake tayar mini da hankali ko?"
Yana rufe baki ta ce "Kadai so hankalin naka ya tashi ne, ha'kuri na zo ba ka, ka ki ha'kura. Ka bi ni da kalaman muzanci, to ai sai ka yi tafiyarka tunda da ma ba kai ka kawo ni ba balle ka ce sai kasa na koma dole."
Ya kalle ta ya ga tana cikin fishi irin wanda bai taba ganin ta yi irinsa ba, sai ya sassauta ya ce,
"Na ji ba ni na kawo ki ba, amma kin ce gurina kika zo, idan kuwa haka ne to ba na son zuwan. Ki koma gida ni zan zo."
Kamar ta ce "Ba na son zuwan naka ni ma!" Sai ta daure ta kalle shi ta ce, "Nasan ba da gaske ka ke ba."
"Zan zo mana da gaske nake."
Ta yi shiru tana rantsuwa a ranta ba za ta yarda da maganganun da ya yi mata ba. Dolensa sai ya janye ko ya ga tashin hankalin da ya ke kirari.
Ya kalle ta ya ga ta turo bakin nan gaba, mamakin yadda ta ke son mayar da laifin da ta masa ya koma kansa ya ke yi.
"Kin yarda na tsayar miki da abin hawa?"
Shiru ta yi masa alamun ba ta yarda ba. Ya kalle ta ya ce, "Magana nake miki."
A gajarce ta ce "Ban yarda ba!Yawon ballagazan ci zan wuce."
Ji ya yi kamar ta wasta masa ruwan dalma a zuciyarsa, ya hassalo sosai ya nuna ta da yatsa ya ce, "Ni kike yi wa magana kamar kina yi da sa'anki? Saboda ba kya ganin girma da mutuncina?"
Ta yi mai shiru ta kasa cewa komai. Ya sake cewa "Ki dinga sanin abin da za ki na fada mini ba na son kau'din baki."
Duk yadda ya so ya tafi ya bar ta a gurin kasawa ya yi, ita kuma ta kafe akan ba za ta tafi ba, shi ya yi tafiyarsa ya 'kyale ta.
Da kyar da jubin goshi ta yarda ya tarar mata Adaidaita, bayan ya rantse zai zo gida ya same ta, sannan zai 'dauki kiran ta.
Yana tsaye yana kallon su har suka bar wajen. Wata ajiyar zuciya da bai san yana ri'ke da ita ba ta kwace, a fili ya ce "Wacce irin yar daru na kwaso wa kaina ne? Da motar nan ta taka ta, ina take son na sa raina? Me zan ce da iyayenmu idan aka gane muna tare ta sami wannan hadari?
Ya dade a tsaye yana mamakin irin son da yake wa Sa'adah. Ya dauka idan ya gan ta ba zai ji komai ba, ya dauka kaifin son ta ya dakushe, ashe ya nan daram. Musamman da ya ga mota na shirin take ta sai ya ji zai iya rasa ransa don ya tserar da ita, ko muzuran da ya mata na karfin hali ne kawai da son kwatar kansa a idonta.
Tana isa gida ana sallar La'asar, sai da suka yi sallah sannan ta ba wa Inna sakon da ta karbo, ta koma daki ta hau kiran MK.
Sai da ta kira har sau uku bai 'daga ba, shi kuma ya fito a Masallaci ke nan kiran ya shigo, bai daga ba sai da ya koma dakinsa ya kwanta sannan ya 'kira ta.
Har ta fara hasashen da ma zai iya rantsuwa akan 'karya? Sai kuma ta ga kiran sa ya shigo, da sauri ta dauka sai kuma ta yi shiru ta tura baki gaba tamkar yana ganin ta.
Shiru ya biyo baya tamkar ba kudi ke bin iska ba.
A shagwabe ta ce, "Na gode!"
Ya ce, "Godiyar me kike yi?"
"Ka cika al'kawari, don Allah ka yi ha'kuri wallahi na horu ba zan sake yi maka laifi ba."
Ta fa'da da rauni a muryarta.
Jikinsa ya mutu, wata irin kasala da ba ta da nasaba da gajiya ko barci ta lullube shi, murya a dakushe ya ce, "Kin bata mini rai, kin tayar mini da hankali, kin jefa ni cikin wasi-wasi mai yawa, kin janyo mini raini."
"Ka yi ha'kuri!" Ta fada da sauri.
Shiru ya yi ba tare da ya yi magana ba, saboda yadda ya ke fama da kansa, ji yake ina ma ya jita a jikinsa.
Murya ba amo sosai ya ce, "zan fada miki, ba na son yaron nan. Ina bakin cikin tarayyarki da shi, wannan ne karon karshe da zan miki afuwa a kansa, ba don girman son da nake miki da kunyar Baffa ba da na ha'kura da ke Sa'adatu. Saboda kina cutar da ni, da ni kika gani da Farida da ban san kalar tashin hankalin da za ki mini ba. Amma saboda yadda nake son ki, na ke gudun bacin ranki haka na rufe ido na rabu da ita da dukkan lamarinta. Ni kuma kin kasa tsayawa gare ni ni ka'dai."
Yanayin muryarsa da yadda ya ke maganar cike da rauni sai ita ma ya jefa ta cikin wani irin yanayin da duk mai lafiya ba zai iya kauce masa ba, tsikar jikinta har tashi take yi.
"Am sorry!" Ta fada a gajarce tana jin ina ma inama...
"Shike nan ya wuce amma kisa a ranki cewar yaune karon karshe da zan saurare ki na miki afuwa akan Khalil".
"Na gode my love!"
Mamaki ya kama shi, karon farko da ta kira shi da wani suna bayan Uncle.
Ya ce, "maimata abin da kika ce?"
Dariya ta yi "Thank you na ce!" Sai ya saki maganar ya ce, "Ba ni labari."
Haka suka sha hirarsu cike da Begen juna, dukkansu sun tabbatar sun yi missing din juna, sun kuma yarda farincikinsu na hannun junansu.
Washagari da yamma ya zo, ba Sa'adah kawai ba, hatta Inna sai da ta yi murnar zuwansa, hira suka yi cikin tattalin juna, har ya ba ta labarin irin gyaran da yake mata a gidan da za su zauna.
Tun daga wannan lokacin Sa'adah ta yanke hul'da da Khalil saboda ba karamin tashin hankali ya janyo mata ba.
Hankali ya kwanta sun shirya da MK amma ta 'kullaci kalmar ballagazancin da ya jefe ta da ita ba ka'dan ba, ta kuma ci alwashin maganar ba za ta bi iska ba, lokaci ta ke jira.
Haka kwanaki suka yi ta zuwa suna wucewa, har watan azumi ya kama al'ummar Musulmai kowa ya koma ga Allah ana fatan dacewa da Rahamar Ubangiji.
Zuwa wannan lokacin shirye-shirye ya yi nisa a bangaren MK, an kammala gyaran gida, gyaran da ya dawo da gidan tamkar sabo.
Mahmoud ne ya hado wa Sa'adah kayan shan ruwa da kayan sallah masu tsada har set biyar da takalmi da jaka set uku sai tarkacen kayan kwalliya da turaruka. Tare suka kawo mata, da za su tafi kuma ya sake ba da kudin 'dinki wanda ta 'ki karba sai da MK yasa ba ki sannan ta karba.
Yawan kayan da kuma tsadarsu ya dan rage mata damuwar rashin lefe musamman idan ta tuna tana da kayan wurin Alh Mamman a ajiye.
Ana yin sallah da sati 'daya iyaye da 'yan'uwan MK suka hada kudadensu, aka sayo dukkan abin da za a bukata, tun daga kan gado da kujeru masu kyau da aminci suka sayo aka shirya gida ya fito sosai, labulaye da carpet suka ajiye sai satin biki za a zo a saka.
MK da ya je ya ga irin kayan da aka zuba masa sai da ya yi hawayen farinciki, ya duba ya ga an 'kawata dakin Sa'adah da dan'kareren gadon da duk fariyarta ba za ta raina ba, ga kujerun ma masu kyau, ba irin gama gari ba, dayan dakin ne kawai aka malale shi da carpet aka bar shi empty, bai sha mamaki ba sai da ya shiga dakin dake tsakar gida wanda shi ne mallakinsa, an saka masa gado amma bai kai na dakin amarya ba, kowanne gado kuma da dimemiyar katifar Vitafoam a kai.
Ya zauna a bakin gadon yana goge idonsa, yana mai yin addu'a ga dukkan ahalinsa, sun masa zumunci ba ka'dan ba.
Ya zauna yana ganin TV da Fridge kawai ya rage wanda su kuma yayarsa Hafsatu ta ce ta aiko da su. Isowa ne ba su yi ba tunda a Lagos take.
Alhaji Isa shi ya sake komawa wurin Baffa ya ce idan ba damuwa suna son a yi auren a cikin sati biyu masu zuwa.
"Yadda ka ce ba ka bu'katar komai a gurinmu sai sadaki, mu ma muna ro'kon ka!Yarinyar kawai muke so don Allah!"
Suka rabu cikin walwala, tare da addu'ar albarkar Ubangiji a cikin auren.
Duk da Baffa ya ce ba zai mata kayan 'daki ba, kan dole ya karbi tsalelen gadon da mijin Sumayya ya aiko masa. Sumayya na zuwa ta nunawa Inna ku'din da za ta kashewa Iya, ita ma ta fito da nata ajiyar ta hada suka shiga kasuwa tare da Sa'adah, suka zabo kayan kicin na garari duk a 'ko'karinsu na kwantar mata da hankali, tunda sun san halinta na son kayan 'kawa.
Hatta kayan fitar biki masu kyau aka tanadar mata shike nan sai hankalinta ya kwanta. musamman da Sumayya ta ha'kur'kurtar da Baffa ya yarda za a kai mata gadonta 'kirar Dubai.
Kafin ranar 'daurin aure gidan amarya ya fito fes komai ya ji, Sumayya ta yaba 'kwarai da kokarin MK da iyayensa, saboda haka sai ta sa aka mayar da gadon dake dakin MK zuwa dakin dake cikin falon wanda babu komai a ciki, shi kuma aka saka masa hadadden gadon Dubai.
Kicin aka sake 'kawata shi da tsirarrun kayan alfarma, aka rufe gidan ana jiran isowar TV da Fridge da kuma amarya! don Mk tuni ya tare a cewarsa gadi yake yi.😁
*05/06*
Ranar aka daura auren Mukhtar Kabir Bichi da Sa'adatu Bashir Gogel, a Masallacin Sahaba dake Kundila, kamar yadda Baffa ya ce ba za a yi party ko ka'de-ka'de ba hakan ce ta kasance.
Amma kuma ya tsaya an yi abincin 'daurin aure da yini na fitar kunya, duk wanda ya halarcin auren Sa'adah mace ko namiji ya ci abinci mai rai da lafiya don kuwa Bijimin sa Baffa ya yanka, duk tanadin Baffa a shirya abincin fita kunya