Showing 159001 words to 162000 words out of 186291 words

Chapter 54 - Halin Yau By Surayyah Dee

18 Dec 2025

9735

tsufa, tana nan da kyaunta, mai kyakkawan jiki ce da yake boye tsufa. Wata'kila haka mahaifin su yake, dan ta lura ba kammanin Inna a tare da Gogel, Sumayya ta fi kama da ita, wanda hakan na alamta cewa mahaifinsu ma ba baya bane.


Sumayya ta 'karewa Farida kallo tsab, takaicin Iyah na kamata da ta dinga kukan Mk ya auri Farida dan ta fita kyau ne, a yau da taga zahairin Farida ba hoto iya fuska ba, sai take ganin ba karamin kerewa Iyah ta yi mata ba. Kawai fararen mutane suna da kwarjini ne ta yadda ake ganin kyaunsu ko da kuwa masu 'karancin kyau ne.


Farida bata dade da isowa ba, su Inna suka yi sallama suka tafi.

Suna isa gida suka tarar da Sa'adah cikin kwalliya ta birgewa, amma tana kwance a falo tana kallo.

Inna ko zama ba ta yi ba, ta hau ta da fa'da "Iyah cewa ki ka yi zaku tarad da mu a asibitin tare da Zainab, ashe karya kika yi mini?"

Cikin rashin damuwa ta ce "na shirya jiranta nake yi".

Kafin Inna ta sake magana Zainab ta kira wayarta, sannan suna jiyo horn dinta tabbacin ta fita, ba shigowa zata yi ba.

Ta mike tana fa'din "gata nan ma, sai mun dawo".

Sumayya ta ce Yanzu irin wannan kwalliya tamkar kin manta asibiti zaki ba gidan biki ba?".

Dake Yan darun akusa suke ta ce "Anty ke kika manta cewa ni wannan ban dauketa kwalliya ba, domin ko a gida haka nake".

Da sauri Sumayya ta ce "gaskiya ce sai na fa'da miki, Hajiyar Bichi na gurin, duka danginsa suna gurin, ki je dubiya cikin irin wannan kwalliyar tamkar me shirin shiga gasar miss Beauty. Ba nadama ba komai a al'amuranki".

Inna ta ce "ta shi ki wanke fuskarki sai ki dauko Hijabin ki dora, ai kinsan yadda hijabi ma yake karbar ki".

Ta mike tana kunkuni wadda yake nuna Sumayya ta fitineta da yawa, dan yanzu ta fi zaman gidanta, to wannan satin ma ba komawa zata yi ba, har sai ta nemeta da kanta.

Yayin da Sumayya ta ce "Ai yanzu kin tabbatar zaki samu burin ranki dole ki tattaro dukkan iyashege ki dawo da shi".

Ai kuwa Sa'aadah ta fasa uban ihun kuka. dai dai lokacin Baffah ya shigo, ya dinga tambayar ba'asin kukan da take yi mai daukar hankali.

Ai kuwa ta fito cikin kuka ta ce "Baffah shata mini layi da Maman Khalifa, ta takura ni, ta matsa mini, saboda ta san duk abin da ta yi mini Inna ba zata ce ta yi laifi ba".

Ya murmusa ya ce "Uwata an taba shiga tsakanin hanta da jini ne, inace da dukkan uku hade mini kai kuka yi.
Yanzu kuma sai kice na shata miki kayi da ita? Ni bana haka, ya kalli Sumayya ya ce ke kuma ki ri'ke girmanki ai dai yanzu kin wuce kisa ta kuka irin haka".


Murmushi sosai Sumayya ta yi, cikin sanyin muryarta ta ce "Baffa daga na ce bai kamata ta je dubiya da kwalliyar da ta yi bane shikenan fa laifin nawa, kuma gani na yi tunda ba zance zata je ba, dubiya ne ai sai ta rage zumudi".

Dariya ta kwace wa Baffah ya shige dakinsa. Ba tare da ya yi magana ba.

Yayin da Sa'adah ta cigaba da kuka sosai, har Zainab ta gaji ta shigo gidan a fusace.

Ganin kukan da take yi, ya tayar mata da hankali ta yi zaton ko Mk ya amsa Kiran mahallicinsa ne.

Amma da ta ji ba'asin kukan sai itama ta hau dariya har tana fadin "Yo dama Ni nasan ba wani bata sonsa, idan akwai abin da na gasgata a duniyata, to kuwa son da take yiwa Uncle na cikin su".

Ai kuwa ta mi'ke a fusace ta ce "Wallahi Zainab har yau din nan ina jin karfi a tare da ni, ya ishe ki".

Zainab ta watsa mata harara ta ce "Da shekarun nan naki, da ilimin lauyancin na ki, da Jawad duk basu sa kin ji cewar kin girma ba? Amma kuwa dai kin ji kunya, kuma na gasgata Anty Sumayya lallai murnar zaki komawa muradin zuciyarki yasa ki wannan fallin, gara ma ki 'dore da kyawawan dabi'un da Kika dauka a shekaru bakwai din nan domin dai kin san yanzu ke Uwargidace kina da amarya mai tsananin wayo da kissa".

Ba'kin cikin maganar Zainab ya sake sawa ta fashe da sabon kuka tana fa'din " Asibitin ma ba zani ba".

Baffah ya fito ya dubi Zainab ya ce "Ni na fi ku fahimtar Iyah tuni Mutari ya fita a ranta, biyayya kawai zata mini, zuwa duba shi ma ai dole na yi mata, ta kuma yarda zata mini biyayya, dan haka ku daina cewa tana sonsa, ko dan shi ta yi kwalliya domin kuwa dukkan mu shaida ne akan Iyah dangin Dawisu ce".

Jin hakan ya sa ta yi shiru.

Yayin da Zainab ta ce "To Baffa ka fa'da mata a biyayyar da zata yi maka ta hada har da sanin ta girma, kar ta koma ta zama ta bizaro a gidan Uncle domin yanzu ba ita ka'dai bace, tana da kishiya mai fi'ilin tsiya".

Baffah ya murmusa ya ce "ke kam Zainab sai a gaishe ki, dukkan mace ai da inda take da tasiri, Ni kuwa na san ko mata uku ne da Mutari ban jin Iyah zata kasa samun kansa, ai duk wannan shagwabar da take yi na gata ne".


Daga haka ya fice ya na fadin "lallai ki fito ku je dubiyar nan Iyah, kinga ba lalle Zainab ta sake samun sukunin fitowa a gobe ba".

Ta fito cikin bakar doguwar riga mai kyau. Tana rataye da Yar karamar jaka, kafarta sanye da flat din talkalmi wadda mahadin jakar ne, powder ce kawai a fuskarta.

Zainab ta mike ta na cewa "Inna sai mun dawo".


Har suka isa asibitin Sa'adah bata ce kala ba, duk da Zainab na janta da hira.

A wajen asibitin Zainab ta samu jikin bishiya ta yi fakin. Suka fito suka taka ciki da kafafuwansu.

Da Abbas suka fara yin tozali, yana zaman jiran Farida ta fito ya mayar da ita gida, dan haka ya mike ya musu jagora har dakin da Mk yake kwance.

A zaune suka taradda shi, Farida tana tsaye a gabansa hanunta na dama ri'ke da hannunsa, yayin da hannun na hagu ri'ke da kwandon zuba abinci, alamun tafiya zata yi.

Zuciyar Sa'a ta buga da tsananin gaske, ta zabura, zata koma da baya, Zainab da Abbas kawai suka lura da hakan, Dan haka cikin hikima Zaynab ta ru'ko hannun ta da karfin gaske, kan dole suka karasa shiga sosai.

Zainab suka gaisa da Farida ta tambayi mai jiki, sannan ta gaida Mk da ya yi mutuwar zaune, saboda yadda ya ji wani abu da bai san menene ba ya dirar masa, gashi dama fama yake da rashin karfin jiki.





Surayya Dee
โœ๏ธโœ๏ธ.


๐ŸŒบ *HALIN YAU*! ๐ŸŒบ

*NA*

*SURAYYA DAHIRU*.


*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ยฎ_* โœ๏ธ
โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ษ—amfare da bin ฦ™a'idar Adabin Hausa.```

```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` โœ๏ธโœ๏ธโœ๏ธ
____________(โœช)______________

https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/



*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*



*GAISUWAR GIRMA GA*
*HAJ SALIHA A.A. ZARIA.*
*MARUBUCIYAR BEGE*
*ALLAH YA KARA MIKI LAFIYA DA NISAN KWANA MAI ALBARKA*.

104-106.


Farida na ri'ke da hannun Mk, ta kalli Sa'a da murmushi ta ce "Maraba da Gogel, karaso kusa mana".

Takaici a zuciyar Sa'adah tamkar ta rushe da kuka, ta ki sakar masa hannu dan ta nuna mata itace matarsa. Sannan dan ta tabbatar mata ita bakuwa ce yanzu a wurin Mk, shine take mata iso a gabansa?

Ta daure ta hadiye damuwarta ta yi kamar bata ga hannuwansu a sarke ba, ta cewa Farida "Sannun ki".

Daga inda take tsaye ta kalli Mk ta ce "ya ya jikin?"

Daga haka ta tsuke bakinta, tana karanta duk addu'ar da ta zo bakinta, tabbas Mk ne ya wula'kanta ta saboda ya nunawa Farida ita ba wata tsiyar ba ce. Shiyasa ya ki zame hannunsa da yake cikin nata.
Amma ai ya yi da yar halak.

A hankali Mk yake kallonta ta kasan ido, yana nazartar yadda take kokawa da fishin da ya ke yun'kuro mata.

Cikin hikima ya zare hannunsa a hannun Farida, gumi sai yanko masa yake yi.

Da sauri Farida ta 'kara karfin A.C da gudun fanka, saboda zufar da taga na karyo masa wadda kawai ta fargaba ce. A ransa ya dinga nazarin anya zai iya jarumtar ri'ke mata biyu kuwa? Saboda yadda ya dinga zullimin kasancewarsa a gabansu a lokaci 'daya.

Mk na wanna tsinkayen ya ga Farida ta ajiye kwandon hannunta tabbacin ta fasa tafiyar kenan.
Wato duk ha'kurin mace ta iya shu'umanci indai akan kishi ne?
Yau ya gasgata hakan domin ko kaffara ba zai yi ba, idan ya yi rantsuwar saboda Sa'adah ta 'ki tafiyar.

Dan haka ya yi kicin kicin da fuska, ita kuma sai kokarin yi masa fifta take yi.

Yayin da Sa'adah da Zainab suke ganin ikon ubangiji na yadda Farida ta kankane komai, Zainab da Mk ne suke mamakinta. Yayin da Iyah ta san dama Farida zata yi abin da ya fi haka.

Abbas ne ya leko daga bakin kofar ya ce "Farida ina ta faman jiran ki, so nake na yi maza na kai ki na dawo, kafin su tafi kar abar shi ba kowa, Hajiya ta tafi tun dazu, zan biya na dauko su Anty Amina Kuma".

Ai kuwa ta ce "je ka dauko su kawai, idan Akil ko Ahamad sun zo, sai je su dauko mini motata, ko kuma na fita na hau adaidaita sahu".

Abbas ya yi sakare yana mamakinta a ransa tare da cewa "Ah adole ita ba zata basu damar ganawa ba, duk da dai bata nuna bacin rai ko damuwa ba.

Sai a lokacin Mk ya ce" amma kin san ban son Ahamad yana hawa motar ki saboda ba ya tuki da nutsuwa, Akil kuma yana shago sai dare ya fara jah yake zuwa".

Ta marairaice ta ce "Ba damuwa sai na hau adaidaita sahu".

"A a bana so kin sani, bana so".
Ya sake sassautawa "ya ce ki je ya kai ki, ana idar da Sallar isha ki rufe gidan, sannan ki taimake ni ki sha maganin ki please".
Ya fa'da cikin sigar rarrashi da kulawa.

Amma ta yi mirisisi ta ki tafiya, lamarin da ya sake dagula lissafin Sa'adah, wai yau a gabanta wata macen take nunawa ta fita son Mk, ta fita kusa da shi.
A gabanta shima ya ke nunawa wata macen tattali da kulawa? Wannan shine duniya rawar yanmata.
Shirun da Farida ta yi ya tabbatarwa da Mk bata amince bane, ya kalleta a tausashe ya ce "Ban son ki wuce lokacin shan maganin ki ne, gobe idan zaki taho, ki taho da shi, sai ki yi ta zamanki, amma yanzu taimake ni ki je ki kular mini da lafiyar ki".

Nan ma ta yi shiru, Mk ya ce "shikenan ai, tunda so kike mu kwanta gaba'daya".

Dakin ya yi shiru na mintina uku, Zainab na mamakin irin wannan al'amarin, ta kasa cewa komai duk da bakinta cike
yake da tarin maganganu, da suke bu'katar fashin ba'ki.

Irin kallon da Farida take yiwa Mk da idanuwanta masu maiko ya sa
nan da nan zuciyar Sa'a ta hauro, ta kalli Abbas dake bakin kofa yana tsayawur jiran Farida, amma ganin Sa'adah yasa ta fasa tafiyar dan kar ta samu damar 'dagawa mijinta hankali ๐Ÿ˜€

Ta ce "Uncle Abbas"

"Na'am Anty Sa'adahtu".

"Tafiya zan yi, kuma akwai sakon da zan fa'da masa, zo ka ri'ke mini shi zuwa waje na mintina kadan".

Da sauri Abbas ya shigo yana cewa "daga nan ma na zagaya da shi, dazun nan likita ya gama ce mini kwanciyar ta yi yawa, ya dinga yin atisaye ko a cikin dakin nan ne".

Ya isa jikin gadon ya mikawa Mk hannun, ya dago shi.

Ya sunkuya ya janyo masa takalma a a kasan gadon ya saka sannan ya mikar da shi, suka fita a hankali.

Zainab ta dinga jin wani irin farin-cikin iyakar da Sa'a ta nunawa Farida.

Sun Jima da fita sannan Sa'adah ta dauki handbag dinta zata bisu, Farida ta ce "Gogel ko zaki fitar masa da kujera, jikin nasa ba kwari har yanzu".

Da sauri Sa'adah ta saki murfin kofar, ta dawo ta zuba mata ido, sai kuma ta sassauta fishinta tace "Da a ce Sa'adatu Kika kira ni da shi, da ko kula ki ba zan yi ba, sai dai na ce miki to, ko da ba zan yi abinda kika ce din ba, sai dan na nuna miki am matured now. Amma tunda Kika 'Kira ni da Gogel zan tabbatar miki har yanzu waccan Gogel din ce dai da kika sani, Billahillazi ki fita a idona, kada ki sake yun'kurin shiga tsakani na da shi, ko ki nuna mini ga yadda zan yi masa, if not kin dai sani. Ba zai zamewa Iyah Basiru komai ba wajen nuna miki har yanzu ina cikin shekarun da ba a mini kan kara ban yi na ice ba".

Daga haka ta juya tana cewa "Zainab zo muje, idan na gama sai mu wuce ba sai na dawo nan ba".

Suka fita bayan Zainab ta cewa Farida Allah ya Kara lafiya.

Sun zo inda su Mk suke zaune, Zainab ta yi masa addu'ar samun lafiya mai dorewa ta yi gaba, haka Abbas ma ya mike suka basu wuri.

Sa'a ta zauna tamkar gaske magana zata yi masa, amma ban da cika tana batsewa ba abin da take yi.

Ta tabbatar Farida na hango su ta windo, shiyasa ma da ta zata zauna sai ta juya baya ta yadda ba zata ga fuskarta, ba haka ma Mk bayansa zata hango.

Banda son ta nunawa Farida dan taki tafiya ba shine dalilin da zata hanata magana da shi ba, da bata tsaya kula Mk ba, tunda agabanta yake nunawa Farida soyayya har ya na lallaba ta.

Dukkansu kowa fishi yake da dan'uwansa, domin ganin ta da ya yi da Khalil ba karamin kidima shi yake yi ba, dan haka, ya danne zuciyar sa ya ki mata magana.
Amma dai a kasan ransa sun bashi dariya ita da Farida kwarai da gaske.

Mintina ashirin na cika ta tashi ga mamakin Mk ya ga ta mi'ke tana murmushi ta fito da wayarta ta Kira Zainab tana fa'din idan Abbas na kusa ki ce masa ya zo mun gama".

Aikuwa sai da Abbas ya zo, ta tafi bata ce da shi uffan ba, sai Abbas ta yiwa sallamah da fatan samun lafiya ga marar lafiya. Mk ya bita da ido yana ganin yadda take tafiya, sai ayyanawa yake yi ko sai yaushe zata daina rikicin gan-gan?

Ban da karfin halin Sa'a ya zata zo ta tarar da mace da mijinta, sannan ta ce sai ya fito waje sun yi magana alhalin ba maganar zata yi ba, kawai son rikici ne da son nunawa Farida karfin da take da shi a zuciyar sa.

A mota Zainab ta ce "Tabdi yau na ga kishi, ashe haka abin yake?"

Sa'a da dama kiris take jira sai kawai ta fashe da kuka.

Jikin Zainab ya yi sanyi sai kuma ta ce "Menene abin kukan kuma? Duk irin jarumtar da Kika yi".

Ta kasa magana illah kukan da ya ki yankewa, tana ta hararo hannun Mk a cikin na wata a gabanta kuma, tabbas har ta mutu ba zata daina kokawa ba.

Da kyar Zainab ta shawo kanta, "kin samu labarin auren Halima next week?"

Murya a dakushe ta ce " a a"

Zainab ta ce "to ai ke ce kinki shiga cikin group din mu na old girls a WhatsApp".

A sanyaye sosai ta ce "Bar ni kin ji, inace ga abin da biyewa 'kawayen ya janyo mini, kina kallon yadda wai magana da Malam ya zama sai an mini iyaka. Ta rushe da kukan da ya sanyaya jikin Zainab, itama idonta ya ciko ta kasa ce mata komai, tana tuki tana taya Sa'adah kuka.

Da kyar Zainab ta shanye kukan ta ce "Ai Halima tana cikin bala'i ke har Safinan ma, domin dai saurayin Halima ya ki aurenta ne adalilin wastewarsu suke yi. Dake akwai alaka tsakanin su da gidan iyayen saurayin shine aka masta masa amma ko kadan babu kwanciyar hankali a tare da ita.

"Ita Kuma Safina har yau dai bata karbi result dinta ba, kiga dai a bayansu da shekaru masu yawa kika shiga makarantar amma kin kammala kin barta".
Aure kuwa shiru kake ji sai dai ana nan ana addu'a. Komai lokaci ne. Amma su kam hakkin kashe aure ne ya saka suka kasa samun nasu auren".

Cikin kuka sosai Sa'a ta ce "Tabbas su Halima sun yi wa rayuwa ta illah, Amma kuma ai da gudunmawata, yarda na yi da su, sannan nima ina da tawa matsalar, bayan wadda suka cusa min, kawai iza mini wutar suke yi, Amma ni na hura abata.
Dan haka na yafe musu, amma bana fatan mua'amala ta sake hadamu, rabona da su tun ina gidan Malam, in sha Allah kuma rabuwarmu kenan domin tarayya da su halaka ce, na rufe babinsu har abada, dan haka kema daina yi mini maganar su".

Zainab ta dinga lallashin Sa'adah da maganganu masu taushi, tana nuna mata, ta yawaita addu'ar sau'kin kishi, itama zata taya ta, sannan yadda ta yi maganar a fita mata da shi waje suyi magana a gadarance, amma ya tashi duk da baya jin da'di ya isa ta gane har gobe ita ke jan ragamar zuciyar sa, sai dai dole ya yiwa Farida adalci domin matarsa ce, dole kuma zai sota.

Zainab ta nisa ta ce "Dan Allah Sa'adah ki 'dore da kyawawan dabi'un ki, kar ki bari kishi ya mayar da ke 'yar gidan jiya, kin san dai yanzu ba ke ka'dai bace, kuma Wallahi duk son da namiji yake yiwa mace indai ta cika kishi da korafi, fita fit take yi a zuciyarsa.
Ke ce uwargida tunda baki yi wani auren ba, dole ki 'dauki hakuri mai yawa. Ki koyi hakuri da juriya, duk yadda kike da mutum kar kiyi zancen abokiyar zamanki da ita mussaman dangin miji, domin duk ranar da abu ya ha'do ku

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login