Showing 54001 words to 57000 words out of 186291 words

Chapter 19 - Halin Yau By Surayyah Dee

18 Dec 2025

9727

ya kare. A lokacin sarkar gold din dubu hamsin babba ce, ita ya siyawa amarya da shawarar Sumayya da take ta 'koda irin kokarin da MK da iyayensa suka yi. Sai kuma 'dinkunan da ya mata na kwalliyar amarci.

A Daren da aka daura aure suna zaune a gabansa ita da Sumayya da mahaifiyarsu, bayan ya yi addu'a ya ce, "Duk wani burina a yau ya cika Iyah, ina kyauta zaton na dan'ka ki a hannu na gari don Allah ki bi mijinki, nasan kinsan idan mijinki, ya yarda da ke to Ubangijinki ma ya yarda da ke, idan kika ri'ke wannan kadai za ki gane komai za ki yi a 'dakin mijinki ibada ne.
Ibada kuwa sai an daure domin za ka ci karo da abin da kake so da wanda ba ka so. Na ro'ki ki yi koyi da yar uwarki wurin boye sirrin aurenta, har yau din nan Sumayya ba ta taba fa'din ga laifin mijinta ba, mun sani ba fa don ba ya mata laifin ba ne, haka shi ma yana ri'ke da ita cikin ha'kuri da girmamawa. Ina sake miki nasiha ki zama mai ha'kuri, baki da'yan aure wallahi hakuri ne ya fi yawa, ina fatan ki yi ko yi da mahaifiyarki wurin ha'kuri da biyayyar aure!"

Ya janyo ledar dake gabansa ya fito da sallaya da kur'ani ya mi'ka mata, ta miko dukkan hannunta biyu da suka sha adon lalle ta kar'ba, yace "Ki rike ibada da kyau ita ce za ta jagorance ki duniya da lahira."
Ya kalli Sumayya yana fadin "Ina abin da nace ki ajiye?"

Da sauri ta mi'ka masa dama ta shigo da shi ya karba ya sake mika wa Sa'adah yana fadin, "Ki rike tsabta da kwalliya da ma ba na jin ki a wannan bangaren. Inda nake da shakku akan biyu ne. ki 'karanta buri Iyah kin dai san ni ubanki ba kowa ba ne, ki yi alfahari da abin da yake hannunki, ki daina sha'awar wanda suka fi ki ko kuma wanda ba tsarin tarbiyarku daya ba, a yanzu da za ki koma 'karkashin mijinki, ina hada ki da Allah kar ki dinga dora masa hidimar da ba zai iya ba, ko ba ra'ayinsa bane. Da ace za ki rabu da harkar kawaye to ina tabbatar miki za ki 'karantawa kan ki buri saboda ba kya hangensu. A karshen karshe na yafe miki dukkan kurakuran da kika mini, ina fatan Allah Ya lullube rayuwarki da albarkaSa, ya ba ki zuri'a mai albarka, ya kuma hore miki ha'kurin zaman aure."

Daki ya yi shiru sai shesshekar kukan Sa'adah, Baffa ya nemi Inna ta ce wani abu, ta girgiza kai tare da cewa, "Duk abin da zan fada na dade ina mata bita indai mai ji ce ai ta haddace su. Fatana Allah Ya albarka ci aurenta."

Cikin soyayya mai yawa Baffa ya kalli Sumayya ya ce, "Saura ke babbar yaya uwa ta biyu!" Ta yi murmushi cikin sanyin murya ta ce, "Komai kun fada Baffa, fatana a ce duk ta ji ku da kunnen basira, ta kuma ri'ke 'yan'uwansa da girma, musamman iyayensa. Ki rike su da mutuntawa komai za su miki kar ki nuna kin ji haushi ki yi hakuri, ki sake ninka kulawarki a kansu, duk kuma wanda ya je gidan, ki karbe shi da sakakkiyar fuska su ji tamkar a gidan yar'uwarsu mace su ke saboda sakewa da walwala."

Baffah ya nisa yace " idan Kika bi maganganun mu kin tsira! Idan kuwa kika je kika biyewa 'kawayen banza da son zuciya ki tabbatar ke 'kadai za ki dauki 'bacin ran da zai same ki, ki bi mijinki ko zaluntarki yake yi ki bishi da addu'a idan abin ya gagara, sai mu shiga, amma idan ke Kika bijire to fa kisani baki da wurin zama a gidannan".

Ya rufe zaman da doguwar addu'a ya kuma rike ta a hannunsa ya tafi kai ta 'dakinta da kansa a motar Alhaji Isa da ya zo daukar Amarya.

'Yan'uwan Baffa da na Inna da suka zo, sai mamakinsa suke yi da ya hana su zuwa kai amarya, ya tafi da kansa ya kai 'yarsa dakinta.

A lokacin kam ya zo da sabuwar dabi'ar da ta sha banban da al'ada, ashe shi yasa yasa aka kai su suka ga gidan amarya tun jiya?






*SURAYYA DAHIRU*.
✍️✍️


🌺 *HALIN YAU*! 🌺




•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```

```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________

https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•


*_Dokɑr hɑkkin mɑllɑkɑ me lɑmbɑ tɑ 68, tɑ nunɑ cewɑ sɑtɑr fɑsɑhɑ bɑbbɑn lɑifi ne dɑ yɑke dɑidɑi dɑ sɑtɑr dukiyɑ._*


*A guji taba ko sarrafa labarin nan ba tare da izinin mai Hakkin mallaka ba.*



*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*



*TUKUICI GA*
_*AISHA IBRAHIM BAFARAWA*_
(*BEAUTY*)
*MK DA SA'ADAH NA GAISUWA*
👍




49-50.




*GIDAN AMARYA*


A gidan su Baffa suka tarar da su Baba Umaru da Baba Idi da kuma MK. Tunda Baffa ya fa'da musu a wurin 'daurin aure cewar shi zai kai amarya 'dakinta kar a turo mata, sai suka fasa komawa Bichi a yau, suka ce su za su karbi amarya da kansu.

Haka Baba Umaru ya tisa MK da jan kunne iri-iri akan ya ji tsoron Allah ya ri'ke matarsa cikin tausayi da adalci, komai za ta yi ya dauke kai ya fahimtar da ita cikin ruwan sanyi.

Baba Idi ya nisa ya ce, "Sannan zan fa'da maka gida naka ne, amma kayan ciki na matarka ne, kana dai ganin irin mutunci da karamcin da aka maka, to ina ro'konka! ka nuna kai ma ka san mutunci ta hanyar zama da yarinyar nan da kyautatawa, ba hankalinku 'daya ba, mata lamarinsu yana da gigitarwa.
Amma idan aka yi ha'kuri da su, aka musu afuwa sai a ji dadin zama da su, saboda masu rauni ne, kuma masu tausayi ne".

Alh Isa kuwa cewa ya yi, "Abin da zan fada muku ni ne uban Mukhtar, ni ne uban Sa'adatu, sannan ni ne alkalinku dukkanku 'daya kuke a gurina. Ba zan saurara wa duk wadda ba shi da gaskiya ba".

Ya kalli Sa'adah da take gurfane a lullu'be cikin lafaya, "Sa'adatu duk da ba na fatan matsala, amma duk abin da ya taso na rashin jin dadi, ni ne Babanki, ni za ki fadawa kar ki ji nauyi ko kunya, waya kawai za ki mini, ni kuma zan miki maganin ko mene ne, domin duk girman Mukhtar yaro ne karami a idonmu, na san kuma mun isa da shi".

Baffa dai bai ce komai ba, da'di ya cika zuciyarsa, Allah Ya kai Iyarsa cikin ahalin da suka san mutunci suke kuma rama shi da alheri.

Bai ce komai ba sai da suka mike, ya kalli Mukhtar ya ce, "Ban baka aure ba sai da na tabbatar kana da nagarta, ina kuma zaton kai din adali ne saboda ka siffantu da kyawawan dabi'u don haka ni ba na shakku a kanka. Sai dai kar ka bari jan kunnen da ake ta faman yi maka na ka kyautata mata, ya yi dalilin da za ka bari ta yi abin da ta ga dama, ka bude kunne ka ji ni sosai. Duk 'kawa ko makwabciyar da ka ga dabi'arta ba ta yi maka ba, ka shata wa matarka layin mu'amala da ita, idan ka bari ta fi karfinka to kai ne za ka sha wahalarta".

Su Baba umaru suka hada Baki wurin cewa, "Ba ma za ta bijire masa ba, ai barewa ba za ta yi gudu d'anta ya yi rarrafe ba, In sha Allah, irin halin gidansu na girma za ta yi ba *HALIN YAU* ba".

Aka rufe maganar da doguwar addu'ar zaman lafiya da neman tsari daga sharrin shaidan, da shaidanun mutane. Suka tafi MK ya bisu a baya, yana ta musu godiya tare da fadin duk abin da suka fada zai kiyaye, bai juyo ba sai da motarsu ta bace wa ganinsa. Sannan ya bi bayansu zuwa bakin titi ya karbo gasassun kajin da tun yamma Mahmoud ya yi masa booking, ya hado da yougurt din L & Z da kuma lemon 5alive, yana tafe yana ayyana bai taba ganin nisan bakin titi zuwa gidan nasa ba sai yau. yana isa ya rufe gidan.

Kamar a guje ya fada falon! ya tarar da ita zaune a inda suka bar ta, tana rufe ruf cikin lafaya.

Gefe daya ya ajiye ledojin hannunsa, ya isa kusa da ita ya tsaya, a zuciyarsa yake ta fadin Alhamdulillah! sannan ya sunkuya ya 'dago ta tare da fadin , "Assalamu alaiki! Barka da zuwa gidanki, ina miki murnar wannan rana mai cike da farinciki".

Ta yi shiru, ta kasa amsawa saboda yadda zuciyarta, take a cunkushe da alhinin barin gida.

Ya ri'ke hannun ta yana janta zuwa cikin 'dakin da shi ne mallakinta, a bakin gadon ya zaunar da ita tare da fadin, "Haka na ga ana yiwa amare." Yana warware mata laffayar zuwa kafadarta, fuskar ta masa kyau duk da ta kode saboda kukan da ta ke yi. Kusa da ita ya zauna sosai har jikinsu na gogayya da juna ya dan ri'ko ta ya ce, "Kukan na mene ne tamkar ba gidanki za a kawo ki ba, ke da kika yi sa'a a gari za ki zauna duk lokacin da kika so zuwa gida, zuwa za ki yi to menene abin kuka sai ka ce ba gidana kika dawo ba".


Tissue ya dauko a kan madubi ya shiga goge mata fuska, yana ta fadin maganganu masu taushi.

Ya kalli agogo ya ga tara saura,ya mi'ke ya dauko ledar kajin da ya bar su a falo, sai da ya shimfida musu abin zama sannan ya janyo ta ta sau'ko 'kasa, ya bude ledar ya tura mata gabanta yana cewa, "Nasan tun safe ba komai a cikinki. Taimake ni ki ci"
Ya zabura ya nufi kicin ya samo 'yar roba ya wanke hannu sannan ya zubo ruwa a ciki ya dawo, da rarrashi da hikima ya sa ta cin kazar nan, har ta manta ita ba'kuwa ce, dama kuma azabar yunwa ce a cikinta. ya sake lallabawa ya tura mata yougurt, sai da ya ga ta nutsu sosai sannan ya kalle ta ya ce, "Ga toilet nan ki shiga ki yo brush ki dauro alwala"
Ya mike yana fa'din ni ma bari na yi alwalar.

'Kirjinta ya buga fargaba ta kama ta yau gata a daren farko da ta ke karantawa a cikin littafai ko ya ya nata daren zai kasance?

Har ya dawo tana zaune a inda take.

"Kin yi alwalar kuwa?"

Shiru ta masa ya tabbatar ba ta yi ba sai ya ce, 'Tashi mana!" Ya sa hannu ya 'dago ta, sai da ya raka ta har kofar bayin da ke cikin dakin sannan ya dawo yana tattare kayan da suka yi amfani da su, ya shimfi'da musu sallaya ya koma gefen gadon ya kishingi'da yana jin matsanancin bege na ratsa shi.

A bandakin ta tarar da sabon brush da makilin, sai da ta wanke bakin sannan ta 'dora alwalar sai kuma ta tsaya a bakin 'kofar ta kasa fita. Wata irin fargaba ce ke haniniya da ita.

MK da ya ga shirun ya yi yawa, sai ya tashi ya tura kofar ganin ta a tsaye, yasa shi yin turus, bai ce komai ba ya ru'ko hannunta yana fadin, "Ba na son ba'kon yanayin nan da nake gani tare da ke a yau".

Laffayar ya mi'ka mata ta fara kokarin na'de jikinta, ya kalle ta ya ce, "kin ga ba sai kin yi wannan na'din ba, kawai ninka ki yafa".

Ba ta musa ba saboda yadda bakinta da jikinta suka yi mata nauyi ainun.

Ya ja su, suka yi sallar da Annabi ya kwa'daitar da sabbin ma'aurata su yi. Bayan sun idar ya ri'ke goshin ya yi addu'a sosai, tana amsawa da amin a cikin zuciyarta. Suna shafa adduar ya mike ya fita! bai jima ba ya dawo bayan ya rufe 'kofar falon tare da kashe fitila da fanka, kasancewar farkon damina ne yanayin zafi ne.

Yana shiga ta kalle shi da gefen idonta saboda yadda kamshin sa ya sake cika dakin da hancinta, ta ga ya sauya kayan jikinsa zuwa farar jallabiya sabuwa 'kal. Hannusa ri'ke da wasu kayan, kai tsaye ya isa kusa da ita ya m'ikar da ita ya cire mayafin ya wurgar da shi, ya zame dan'kwalinta!dogon gashinta da ya sha gyara na musamman ya bayyana, ya kasa cigaba da dauriya ya fizgo ta jikinsa ya sa hannunsa biyu ya rungume ta sosai tamkar zai mayar da su halitta guda.

Ba ita ba, shi kansa jikinsa 'bari ya ke yi, 'kamshin man gashinta da na jikinta da kuma nasa kamshin suka hadu guri 'daya suka sake rikita shi, hannunsa sai kai komo ya ke yi a bayanta cikin wani irin shau'ki mai rikitarwa.

Ta yi luf a 'kirjinsa jikinta sai 'bari ya ke yana sake rikicewa da sa'kon da ya ke kar'ba.

A kunne ya ke rada mata "please hold me Sa'adah, sa hannu ki ri'ke ni don Allah!"
Cikin wata irin murya da ba ta san shi da ita ba yake ro'kon.
Kunya da tsoro suka sa ta kasa koda 'kwak'kwaran motsi balle ta iya masa abin da ya ke ro'ko.

Da 'kyar ta samu ta zame daga jikinsa ta koma bakin gado ta zauna kunyar duniya ta rufe ta.

Murya a da'kushe sosai yace, "Ga rigar barci tashi ki saka".

Kai ta sunkuyar 'kasa tana kallon 'yar guntuwar rigar da ba ta da maraba da abin tatar koko, ta ya ya za ta iya sanya wannan rigar, ko a ina ya samo ta?

Ganin ba ta da niyyan tashi ya matsa kusa da ita ya 'dora mata akan cinyarta tare da fadin, "Tashi ki saka don Allah"
Ta 'daga taga lalacewar riga ta wuce ma yadda ta ke tunani, da sauri ta ajiye ta tana fadin "Ni ba zan iya sawa ba, ba na son ta".

"Ni ina so! kin san tun yaushe na siya miki na ajiye? Kullum addu'a nake Allah ya kawo mini ranar da zan gan ki a cikin ta.

Ta shagwabe fuska ta 'daga rigar da sauri ta mayar ta ajiye, ita rigar ma kawai kunyata take yi, balle kuma a ce ta saka, kanta a kasa ta ce "Ka yi hakuri ni ba zan iya sawa ba".

Nan da nan ya ci laya, "Wallahi sai kin saka na gani".

Ya fada a dake! gabanta ya yanke ya fa'di ta shiga bubbuga 'kafa, tana 'kananun kukan da babu hawaye, hakan da ta yi ya sake 'kawata masa ita, ya sake matsawa kusa da ita sosai, ya yi 'kasa da muryarsa ya ce, "Rufe idon ki ni sai na sa miki da kaina".

"Ni dai ka yi hakuri ka bari".

"Amma kin ji na rantse, so kike tun yanzu ki fara 'ba ta mini rai, ki fara kwasar zunubi?"

Kai ta girgiza, ya ce, "To ki bar ni na yi abin da nake so, tun yaushe nake ha'kurin ki zama halaliya ta".

Ya fara zuge zip din rigarta ta ri'ke da sauri, tana fadin "Ka kashe fitila to".

"Idan na kashe fitila me zan gani?"

Ta yi shiru tana jin tamkar kasa ta tsage ta shige. Ta kasa kallon sa a raunane ta ce, "Ka juya to, ya yi murmushi ya ce, "To" Ya juya mata baya.

Kan dole ta sanya rigar amma ta kasa cire kayan ciki! Ta kuma lullube jikin da mayafi.

Jin ta daina kiciniyar sanyawa ya sa shi cewa "Na juyo?" Jin ta yi shiru ya sa ya juyo gabadaya, sai dai ganin ta a lullu'be kuma a takure ya sa shi fa'din "mene ne haka kuma?"

Ya isa ya mikar da ita tsaye ya fara janye mayafin, ita kuma ta 'kan'kame 'kirjinta da dukka hannun ta biyu. Ya juya ta bayanta ya ga yadda rigar ta kama ta, shape din surarta ya fito sosai. Da 'kadan ta rufe mazaunanta 'yar guntuwa ce sosai, mai kuma kama jiki, rashin kirkin rigar ya kai 'kurewa.

Tsayawa kawai ya yi yana kallon ta yana fadin "Ma Sha Allah kin yi mini fiye da yadda nake so".

Jin yana 'kokarin 'daga rigar sama sai ta yi maza ta saki 'kirjin ta ruko kasan hakan ya ba shi damar juyo wa ya kalli 'kirjin ta. bai ce komai ba kawai ya ci gaba da tasbihi, ya jawo ta ya rungume ta sosai fiye da rungumar farko.

A haka ya dangana su da gado, ya sa hannu ya kashe fitila, hasken bandaki ya ragewa dakin duhu, ya cire rigar da ragowan kayan ya wurgar.

Sannu-sannu ya bi da ita, duk wata ga'ba da 'kofa ta jikinta ba inda bai sa baki ya lashe ba, ya rikita mata jiki sosai! nishin da yake yi ya sake jefa ta cikin tsananin shauki da za'kuwa. A ranta kuma ayyana rashin 'kyankyami irin na MK take yi, inda ba ta yi zaton ana sa baki ba, shi yasa harshe yana lasa bai kuma tofar a 'kasa ba.

Sai da tafiya ta fara nisa ta gane al'amarin ba mai sauki ba ne, bai 'kyale ta ba sai da ya mayar da ita cikakkiyar mace.

Dukkansu sun galaibaita, saboda a tare suka bude junansu a leda. Sai da nutsuwa ta zo wa MK ya rungume ta tare da shafa kanta yana fadin maganganu masu nuna 'kololuwar soyayya da yabawar yadda ta kame kanta, kamar yadda shi ma ya kame. Wani irin son junansu ya cika zuciyarsu da gangar jikin su gaba'daya.

A tsakiyar Daren ya fita kicin ya dauko buta ya jona musu ruwa, shi ya fara shiga, kafin ya fito nata ya tafasa, ya kai mata ban'dakin ya taimaka mata ta sauko da ga gadon sai da ya ga ta shiga toilet din sannan ya ye zanin gadon saboda yadda suka bata shi, idan ya bushe jirwaye zai yi,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login