Showing 39001 words to 42000 words out of 186291 words
ne dɑ yɑke dɑidɑi dɑ sɑtɑr dukiyɑ._*
*A guji taba ko sarrafa labarin nan, ba tare da iznin mai Hakkin mallaka ba*.
*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*.
*Fatan alheri ga*
*Asma'u Sani*
*Aisha Lagos*
*(Mrs Dan manya)*.
*Shafin na ku ne ku yi yadda kuke so da shi*.
38_39.
Haka ta ci gaba da kiran har ta gaji, tana 'kiyasta adadin kiran da ta yi masa ya kai ashirin, jikinta ya mutu tamkar marar laka, zuciyarta ta cunkushe da fargaba, tasan tana son MK sosai amma a yau ta sake sanin son da take masa marar adadi ne, duk da kasancewar ba lokacin zafi ba ne sosai, amma zufa sai karyo mata take yi. Waya kuma na hannunta, tana ci gaba da kiran sa.
Tunda ya bar gidansu Sa'adah Masallaci ya nufa da 'kyar ya karasa saboda yadda zuciyarsa ta daure, ba abin da yake bukata sai kadaici. Ya Jima a zaune yana ta ambaton Allah har ya sami sassauci sannan ya dauki Qur'ani ya fara karatu a fili, a hankali, duk kiran da Sa'adah ke yi masa yana gani, duk da a silent ya mayar da wayar.
Bai bar massalacin ba sai da aka yi Magariba zuwa wannan lokacin ya samu saukin daurewar da zuciyarsa ta yi a dalilin kishi, ya fito daga Massalacin ke nan kiran ta ya ci gaba da shigowa ba kakkautawa.
Gefe sosai ya samu ya zauna ya fito da wayar ya katse kiran nata sannan ya kira ta.
Jikinta har rawa yake yi wurin amsa kiran wanda ta dade ba ta ji zakuwa da dokin amsa kiran sa ba kamar a wannan lokaci.
Muryarsa ba amo sosai ya mata sallama tare da cewa, " Sorry Sa'adatu! Kin kira na bar wayar a caji ne tun dazu sai yanzu na ga tarin missed calls."
Wani nauyin jiki ya kara kama Sa'adah, ta rasa kalmar da za ta furta saboda abubuwa biyu, na farko bai nuna ta masa laifi ba tunda da ban ha'kuri ya bude maganarsa bugu da kari ma katse kiran ta ya yi, ya Kira ta.
Na biyu ya ambace ta da Sa'adatu rabon da ya kira ta da hakan tun lokacin suna yar tsama, ita kam ya binneta, ha'kuri za ta ba shi ko kawai sharewa za ta yi kamar yadda ya yi?
Da kyar ta bude baki ta ce "Ai na dauka kana sane ka 'ki amsawa."
Tana rufe baki ya ce
"Ko daya to mai kika mini?"
Ta san sarai a cikin fishi yake, don haka sai ta lankwashe harshe ta ce "Ka yi ha'kuri don Allah!"
Da sauri ya cafe da cewa
"Ni fa ba ki mini komai ba, laifina ne da na zo kai tsaye ban sanar da ke ba, sannan ai yaudarar kai ne na yi tsammanin ni kadai kike kulawa, ke allura ce a cikin ruwa don haka feel free you did nothing."
Ta kasa gane inda ya dosa shin gatse ya ke mata ko kuwa da gaske hakan yake nufi a zuciyarsa?
Don haka sai ta ce "To ka dawo na ganka dama ai na kwana biyu ban gan ka ba"
Kai tsaye ya ce, "Ai ba na zuwa zance da daddaare"
Shiru ta yi sannan ta ce "To gobe za ka zo?"
Tana rufe baki ya ce "Ina da schedules masu muhimmamanci a gobe."
Kawai sai ji ta yi kuka ya zo mata, cikin rawar murya ta ce "Har sun fi ni muhimmamanci?"
Cike da rashin kulawa ya furta "Wadancan tabbas ne, ke kuwa gaibu ce."
Ta yi shiru amma kuka take yi, yana jin yadda ta ke jan majina da shassheka, amma ya yi burus da ita, yana fatan ta ji a ranta cewar ita ba wata tsiya ba ce a gunsa.
Cikin kuka ta ce "Ni ka ke kwatantawa da gaibu?"
Ko dar bai ji ba wurin ba ta amsa da cewa, "E!" A gajar ce.
Bai sani ba ko kishin dake cin zuciyarsa ne, ya sa bai ji kukanta ya taba shi sosai ba.
Yayin da ita kuma bakin cikin yadda yake nuna mata rashin kulawa yake dada addabar ta.
Duk da hakan sai ta daure ta ce "Jibi Juma'ar za ka zo?"
"Zan zo idan ina cikin masu rai da lafiya idan kuma uzuri ya taso ban sami zuwa ba, to sai satin sama."
Ta yi shiru tana jin ta rabu da wannan mutumin da yake nuna mata ita ba komai ba ce a idonsa, sanin ya gan ta da wani ta san dole zai ji ba dadi yasa ta ajiye komai ta neme shi.
Har ha'kuri ta ba shi amma shi ya nuna ma ba laifi ba ne bai yi fishi ba, anya kuwa yana son ta, anya ba ita ke bankaura akansa ba?
Jin ta yi shiru ya sa ya magantu da cewa, "Sai yadda ta yiwu." Ya katse wayar! Bakin ciki ya kama ta sai kawai ta kife kai a kan filo tana kuka.
Shi kuma ya mike ya mayar da wayar aljihunsa, yana sake jin sau'kin radadin da zuciyarsa ke yi masa, tunda dai ya tabbatar ita ma ta shaki takaici.
Washegari tun safe Sa'adah ke zuba idon kiran MK har aka yi sallar Isha bai kira ba, a lokacin ha'kurinta ya gaza, ta dauko wayar Inna ta shiga kiran sa, sai da ta gama ringing bai dauka ba, tana shirin sake kira sai ga kiransa ya shigo. Ba ta tsaya jan aji ba ta dauka da sauri sai kuma ta yi shiru ta ki yin magana.
Sai da ya yi sallama har sau biyu sannan ta amsa ciki-ciki, mamakin ta ya kama shi amma ya waske ya ce, "Mura ki ke yi ne?"
Nan ma ta yi shiru ya nisa ya ce, "Yau yini guda ban zauna ba, ina ta yunkurin kiran ki, sai wani al'amarin ya mantar da ni.
Yanzu kuma na dauko wayar da nufin na kira sai kika riga ni, Ina fatan kin yini lafiya?"
Haushin sa ya kama ta sosai ta kasa tanka masa, amma tana raya cewa wai ya manta da jin muryarta.
Jin ta sake masa shiru sai ya kashe wayarsa.
Ita ma ta ajiye wayar daga kunnenta, tana gaskata zarginta na zaton MK da gaske ba son ta yake yi ba.
Kafin ta yi yunkurin yin wani abu kiransa ya sake shigowa ta yi kamar ba za ta dauka ba sai kuma zuciyarta ta kasa jarumta. Haka ta sa hannu ta amsa, ba tare da ta yi magana ba.
"Kina jina?"
Abin da ya furta ke nan, ta sake yin shiru! takaici ya kama shi cikin fa'da fa'da ya ce, "Kin san ba za ki yi magana da ni ba mene ne zai sa ki kira ni?"
Sai kawai ta saka masa kuka mai tsananin gaske irin mai cin rai! Ya yi shiru yana jin kukan nata wanda yake rasta dukkan sassan jikinsa musamman yadda take yi tana ajiyar zuciya.
Jikinsa ya yi sanyi sosai sannan kuma hankalinsa ya tashi, duk da ya san ma'abociyar kuka ce ita din, amma wannan ba na zallan shagwaba ba ne, da alamun damuwa sosai a cikin kukan.
Ya yi kasa da muryarsa sosai ya ce, "Me ya faru, fada mini mene ne yasa ki kuka haka?"
Jin ya karya murya yana tambayar ta sai wani kukan ya sake kwace mata sosai wanda ya tayar da hankalin MK sosai.
A gigice ya dinga fadin "Don Allah ki yi shiru ki fada mini me ya faru, kin tayar mini da hankali."
Ta kasa magana saboda kukan ya ci karfinta ita kanta so take yi ta daina amma ta kasa sai shesshka da ajiyar zuciya ta ke yi.
Ya yi shiru yana jinta, yana jin shi ma tamkar ya rushe da kukan ko ya sami sau'kin yadda zuciyarsa ke bugawa.
Ya lankwashe murya ya ce, "Sa'adah! so ki ke ni ma na yi kukan ne? Don Allah ki taimake ni ki yi shiru haka nan , ko so ki ke kanki ya yi miki ciwo?"
Cikin kukan ta ce, "Ka damu da ni ne da har kake gudar mini jinya?"
Ya ce, "Haba Sa'adah wacce irin magana ce wannan! Ai ni gani nake yi Baffa da Inna ne kawai suka fi ni damuwa da ke "
Ta yi fit ta ce "A hakan?"
Ya nisa sannan ya ce, "Ke matsala ta da ke ba ki fahimce ni ba, har yanzu kin kasa gane manufata. Kowanne Dan adam yana da tsarinsa, don ina sonki ba zan miki karya ba, abin da nasan zan iya shi zan miki, amma tun ba mu je ko'ina ba, na gane kin raina kulawar da nake ba ki gaba'daya"
Ya dan yi shiru sannan ya nisa ya ci gaba da fadin, "A farko tsakanina da Allah kamar yadda na fada mikil saboda jarrabawar da za ki yi yasa ban cika yawaita zuwa da kuma kiran ki a waya ba, sai ke kuma hakan ya zama dalilin da kika mini kishiyoyi, alhalin kin san har a gidanku na bayyana kaina ina son auren ki"
Ya fada muryarsa da rauni sosai.
Yayin da ita kuma kukan ya tsaya mata cak, tana jin wani irin abu na taso mata da ta kasa tantace mene ne shi.
Ya sake cewa, "Sa'adah duk motsin ki akan idona kike yin sa, ta ya ya ki ke tsammanin zan saki jiki da ke alhalin na tabbatar zuciyarki tana rawa a kaina! Na dade da gane kin samu mai kudi, na dade da sanin kina tare da Khalil har yanzu, ba don ina son ki sosai ba ai kamata ya yi na janye kaina a cikin 'yan takara amma kullum ina karfafa wa kaina guiwa da cewa idan rabona ce ke zan same ki, duk da haka dole na yi kaffa-kaffa don ba ni da tabbacin kina so na bare nasa rai Sugar Daddy ba zai kada ni ba!"
Kunya ta lullube ta, da kyar ta iya cewa "Ba ka da tabbacin Ina son ka fa ka ce?"
Da sauri ya amsa da cewa, "E wallahi da kina so na ba za ki saurari kowa ba, kin ga ni namiji ne zan iya hada mata biyu ko sama da hakan a rana na aura, amma tunda ke nake so, ke na aminta ta zamo mini uwar 'ya'yana ban sake kula wata da sunan soyayya ba. da na lura ba ki ba ni irin wannan matsayin ba, shiyasa na ke janye jikina, musamman yadda kika ci gaba da kula fitanannen yaron nan."
Kalamansa sun sa mata kasala sosai bayan kunyata ta da suka yi.
Da kyar ta bude baki a hankali ta ce, " Na daina!"
Ya yi murmushin da ya iso har cikin kunnenta, ya ce, "Mai ki ka daina din?"
"Abin da nake yi da ba ka so! Sannan kai ma ka daina mini wulakanci, kana nuna mini ba ni da daraja a gunka"
Ya sake murmusawa ya ce, "Akwai darajar da ta wuce na aure ki, na killace ki a gidana?"
Kunya ta kama ta, ta yi shiru dadi na cika mata zuciya.
Ya lankwashe murya sosai ya ce, "Ke ba ki san idan na tsananta zuwa ina kallon ki, za a samu matsala ba? Ko fa waya mu ka yi mai tsayi sai wanka ya kama ni, ya kike ganin kuma idan kullum zan gan ki a kusa da ni?"
Kunya mai tsananin gaske ta kama ta ta kashe wayar tare da rufe idanuwanta tamkar yana tsaye a gabanta.
Ya kira tana gani har ta katse amma ta kasa dauka ya ci gaba da kira har sau uku ta kasa dauka saboda yadda ya ba ta kunya.
Sai ga text ya shigo ta bude ta karanta kamar haka
_"Da gaske nake yi Sa'adah, don haka na roke ki, ki daina kallon rashin zuwana akai-akai da sunan rashin daraja ki, kokari nake yi mu kiyaye dokokin shari'a! zan zo gobe bayan Masallaci amma plz kisa hijabi ki 'boye wadannan abubuwan da suke karya mini alwala. Good night!"_
Ta karanta yafi sau ashirin tana jin shauki mai dadi na fizgar ta, tana jin ta tamkar a gajimare take yawo tsabar dadin soyayya. Ta hakikance MK shi ne mabudin farincikinta, duk wata damuwar zuciyarta ya wanke mata tas.
Alkalamin
*SURAYYA DAHIRU*
✍️✍️.
🌺 *HALIN YAU*! 🌺
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```
```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________
https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_Dokɑr hɑkkin mɑllɑkɑ me lɑmbɑ tɑ 68, tɑ nunɑ cewɑ sɑtɑr fɑsɑhɑ bɑbbɑn lɑifi ne dɑ yɑke dɑidɑi dɑ sɑtɑr dukiyɑ._*
*A guji taba ko sarrafa labarin nan ba tare da izinin mai Hakkin mallaka ba*.
*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*.
*TALLAH*
_Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number...... 08089965176 domin karin bayani, maganin ya samu lambar yabo saboda ingancinsa, yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k'iba dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka fara amfani da maganin zaki ga sauyi, domin yana gyara mace, zawarawa da 'yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!...ga masu bukatar sari ko sayan d'aya muna KANO muna turawa kowane gari 2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi.......*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya 'kare da ikon Allah._
40.
Washegari tun safe Inna ta lura da yadda Iyah ta tashi da kuzari da walwala, duk ayyukan gidan cikin kuzari take yin su sabanin kwanakin biyun da suka gabata da ta ke sukuku.
Kafin La'asar ta shirya, sai dai ta rasa hijabin da za ta saka. Gabadaya hijaban ta guda uku ne, biyu na Islamiyya ne, dayan kuma sallah take yi da shi, ta yi shiru tana nazari sai ta zabura ta fita. 'Dakin mahaifiyar ta shiga ta lalubo wani hijabinta da ta sayo a Jos amma ba ta taba sawa ba, a tsakar gidan ta ware shi kalar fari da maroon fulawa a jikinsa ya yi kyau sosai, ta saka ta ga ya zarta guiwarta da kadan, ta isa kusa da Inna da take zaune ta na tsinkar zogale ta ce, "Inna na dauko Hijabin nan."
"To." Kawai ta ce mata ta bita da ido, tana mamakin yau Iyah ce za ta saka hijabi ba don zuwa makaranta ba? 'Dakinta ta koma ta gama shiri, ta fito sanye cikin riga da siket na wani yadin material mai laushi, maroon colour! Hijabin ya hau sosai, ba karamin karbar ta suka yi ba.
Tana fitowa Inna ta juyo ta zuba mata ido tana raya komai Iyah ta saka sai ya mata kyau, ta ce, "Da kin san yadda Hijabin nan ya miki kyau da kin daina saka mayafi kin koma ado da hijabai."
Dariya ta yi tare da cewa, "Allah Inna tsokana ta kike yi"
"Da gaske nake yi miki, ba ki gan ki ba tamkar bakar Balarabiyar Habasha."
Dariya Sa'adah ta dinga yi sosai tana cewa, "Ashe har haka autar ki take da kyau Inna?"
Can kuma ta katse dariyar ta ce, "Inna Uncle Mukhtar ne zai zo kuma ya ce zai shigo ya gaishe ki."
Dadi ya sake kamata da sauri ta ce, "To! Kamo mini Baffanku a waya na fada masa."
"Kai Inna don zai gaishe ki ne za ki ce a fada wa Baffa?"
"Dole na fada masa mana tunda dai bai san wani zai shigo masa gida ba, idan bai amince ba ai kin san kuwa ba yarda zan yi ya shigo ba."
Sa'adah ta tura baki gaba alamun maganar Inna ba ta mata dadi ba ta ce, "Inna Uncle din ne wani?"
"Wani ne mana tunda ba mu da alaka da shi, sai ya aure ki tukun, zai zama cikin ahalinmu, amma a yanzu kam dole yana da iyaka."
Hakan kuwa sai da ta sanar da mijin nata, ya ce ya shigo idan ya zo babu damuwa. Ta kalli Iyah ta ce, "Komai aka yi shi akan ka'idojin shari'a ba a nadama, ke ma ki yi koyi da hakan. Kar ki yarda ki yi wasarere da hakkin mijinki, ko da baya gidan ki kiyayi duk abin da kika san ba ya so."
Sa'adah ta amsa da "To!" Sannan ta sauya maganar da tambayar, "Inna na dauko juice din?"
Da sauri ta amsa mata da cewa "Dauko mana ki hado da ruwa, ai ba sai kin tambaya ba."
"To Inna ai shekaranjiya na ga kin hana ni dauka ne!"
Tana rufe baki ita ma ta ce "Ai ba don shi aka saya ba, saboda Muutar ya sayo ya ce a ajiye idan ya zo ki dinga ba shi. Kin ga kuwa idan har ba Muutar ba ne ai ni ba zan bayar ba."
Wucewa dakin Sa'adah ta yi tana dariya tare da cewa,"Oh Innah maganar Baffa tamkar hadisi take a gunki!"
"Aljannata nake nema kin san kuwa aljannar mace ta fi samuwa idan mijinta ya yarda da ita."
Cikin dariya sosai Sa'adah ta ce, "Sadaqati Inna! Kin yi gaskiya In Sha Allah har a aljanna ke ce uwargidan Baffah."
Dariyar ita ma ta shiga yi tana fadin, "Allah ya shirye ki Iyah"
Daidai lokacin kuma waya ta hau kuwwa tana dubawa ta ga MK ne, ta amsa, ya sanar mata ya iso.
Ta mikawa Inna wayar tana cewa, "Ya iso."
Daki ta koma ta sake gyara fuskarta sannan ta feso turare ta fito, ta dauki tabarma ta na fadin, "Ki tashi Inna ki kintsa, na ajiye miki Hijabin da za ki saka a kan gado."
Harara ta galla mata tare da cewa ba zan saka wanda kika ajiye din ba 'yar fariya! Kin yi shigarki ta burgewa, amma kin tashi kin fesa turare."
Ta yi kwafa tana ayyana dauke shi za ta yi ta boye.
Murmushi ta yi tare da cewa, "Take heart