Showing 111001 words to 114000 words out of 186291 words

Chapter 38 - Halin Yau By Surayyah Dee

18 Dec 2025

9719

fashe da kuka fiye da na farko.

Yace "Na sani! yau kika fara period 'din ki na uku, me kike jin tsoro?"

Ta kasa yin magana, ya ce "Ni ya kamata na yi fargaba, Ni ya kamata na koka, domin zan rasa damata, sai dai na shiga sahun zawarawa, ke kuwa ai baki da damuwa idan har kina sona ai za'bin a hannun ki aka dam'ka shi".

Cikin kukan ta ce "Ban son muje ga haka, Ni ka zo ka dauke ni mu koma gidan mu, na yarda kar ka ci abinci na, kar ka kula ni har sai ka gamsu kamin abin da ka huce".

Ya ce "matu'kar muna tare kin san ba zan iya wannan jarumtar ba".

Ya sassauta ya ce "ki dinga addu'a sannan ki bar komai a hannun Ubangiji. Abin da nake so ki fahimta, wallahi na fiki shiga damuwa da tasku, kawai ni jarumta na fiki saboda kasancewata Namiji! Sannan ba zan ta'ba sauya hukuncin da na yi mana ba, har sai kin fa'da mini gaskiya koda hakan na nufin rushewar farin-ciki na gaba'daya, duk lokacin da kika shirya fa'da mini gaskiyar magana, ki mini magana".
Da haka ya kashe wayar gaba'daya.

Ta yi sororo da waya a kunnen ta, tana kallon agogo da ya nuna uku da rabi da minti biyu.
'
Har aka fara 'kiraye 'kirayen sallah barci bai iya surarta ba, tana ta tufka da warwara, ta yaya zata iya fa'da masa Khalil ne ya bata wadannan kayan? To akan wanne dalilin zai mata kyautar su ta karba? zuciyarta ta shiga harbawa, bare da ta tuno waccan kato'barar maganar da ta yi.

Ta yi amanna har da wancan laifin ya sake girmama wannan laifin a zuciyar Mk, sai ta yi kamar ta fa'da masa gaskiya sai ta tsorata, a yadda tasan ya tsani Khalil zai iya 'kararsa ko dan ya ci mutuncin gidansu tunda mahaifin Khalil fittacen 'dan siyasa ne, ita kuma ta hadu da zubewar mutunci a idon dangi dama duniya gaba'daya tunda tasan suna chatting da shi, ha'kika Sa'a na cikin hali irin na canka ca kare.

A fili ta dinga fa'din "Allah na tuba! na cuci kaina, son zuciya ya janyo mini 'bacin rai da damalmalewar lamura! Na keta alfarmar shari'a shiyasa na ke 'dan'danar 'bacin rai mai azabtarwa".

Tamkar mahaukaciya take surutai, tana sake cewa "Na yi al'kawari idan har na koma 'dakina bazan sake yin wani abu na rashin gaskiya ta kowacce fuska ba, sai da nace wa su Halima ina jin tsoron abin da zai biyo baya ta mini ingiza mai kantu, na biyewa 'kawar zuciyata na gasgata su, waiyo waiyo! Lah ilah ha illah anta subhanaka inni kuntu minan zalimin".

Duk akan kunnen Inna take wannan koke koken, da suratai duk da bata fahimci me take fa'da ba, da farko tsorata ta yi, ta 'dauka gwaiguna ne, sai daga baya ta fahimci daga 'dakin Iyah ne, a hankali ta fito, kasancewar Baffah yana Gogel.
Har ta isa bakin 'kofar dakin, sai kuma ta fasa, ta juya a zuciyar ta kuma tausayin'diyarta ya fara kamata, ta dinga mata addu'ar samun sassauci a zuciya.

Haka kwanaki suke ta shudewa, fargabar Sa'a na sake girmama, ba ta sake tuntunbar Mk ba, sai ana gobe za ta kammala iddarta, duk yadda ta kada billenta ta dinga ro'kon kar ya bari ta fita a matarsa bai ji ba, ya nan akan bakansa sai ta fadi gaskiyar lamari.

Washagari ta tashi da zazzabi ga kuka ya ki yanke mata. Inna ta kasa jurewa yanayin da ta ganta a ciki, har 'dakinta ta shiga ta zauna kusa da ita, ta ta'ba jikinta.
Zafi zau ta ji, ruwa ta samo da tawul ta dinga goge mata jiki. ta taimaka mata ta canja Riga, ta zubo mata kunu a kofi ta matsa mata ta shanye, sai dai tana gama shan ta amayar da shi tas.

Haka Inna ta sake gyara mata jiki, da kuma wurin, tana fatan inama ace ciki ne da ita wata'kila hakan yasa mijinta ya mayar da ita.

Baffah da bai fita ba, shi ya nemo Usaini mai chemist ya duba ta, ya kawo mata magungunan da zata Sha.

Tafi kwana uku tana mukurkususu, kafin ta fara warewa, saboda yanzu Inna ta sassauta mata, damuwar ta dan yi sauki.

Sati biyu da kammala Iddarta, tana tsakar gida tana wankin kayansu dana Inna sai ganin Jawad suka yi ya shigo a guje kamar yadda ya Saba.

Kai tsaye ya nufi uwarsa ya rungume ta, ita kuma idon Inna ya hana ta rungume shi, sai ta bige da fa'din wa ya kawo ka?

Yana jikinta yace " Malam ne, kullum sai na yi kukan gurin ki zan zo shine yau Hajiyar Bichi tace sai ya kawo ni, tunda jiya anyi hutun boko".

Inna da ta ke zaune tana fere doya tace "wato Jawad ba ka ganni ba ko, Anya kuwa za ka yi al'kawari?"

Kafin ya yi magana sallamar Hajiyar Bichi ta cika kunnuwansu tare suka shigo da Baffa, Inna ta mike da azama tana fa'din lale da Hajiyar Jawad, ashe tare ku ke tafe?"

Falo suka shiga! Inna ta gabatar mata da ruwa ta zauna Don gaisawa, sai taga Hajiyan na share hawaye Baffa na cewa "to ya za'a yi, sai ha'kuri, komai rubutacce ne, idan rabo bai 'kare ba za su koma, idan kuma ya 'kare sai duk mu yi ha'kuri, mu bisu da addu'ar fatan alheri! fatana dai ki cire damuwa a ranki.
Wallahi bamu 'kullace ku ba, Ni ko Mutari har yau ban ga laifinsa ba, Allah shine shaidata, kawai dai zan so ace sun shirya kansu ko dan rayuwar 'dansu ta inganta".

Murya a dakushe Hajiyar ta ce " Nima abin da nake ta hango musu kenan ban da dole yaushe za'a raba yaro da uwarsa! kome za'a masa ba zai gamsu ba idan ba uwarsa yake gani ba. Haka nan ba kowacce mace bace zata ri'ke'dan da ba nata cikin adalci da kyautatawa ba, akwai su amma sun yi 'karanci 'kwarai da gaske".

"Allah ya musu za'bi mafi alheri" Baffa ya fa'da yana barin falon.
Hajiya da Innah suka ha'da baki wurin cewa " AMEEN".

sannan suka shiga gaisawa tare da jajanta 'kaddarar da ta fa'dowa yaran su. Jikin Hajiya a sanyaye yake sosai, tunda abin nan ya faru take son zuwa, amma kunya da nauyi sun hanata, sai yau ta yi shahadar zuwa, ha'kuri ta bayar yafi cikin kwando, karbar da ta samu daga iyayen Sa'a yasa ta sake jin nauyinsu ainun, karamci a jininsu yake, tabbas Mukhtar ya yi asarar irin zuri'a me yakana da alheri.

Ganin Baffah ya fita ya Sanya Sa'a dauko Hijabinta ta saka ta shiga falo Jawad na binta tamkar jela.

Daga gefe ta tsugunna, ta gaida Hajiya kanta a 'kasa.

Hajiya ta hau fa'din taho ki zauna kusa da ni Sa'a.

Da rarrafe ta karasa kusa da Hajiyan, amma kanta a 'kasa tana Jin kunyar Hajiya na kamata irin wadda bata ta'ba ji ba.

Sosai Hajiya ke kallon yadda ta lalace ta yi ba'ki sosai, 'kwalla ta cika idonta a sanyaye ta ru'ko ta jkinta, hawaye ya gocewa Sa'a ba tare da ta shirya ba, tana yiwa kanta jajen rashin suruka irin Hajiya! Ta tabbatar samun uwar miji irinta a Yau zai yi matu'kar wahala.

Itama Hajiyar kukan take yi, tausayin Sa'a da Mukhtar da tilon dansu na matu'kar sa ta zubar da hawaye. Wacce irin ba'kar 'kaddara ce ta afka musu haka?

Mussaman yanzu da taga irin bibiyar da Jawad ke yi wa uwarsa, duk inda tasa 'kafa nan yake mayarwa, duk irin gatan da take masa, duk yadda ubansa yake masa siye-siyen kayan wasa da na ciye-ciye kala kala, bai hana ya yi kukan neman uwarsa ba, yanzu da ya ganta kuma ita ka'dai yake bibiya duk kuwa da yasan ubansa na 'kofar gida a zaune.

Duk dabarar Hajiya dan Sa'a ta fa'di musabbabin rabuwar ta su ta 'ki!kuka kawai ta ke yi mai tada hankali, Jawad kuma na ta goge mata kamar yadda ya saba yi mata idan tana kuka.

Tausayinta ya sake cika zuciyar Hajiya, ta dinga rarrashinta da kalmomi masu da'di.

Da zasu tafi Hajiya ta kalli Jawad taga ya ri'ke Sa'a sosai, sai ta yi nufin tsokanar sa ta ce "to zo mu tafi Jawad".

Ai kuwa nan da nan yasa kuka yana nuna dukkan yatsun hannuwansa yana cewa "Malam fa ya ce kwana haka zan yi?"

Hajiya ta yi gaba tana cewa "yi shiru da bakinka wasa nake maka".

Har zaure ta yi wa Hajiya rakiya, Mk na bakin kofar gidan a jingine yana waya, take zuciya ta ayyana wa Sa'adah da Farida yake waya a kofar gidansu.

Hawaye ya sake kwace mata, Hajiya da ta zaci ganinsa yasa ta kuka ta hauta da fa'da sosai tana cewa "wanne irin sakarci ne wannan Sa'a? Kina bada ni, banda bayar da kai menene ba zaki warware ki saki ranki ba, kina kallon kanki a madubi kina ganin irin lalacewar da kika yi?"

Ita dai Sa'a kuka kawai take yi 'kasa 'kasa, Hajiya ta nisa ta cigaba da cewa "ki kwantar da hankalin ki, kin ji!komai zai wuce kamar ba ayi ba, so nake nan da wata daya na ga kin dawo Sa'adatun nan mai birge yara da manya, Allah ya shiga lamarin ki, ya baki miji nagari, da zai wanke miki dukkan ba'kin cikin da kika kwankwa'da".

Wani irin kishi da Mk bai yi zaton zai sake ji akan Sa'adah ba, ya kama shi, takaici yasa shi barin bakin 'kofar ya nufi mota ya shiga yana ta a'uziya, saboda yadda ya ji takaicin Hajiya ya kama shi matu'ka da gaske.

Yana tuki amma zuciyarsa tamkar ta fashe, a gabansa Hajiya ke wannan fatan. ita kuma da ta lura da yadda yake ta 'dacin rai, tunda ta shigo motar ta gane kishi ne ya turnike shi, dan ayiwa matar da ya saka, ya ki mayar da ita fatan samun wani mijin.

Ta dinga kallon yadda ya fusata tamkar kububuwa, Hajiya ta tsinci kanta da mamakin kishin maza, ka saki mace, kace ba za ka dawo da ita ba. Sannan baka son kowa ya aureta alhalin tana cikin shekarun da take bu'katar auren.

Itama haushinsa ya kamata da ya kasance cikin masu son kansu, sannan har ita zai yi wa wannan fishin?.

Dan haka Yana shan kwanar layin 'Dan Hassan da shine layinsu amma a ciki suke sosai, sai an hau abin hawa.

Murya a dake ta ce samu wuri ka tsaya! Bai yi musu ba, ya gangara ya yi parking.

Ba jinkiri Hajiya ta fito cikin sa'a kuwa ta tsayar da dan adaidaita da zai shiga ciki, ba 'bata lokaci ta shiga suka tafi.


Ba'kin ciki ya sake kama Mk idonsa ya yi jawur, ji yake tamkar ya hadiyi zuciya ya mutu, Hajiya da Sa'a su huta da ganinsa.

Yasan Jawad kawai ke da asarar rashin mahaifi, amma ita Hajiya tana da Ahamad, haka nan Sa'adah zata auri wani ya iya mantar da shi a ranta, amma Jawad fa?
Duk yadda yake da tabbacin Abbas da Ahamad har ma da 'Karfi baza su bar tilon 'dansa ya yi kukan maraici ba, ya tabbatar Jawad ba zai rasa uba ba, amma tabbas zai yi asarar rashin mahaifi da ba a samun biyu.

A hankali ya ja motar yabi bayan su Hajiya. Tsawon lokaci yana gurfane gabanta, ita kuma ta yi 'diban karan mahaukaciya da shi.
"Hajiya Dan Allah ki gafarce ni, ban san me na yi miki ba, fishin ki dafi ne a rayuwata, ki mini ha'kuri dan Allah". Karo na hudu kenan yana maimaita wannnan kalamin, ta kalle shi ta ga duk ya sake firgicewa, da gaske tasan yana tsananin gudun zuciyar ta, amma dole ta nuna masa ita ba UWA bace irin Agwagwa ba, yaranta a gaba ita tana binsu a baya. Ita kaza ce da ta ke gaba 'ya'yanta na bayanta, sannan idan ta ga 'da ya yi rashin 'da'a ta take shi ba dan bata sonsa ba sai dan ya zama nagari abin so da kwatance a ckin alumma.


A raunane ta ce "Kai ne da ha'kuri da na yi laifin da zaka iya mini fishi, har yaushe ka yi motar? da zaka dauko ni ka hade mini fuska tamkar wadda ka mini alfarma, ka sani ai ni ba bakuwar mota bace, idan ana sako wadda suka fara mallakar mota a Bichi da kewaye sai ansako gidanmu. sannan tun kafin a haifeka duk inda zani a mota ake kaini, bude ido ka yi ka ga mota a gidannan bare ka mini wani iyashege".

A matu'kar gajiye Mk yake fa'din "Na yi kuskure, ki yi hakuri abin ne yafi 'karfi na, ki mini uzziri Hajiya, ki sake dagewa wurin yi mini addu'a".

Ya Dora hannunsa daidai setin zuciyar sa ya ce, "zuciyata ciwo take mini sosai, tana mini zafi, wataran har numfashi bana iya yi, dan Allah ki yafe mini kar mutuwa ta zo mini kina fishi da ni, zan roke ki, komai na miki, da wadda zan miki nan gaba ki dubi Allah ki yafe mini, Ina rayuwa ne kawai amma wani lokacin bana sanin me nake ciki".

Tausayinsa ya kama Hajiya sosai, ta zuba masa ido tana nazarinsa.ta sassauta murya tace kana son ka warke daga ciwon da keke 'dan'dana, kana son nutsuwa ta zo maka, ka dinga sanin halin da kake ciki, kana son nutsuwar da ta yi maka tutsu ta dawo maka?

Ya ri'ke hannun ta muryar sa na rawa ya hau cewa 'ina so Hajiya, bana iya barci fa, ko abinci da na fara ci sai na ji ya tokare mini a wuya shikenan sai na kasa ci, kuma ina jin yunwar".

Hajiya tace "fada mini laifin da Sa'a ta maka na san shine yake neman kassara ka, rashinta kusa da kai ne yasa kake rasa gane halin da kake ciki domin kana sonta, farincikinka na 'damfare da ita ne".

Bai musawa Hajiya ba domin kuwa yasan gaskiya ta fada, amma sai ya saukar da kansa 'kasa ya ce 'kaddara ce ta rabamu Hajiya".

Cikin rarrashi ta ce "Ni uwarka ce, duk wadda zai ri'ke maka sirrinka a bayana yake, me yasa kake gudun abin da ka ke so da gangan?"

Sai lokacin bacin rai ya sake taso masa cikin fitar hayyaci ya ke firzar da maganganu " Ina sonta sosai, Ina son na rayu da ita, komai Ina yi mata, har da wadda ya fi 'karfina yi mata nake yi, amma kullum cikin zullumi nake zaune da ita, fa'da mini Hajiya me na gaza da ban cancanci na sami kwanciyar hankali da ita ba?".

"Ba ka gaza ta ko Ina ba, itama ai kullum cikin damuwar take tunda kishin rashin hankali ta 'dorawa kanta".

"Yanzu fa'da mini abin da ya kawo musabbabin rabuwar dan nasan irin hukuncin da zanyi, na kuma daina zarginka da manta alheri, da kuma rashin ha'kuri".

"BA KOMAI QADDARAR MU CE".

Ta zuba masa ido ta ce "Ko dai Ni ta zaga ko mahaifinku ko Hajiya Babba?".

A hankali ya girgiza kansa ya ce "Haba dai, ai komin tsiyarta ba ta isa ta mini hakan akan idona, na barta haka salin alin ba, sannan fa Hajiya yadda kike sonta haka take son ki, Ina mata shaida ko giyar wake ta sha ba abin da zan yi mata ta zage ku".

Ta kalle shi tana tuna fa'dar gaskiyarsa tun yana Yaro yana cikin abin da ya janyo masa soyayya a zuciyar mahaifinsa.

"To Ni dai indai ba wannan laifin ba, banga me zata yi ka 'ki yafe mata har haka ba".

Zuciyar Hajiya ta kasa daurewa tace "ko dai kama ta ka yi da wani?"

A zabure ya mi'ke yana fa'din subhanllah! haba dai Hajiya me yasa za ki yi wannan hasashen, har abada Sa'a ba zata yi hakan ba, in sha Allah ba zata yi hakan ba duk lalacewar *HALIN YAU* SA'ADATU ba zata yi hakan ba".







*SURAYYA DEE*
✍🏼✍🏼.


🌺 *HALIN YAU*! 🌺




•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```

```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________

https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•





*_Dokɑr hɑkkin mɑllɑkɑ me lɑmbɑ tɑ 68, tɑ nunɑ cewɑ sɑtɑr fɑsɑhɑ bɑbbɑn lɑifi ne dɑ yɑke dɑidɑi dɑ sɑtɑr dukiyɑ._*


*A kiyayi ta'ba wannan labarin ba tare da izinin mai Hakkin mallaka ba*.


*Fatan alheri ga*
*UMM ASGHAR NOVELS*.
*NOVEL ONLY GROUP*.
*Da dukkan grops din da ake tura wannan labarin ake sharhi tare da fatan alheri, ina ji ina kuma godiya da fatan Allah ya bamu damina mai albarka*.


*Gaisuwa ga*

*Fati Eshaik(Ummu Asghar)*
*Zalhatu Umar(Yayar mu)*
*Hauwa Umar(Mrs Nasir)*
*Zainab Abdullahi(Beneficial group)*.
*Fatima (Maman Aslam)*
*Aunty Ai'nau*
*Hauwa'u Umar Gwaram*
*Balki Sani*.
*Rahma Shu'aibu Kankara*.
*Kulsum Baffah Azare*.


*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*.



83-84.



Sosai Hajiya ke nazarinsa, sannan ta sami nutsuwa da ya kasance ba abin da shaidan ke kissima mata bane. Dan haka sai ta ce "idan kuwa hakane banga menene mai zafi da ba zaka yafe mata ba, wallahi ta gane kuskuren ta, ka bata wata damar Ina tabbatar maka lafiya lau za ku zauna".

A hankali ya ce "Dan Allah Hajiya na ro'ke ki, ki bar wannan maganar, ki mini afuwa, ki kuma yi mini alfarmar daina yin wannan maganar, kawai fatana ki mini addua".

"To shikenan Allah ya yi zabin alheri".
Ta fa'da jikinta a sanyaye.

Ta bangaren Sa'a kuwa, har lokacin tana yawan 'kiransa a waya ta bashi ha'kuri, ko ta yi text, har ta kai har makaranta ta bishi, ta tsugunna a gaban sa cikin cire girman kai, tana bashi ha'kuri, a irin haka Farida ta fa'do ofis 'din ta tarar da su a hakan, ta juya da mugun sauri tana fa'din "Sorry excuse me"

Ganin da Farida da ta yi mata gurfane a gabansa ya matu'kar dukan zuciyar Sa'a, da muryar kuka ta kalle shi tace "yanzu ita ka ke so shiyasa ka rufe mini 'kofar afuwa ko?"

Kai tsaye ya ce "kinsan ba haka bane ,amma idan haka zuciyar ki ta rinjayar miki to bazan 'karyatata ba! Kar ki kuma zuwa mini nan, idan kina son magana da ni ki kira Ni a waya, Ni Kuma zan zo!amma wannan ya zama shine zuwan ki na karshe if not, zan fa'dawa Baffah".

Da kuka sosai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login