Showing 30001 words to 33000 words out of 186291 words

Chapter 11 - Halin Yau By Surayyah Dee

18 Dec 2025

9740

aure za su yi ba wata 'barna ba.

Ya gaji da shirunta, ya ce,
"Kina tare da ni kuwa?"

Nan ma shiru ta yi, bai ji dadin shariyar da ta mishi ba, amma sai ya waske, ya san dama haka take, bare kuma yau ya ta'bo ta.

'Kasa ya yi da murya sosai ya sake cewa, "Magana fa nake miki, amma kin yi mini shiru".

Cike da fishi sosai ta ce
"To ni me zance?"

Zuba mata ido ya yi, yana kallon yadda take ta cika tana batsewa har wani huci take yi, jikinsa ya yi sanyi bai cika son mace mai fusata sosai irin haka ba, sai dai son da yake mata ya riga ya yi bunkasar jurewa duk wani kalubale daga gare ta.

Wannan karon ido ya zuba mata, tare da bude murya sosai ya ce, "Ina ta miki magana amma kina jina kin mini shiru, kar ki bari na ji a zuciyata son da na ce ina yi miki shi ne dalilin da za ki fara raina ni".

Kawai sai ganin hawaye ya yi yana tsere a kan kuncinta, tana ta yunkurin bude baki don ta yi magana amma ta kasa.

A ransa yake fadin akwai aiki a gabana, a kankanin lokaci ya gane shagwababbiya ce ta gaske, banda haka mene ne kuma abin kuka a maganar da ya yi? kan dole ya yi ta rarrashi akan ta fada masa abin da yasa ta kuka cikin maganganun da ya yi.

Cike da kukan kuwa ta hau cewa, "Ai an sha fada mini duk saurayin da yake boye kanshi kar a san yana son mace, to ba da gaske yake ba, yaudarar ta zai yi".

Ta 'karasa maganar cike da gunjin kuka, mamakin ta ya kama shi sosai ya ce, "Amma na sha fada miki gidanku ba gidan da zan yi wasa ba ne, tunda kina shakku a kaina a satin nan zan gabatar da kaina a gaban Baffa shike nan?"

Ta goge Hawayen da ya'ki tsaya mata, a hankali ta ce
"To saboda kar Farida ta sani ne kake son a boye?"

Takaicinta ya kama shi, amma kuma ya kasa yi mata jan ido, sai ma lallaba ta da ya shiga yi, ta hanyar fadin. "Sa'adah ya kamata ki dinga fahimta ta, inda Farida nake so, nake burin aure ba abin da zai kawo ni gunki tunda ba dole aka mini ba! Ribar me zan ci idan na zo don na miki karyar ina son ki? Mahaifinki mutumin kirki ne, na san shi, tun kafin na san ki, akan me zan yaudari yarsa? Ina son ki yarda da ni, yarda ita ce matakin farko a soyayyar gaskiya, abin da yasa nake son mu bar maganar a tsakaninmu ba komai ba ne illa don na kiyaye dokar makaranta!

Ba makarantar da ta yarda malami ya yi soyayya da 'daliba, ni kuma zan yi iyakar'ko'kari na kiyaye kowacce irin dokar makaranta, ta kowacce fuska wannan shi ne gaskiyar magana".

Ta yi kasa da kanta, tana jin nutsuwa da maganganunsa.

Ya nisa ya ce, "Kin yarda da manufata?"

Kai kawai ta 'daga mishi alamar eh, sai ya ce "To ba ki ce komai akan wancan yaron ba"
Ta sake yin kasa da kanta ta ce,

"Ai ni ba saurayina ba ne".

Da sauri ya ce "Magana muke ta gaskiya fa Sa'adah! kin san har letter da kika masa wacce na dauka tana nan, kawai idan kin amince kina sona, to ki fita harkarsa, kin san dai yaro ne karami, da ba zan iya hada soyayyarki da shi ba, ga shi dama ba tarbiya ce ta wadace shi ba".

Kanta tsaye ta ce " To! na ji zan rabu da shi, kai ma kuma ban yarda na dinga ganinta tare da kai ba, kodayaushe tana hanyar staffroom saboda kai, kai ma da ka motsa sunanta ne a bakinka, to ba ita kadai ba ce mai 'kokari ba, ire irenta suna nan, wasu da yawa ma a cikin makarantar sun fita kokarin, ita zubin Sadakar Yallah da kuke gani a tare da ita yasa kuke ga kamar ta fi kowa".

Mamaki da dariya suka kamashi lokaci guda, amma ya dake bai bari dariyar ta fito ba, ya ce, "Amma ai na tabbatar miki ba son ta nake ba, sannan kin san dole wani abin zai hada mu tunda dai ni malaminta ne, abin da za ki yarda da shi shine wallahi ba budurwa ta ba ce, ba ni kuma da niyyar auren ta".

"Amma da bakinka kace mini za ka iya maye gurbina da ita".

"Tabbas na fadi hakan amma ki sa a ranki sai idan ke ce kika so faruwar hakan, ina nufin kika juya mini baya, sai na yi maleji da ita a rashin ki, kin san Bahaushe ya ce a rashin uwa, akan yi uwar'daki".

Da'di ya kamata har murmushi ya subuce mata, shi ma ya taya ta murmushin tare da cewa,

"Na rantse miki ban taba ganin wacce ta fi ki kyau a duniyata ba, musamman idan kika murmusa".

Kunya ta kamata tasa dukkan hannunwata ta rufe ido tana jin kamar su tabbata a haka.

Ganin sun dan fahimci juna ka'dan ya ce "To muje ki tafi gida kar aga kin dade da yawa, tunda ba za ki yarda na kai ki ba".

Sai da ya sa ta cikin Adaidaita Sahu ya biya kudin, sai da ya ga sun tafi sannan ya koma ya hau mashin dinsa yana jin shauki na shigarsa, yana kuma jinjina kishin Sa'adah.


WAYE MK BICHI?

Haifaffen karamar hukumar Bichi ne, a jahar Kano. Mahaifinsa Alhaji Kabiru Wadata, Bafulatanin Bichi ne, mai arziki ne a lokacinsa, don zai shiga cikin jerin attajiran Bichi shi yasa ake masa la'kabi da Wadata. 'Dan kasuwa ne mai sana'ar fata, yana fataucin ta zuwa jahohin Arewa.

Mukhtar shi ne babban dansa na namiji, shi ne kuma na biyar a dukka gidan, an haifi mata hudu kafin shi.

Matan gidan biyu ne Hajiya Babba (Indo), tana da yara bakwai wadda ukun farko dukkan su mata ne, Zainab, Khadija, Amina, kuma duk sun girmi MK, sannan Abbas, Akil, Sameera, da auta Bilkisu.

Sai dakin amaryar gidan wacce ita ce mahaifiyar MK, Hajiya Rabi yaranta uku kacal, Hafsatu ce Babba, sai Mukhtar sannan auta Ahamad, da Mk ya girme masa da shekaru kusan goma

Mahaifin MK mutum ne mai sau'kin kai, mai kokarin wadata iyalinsa da komai na bukatar rayuwa, dukkan su, sunyi karatu, matan dai suna kammala sakandire yake aurar da su, yayin da mazan ke zurfafa karatunsu a jami'o'i daban-daban a cikin kasar nan.

Gidansu akwai zaman lafiya, duk da ba a rasa yan kananun gutsuri tsoma irin na gidan Polygamy Family, amma dai nasu da sauki ainun kasancewar iyayensu matan ba su cika samun sabani ba. Idan ma sun samu to suna bari a tsakaninsu ba tare da sun bari yaransu sun shiga rigimar da ba tasu ba.

Wannan dabi'ar tasu, tasa hankalin mijinsu ya kwanta da su, inda yake musu hidima su da ya'yansu kan jiki kan karfi.

Mahaifinsu a tsaye yake kan sha'anin tarbiya, sannan ya dace da mata na-gari da suke taya shi, dora yaran akan kyakkawar turba, domin kuwa duk yadda namiji ya kai da kula da tarbiyar yara in bai yi dace da mace ta-gari ba, to da wahalar gaske yaran su bi tsarinsa.

Mukhtar ya fara karatunsa a kwalejin ilimi ta tarayya dake garin Bichi, bayan ya kammala sakandiren hadaka ta gwamnatin jaha (Unity Boys Karaye). Sai da ya kammala NCE, sannan ya yi JAMB ta D.E, ya yi sa'a ya samu level 200 a jami'ar Bayero, inda ya karanta harshen turanci (English Language), yana shekara ta biyu ne Allah Ya yi wa mahaifinsu rasuwa a hadarin mota ya je dauko Bilkisu a makarantar kwana, wacce tare suka rasu da Bilkin.

Wannan mutuwa ta matu'kar taba ahalin wannan gidan, dole suka tattara suka ha'kura suka bi su da adduar samun rahamar Ubangiji.

Haka iyayensu mata suka ci gaba da zama suna ci gaba da kula da ragowar yaran da ke gabansu wanda Sameera ce kawai ta rage ba a aurar ba sai maza su kuma suna ta karatunsu cikin nutsuwa.

Da ma can suna da sana'oinsu, sai suka samu sau'kin tafiyar da gidan da kuma tallafin 'ya'yansu maza da mata, musamman MK da ya kasance shi ne babba, kuma shi ya debo kusan halin mahaifinsu, na hakuri da yawan kula da lamarin gidan.

Yana da sau'kin kai ta yadda duk yan'uwanshi suna jin da'din mu'amala da shi, kafin ya fusata yana jimawa, amma fa idan ya yi fishin wuyar sauka ne da shi.

Abu mafi kyau cikin halayyar MK Bichi, ma'abocin addini, mai kokarin kiyaye dokoki ne na gaske, sannan duk layin da ba gaskiya, ba za ka same shi a ciki ba. Akidar son bokon da ya taso da ita bai sa ya yi watsi da kyawawan al'adun Malam Bahaushe ba.

Sannan MK ma'abocin 'kamshi ne tun yana Secondary, da kamshinsa ake gane ya zo guri, bayan haka kuma He is Frank and friendly to all.

Wannan ke nan.




Alkalamin
*SURAYYA DAHIRU*
✍🏼✍🏼.

🌺 *HALIN YAU*! 🌺




•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```

```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________

https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•





*_Dokɑr hɑkkin mɑllɑkɑ me lɑmbɑ tɑ 68, tɑ nunɑ cewɑ sɑtɑr fɑsɑhɑ bɑbbɑn lɑifi ne dɑ yɑke dɑidɑi dɑ sɑtɑr dukiyɑ._*




*KAR KU BARI A BARKU A BAYA WURIN KARANTA LABARIN HAZI'KAR MARUBUCIYA*.

*⚜️BUƊAƊƊIYAR SOYAYYA⚜️*

*Jameey yar'mutan kankia*.


*Promo* *Promo* *Promo*


_Daga yau 21/5/2022 promo dinmu zai fara,har zuwa 30/5/2022 inshaa Allah,ga yanda promo din yake_.

*#300-sau biyu a rana*
*#500 -sau ukku a rana*
*#700 -sau hudu a rana*


_Kiyi man wanann number magana danjin ynda zaki biya 08160508316_.



*MASU SON A TALLATAH MUSU HAJARSU 'KOFA A BUDE TAKE*
_TUNTUBI_
08032773332.





*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*.




32-33.





Tana isa kofar gida ana kiran La'asar, sai da gabanta ya fadi saboda yadda za ta sha tuhumar inda ta tsaya har zuwa wannan lokacin a wurin mahaifiyarta.

Ilai kuwa a tsakar gidan ta tarar da ita sai safa da marwa take yi, jin sallamar ta yasa ta tsaya cak, tare da zuba mata ido, amma ganin ta futu-futu kuma idanuwanta a kumbure sai ta sami sau'kin tashin
hankalin da ta shiga, don ta tabbatar Iyah ba za ta iya biyawa wani wajen a haka dukun-dukun ba, amma duk da hakan sai da ta ce "A ina kika tsaya har zuwa wannan lokacin?"

Fuska daure ta ce "kwanakin da na yi ban je makarantar ba shine suka ci zalina."

Ajiyar zuciya Innar ta sauke sai kuma ta ce "Madalla da wannan cin zalin."
Sannan ta dauki buta ta zaga ban'daki.

Sa'adah daki ta yi tana tube kayanta, zuciyar ta fes ,tana tuno hirar su da MK da ya mantar da ita takaicin da ya kunsa mata a safiyar yau.

Tana idar da sallah ta wanke uniform din da ya baci da 'kura sannan ta zuba abinci, kai tsaye falonsu ta shiga wanda ba komai sai leda a shimfide da labulaye, sai yar karamar talabijin kirar (sharp) a kan dan karamin tebur, kusa da mahaifiyarta ta zauna da ta ke kulla bushasshiyar kubewa.

Ganin Innar ba ta 'daga kai ta kalle ta ba yasa ta fadin, "Inna ko ki tambaye ni, ko na ji ciwo a cin zalin da aka mini?"

Cike da rashin kulawa ta ce "Tsuntsun da ya ja ruwa shi ruwa kan doka, tunda kin yi girman da za ki zabawa kanki abin da ya dace da ke ai magana ta 'kare"

Jikinta ya mutu ta ce "Inna kin ce magana ta wuce, amma kina ta share ni kina nuna ko oho da ni" Ta ture abincin tare da fashewa da kuka.

Da farko share ta ta yi, amma jin yadda take ta sauke ajiyar zuciya, ga kuma hawaye nata tsere a fuskarta, sai ji ta yi raunin da bata son ta nuna mata ya kubce mata cike da tarin soyayya irin ta uwa ta tausasa murya ta ce "Share hawayen kin san dai ba na son kukan ki ko?"

Ta tura baki cike da shagwaba ta ce "Inna ai da ne ba kya son kukan nawa, yanzu sau nawa za ki ga ina kuka amma ko ki nuna kin gani bare ki rarrashe ni?"

Murmushi ta yi ta ajiye ledar da take hannunta ta zuba mata ido sannan ta ce "Iya bawai kukan naki bai dame ni ba ne. Ni kadai na san yadda zuciyata ke zafi idan na gan ki cikin rashin sukuni, halayen da nake gani a tare da ke ne ba su mini ba, ina matu'kar kaduwa da yadda kike kokarin jefa kanki a rayuwar da ba za ta bulle da ke ba"

Sa'adah da jikinta ya yi laushi amma sai ta yi karfin halin cewa, "Don Allah Inna wai mene ne nake yi wadda bai miki ba?".

Muskutawa ta yi sannan ta ce "Iyah kin san dai ke din nan ba 'yar kowa ba ce, mu iyayenki ba wasu ba ne illa masu neman abin da asirinmu zai rufu, amma ke kina daukar ra'ayin ya'yan masu wadata, ba kya duba idan ba yawan gashinku daya ba, yawan kitson ku ba zai daidaita ba! Watanni kadan ya rage ki kammala makarantarki, kin san kuma aure za a miki amma duk saurayin da zai zo gidan nan da maganar aure za ki yi tsalle ki ce bai miki ba, amma kina son abin hannunsu saboda kawai kin 'dorawa kanki sai kin daura abin da kike gani a jikin yaran da 'karfin iyayenku ba 'daya ba"

Ta nisa tana jiran ko Sa'adah za ta yi magana sai taji sabanin hakan, duk da dai ta lura jikinta ya sake yin laushi fiye da 'dazu, don haka sai ta sake cewa, "Ki ajiye wannan dabi'ar, sannu a hankali idan kina da rabon yin arzikin za ki yi shi ne. Yanzu dai babban misalin da zan miki da yayarki ne, duk da cewa lokacin da aka aurar da ita ba ki da wayon da za ki gane komai, mijinta ko mashin din da kika raina mai hawansa ba shi da shi, amma a yau mene ne bai mallaka ba? A saninki 'kasashe nawa ya debi iyalinsa suka fita? Wace irin hidima da karamci ne ba ya mana ke ma shaida ce tunda dai ko wannan makarantar da kike yi ba don shi ba, da ba ki yi ta ba, da ace farko ta raina matsayinsa da yanzu ta cim ma wannan jin dadin da kowa ke mata kallon tana ciki? Tsakanin ki da Allah ba don ta sau'ka'ka buri ba ta kai wannan matsayin?"

Kai Sa'adah ta girgiza wa mahaifiyarta don kuwa harshenta ya mata nauyi, amma a ranta tana raya in dai akan zaben miji ne an wuce wannan babin, zuciyarta ta riga da ta aminta da MK Bichi kuma shi ma ai talaka ne tunda ko mota ba shi da ita. Jin da'di da son kayan 'kawa kuwa ba mahalukin da ba ya so sai idan bai samu ba, ita a jininta ne son gayu ba wai fariya ko 'karya ta sa a ranta ba. 😀 Don haka ba ta dauki maganar ajiye dogon buri da aka mata nasiha da wani muhimmanci ba.

"Kullum addu'a ta Allah ya ba ki miji nagari wanda zai kula da ke da amana, ke ma irin adduar da za ki rike ke nan. Dauki abinci maza ki ci kar ya gama hucewa, Allah ya miki albarka."

Ajiyar zuciya ta sauke ta ce "Amin na gode?" Sannan ta ja abincin ta hau ci, danwaken fulawa ne da yaji mai da'din gaske, tana ci tana yaba yadda Innarsu ta iya sarrafa abincin gargajiya masu da'di, kawai dai abincin zamani ne ba ta yin su ko kuma don za su ja kudi ne?

Sai ta tsinci kanta da cewa "Allah Inna na kusa daina cin abinci mai nauyi."

Cike da mamaki ta ce "Me za ki dinga ci to?"

Murmushi ta yi, ta ce "Chips, chicken, sai dangin su pizza, da indomie da kwai, sai na bi bayansu da ababen ruwa irin su juices da yougurt ko hadadden shayi hadin kauri."

Salatin da Inna ta 'dauka ne ya sa ta dakatawa tare da tunanin ta yi subutar baki.

"Ashe duk togaciyar da na gama yi miki bai shiga kunnenki ba? A gidan uwarki kika san wadannan kayan, wadda ba ta alfahari da abin da ta bude ido ta gani a gidansu, sai hangen kayan wani da ba ya rufa maka asiri!
Nasan kina nufin idan kin je gidan miji ne kike tunanin wannan rayuwar za ki yi"

Ta kafe ta da ido tana mata kallo mai tsanani sannan ta ci gaba da cewa, "To saurare ni da kyau aure ya wuce wasa tun wuri ki cire wannan tunanin a ranki, gabadaya aure ibada ne, duk abin da akace ibada ne, to ba son ranka za ka yi ko zaka gani ba, sannan ba abin da ke ri'ke da aure gabadaya sai ha'kuri don haka ki cire wannan tunanin a ranki. ki yi fatan Allah ya ba ki miji nagari, da hankalinki zai kwanta, domin komai za ki samu idan ba kwanciyar hankali ina tabbatar miki ba za ki ji dadinsa ba Allah ya shirye ki, adduar da zan dinga miki ke nan."

Ta fada da iyakacin gaskiyarta, domin ta lura addu'a ce kawai za ta canja mata Iyah ba hantara ko nuna fishi ba.

***

MK yana isa gida ya tarar da Hajiyar Bichi ta zo, a falo ya tarar da su ita da Hajiya Babba suna cin makani wanda ba ya tantamar daga Bichi ta taho da shi, da murna ya hau fadin,
"Hajiya ashe da gaske kike da wuri za ki dawo?"

Dariya ta yi ta ce "Allah Ya yarda ban dade ba".

Suka ci gaba da hirarsu har su Abbas da Ahamad suka dawo aka ci gaba da hirar da su, Maghriba ce ta dakatar da su.

Bayan sallar Isha MK ya tarar da Hajiya Babba a dakinta, ya gama kame-kame da soshe-soshen 'keya, sannan ya ce "Hajiya so nake aje a tambayar mini izinin magana da wata yarinya a wajen

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login