Showing 135001 words to 138000 words out of 186291 words

Chapter 46 - Halin Yau By Surayyah Dee

18 Dec 2025

9699

hade girar sama da ta kasa kuma bai amsa ba, hakan da ya yi ya sake hassalo da Sa'a.

Baffah ya cije ya ce "Yanzu kuma laifinka ne ta gaisheka baka amsa ba, tunda hakane sai ka tashi ka kaita, ai bazai yiwu ka sace mata iska a banza ba, dole ka hutar da ita tsayuwar jiran mai adaidaita sahu dama kuma garin hadarine sossai".

Mahmoud ya yi maza ya ce "To Baffa bari mu kaita mu dawo, mun gode Allah ya kara girma".

Baffah ya shige gida ya barsu a zauren Sa'a ta na jin tamkar ta yi ta zunduma ihu.

Hawaye ya dinga tsere a idonta, wannan irin bada ita da Baffa ya yi? Duk wula'kancin da Mk ya mata wato Baffah bai ga laifinsa ba, daga zuwa da magana zaice ta shiga motarsa ya kaita a matsayinsa nawa din ta?
Zauciyarta ta kuntata sosai tana jin gara ta tafi da kafa a kan ta shiga motar Mk.

Har suka fita kofar gida kuka take marar sauti, Mahmoud ya bude mata gaban motar, ta cije, a hankali ya ce "a titi muke fa, sannan umarnin Baffa zaki bi, ba son ranki ba" .
"Akan me za'a tilas ni shiga motarsa,?"

Ta fa'da cikin rishin kuka.
"Yi ha'kuri ai dukkan mu umarnin Baffa zamu yi wa biyayya akan kunnen ki dai ya hukunta Mk ta hanyar mayar da shi dureban ki, adalilin amsa gaisuwar ki da bai yi ba. Kina kallon bai yi musu ba sai ke?"

Hawaye ya zubo mata ta ce "Ni na yafe masa zan tafi da kaina".

Mahmoud ya ce "Ai tunda Kika bari Baffa ya shige cikin gida dolen Mukhtar ya miki direba kar ki yadda ki sab'awa mahaifin ki adalilin wani Mukhtar".

Take Sa'adah ta gane gaskiyar Mahmoud ne, tunda rashin gaisuwar da bata yi bane ya janyo mata wannan hukuncin mai kama da saukar aradu.

Maimakon ta shiga gaba inda Mahmoud ya bude mata sai kawai ta bude baya ta shiga.

Da azama Mahmoud ya isa setin direba Mk ya juya musu baya tamkar baya wurin hakan da ya yi ya sake tunzura Sa'a tun fil'azal ta tsani a nuna mata rashin kulawa.

Mukullin hannun Mk Mahmoud ya karba, a hankali ya ce "shiga baya mu je".

Ba musu Mk ya bude bayan motar ya zauna, Yana rufewa Mahmoud ya ja motar.

Zuciyar Iyah tamkar ta fa'do kasa dan tsananin ba'kin ciki mussaman da ta tuno irin addu'ar da dinga yi, tun bayan da ya auri Farida na kar Allah ya sake ha'data ko da zaman mota ne da Mukhtar balle kuma zaman aure, sai gashi karon farko da zaman motar aka sake ha'dasu, zuciyar ta dinga bugawa fiye da kima tana fargabar menene zai biyo bayan wannan zaman?


Ta dinga jin takaicin kin shiga gaban motar, da ta shiga ai tasan shine dole zai ja motar, Kuma dolensa ya zauna iya kujerarsa sannan ya kula da tukinsa.

Amma yanzu ya babbake har gefen jikinsu na gogar juna, gilashin motar irin na munafunci ne wato tint, ya matseta sosai tamkar su hudu ne a bayan motar.

Ba'kin ciki ya isheta sai kawai ta fashe da matsanancin kuka mai sauti sosai, Mk ya yi tamkar bai ji ba, yayin da Mahmoud ya juyo da sauri tunda a tsaye suke traffic ya tsayar da su.

"Menene kike yi haka Sa'adatu?"
Zuciyarsa ta buga ganin yadda Rabin jikin Mk na jikinta, wani irin abu ya tsayawa Mahmoud da bai yi zaton zai ji ba, ya juya da sauri ya dauke fuskarsa yana ambaton innalillahi.

Kukanta ya dinga tsuma Mk ya dinga jin tamkar ya danneta ko ya samu sau'kin halin da yake ciki.

Ya lura fishi na fitar hankali take yi da shi, idan ya ce zai lalla'ba ta to ya kai shekara yana fama adalilin taurin kai irin nata.

Ba zato Sa'a ta ji Mk ya ja uban tsaki mai tsayi, sai kuma ta ji yana cewa "Mahmoud saka mini wa'kar Auren Dole ta Ali jita".

Dariya Mahmoud ya yi ya ce "bansan jita yayi wakar auren dole ba, ta aure mai da'di nasan ya yi"

A gajarce Mk ya ce "to lalubo mini wadda zata dace da halin takurar da nake ciki, banda Hajiya da Baffa sun matsa mini, ina zan zo gurin wannan shugabar masu wula'kancin da niyyar wata magana, ai tun wulakantani da ta yi a ziyarar Jawad na gane idan ka shekara dubu baka mutum ba, kar ka tambaye shi komai binciki halinsa".

Ya nisa ya sake jan tsaki ya ce " Ta tisa ni tana kukan gulma da iskanci, alhalin kasan ranta murna da farin-ciki ne fal, dan kuwa ban tsammaci zata iya barci ba, mafi yawa butulcin mace ke kaita wuta, abin da aka jima ana rokon ya tabbata ne, ya zo kuma sai a bude shafin iyashege, har da kuka kala kala tamkar wata yar yarinya alhalin gyara da kwalliya ne kawai domin ana kallon Jawad za'a gane ta tsufa".

Wani irin daskarewa Sa'adah ta yi, wato Mk da rashin mutunci ya zo, ta tabbatar da hakan tunda a gaban Baffa ma ya yi mata diban karan mahaukaciya, amma ba laifinsa bane, Baffa ne ya bada ita, dama kuma ance naka ne yake bada kai.

Duk yadda ta so shanye maganar Mk kasawa ta yi, ta yi jarumtar shanye kukan ta ce "duk tsufana dai ka girme ni, kuma ina rokonka ka koma ka fadawa wadda suka yi maka dolen aurena! na ce bana sonka, bana sha'awar zama da kai, domin wadda ya soni ina budurwa, yanzuma da na tsufa son nawa ya nan a tare da shi saboda ba sha'awata yake yi ba, idan kuma na so ma saurayi zan aura wadda ni zan cire masa samartakarsa fiye da yadda na ta'ba cirewa wasu".

Ai bata karasa ba, ya shammaceta ya wawurota ya kama bakinta ya murde da karfin gaske, dan kansa ya saketa bayan ya tabbatar ta ji a jikinta. Jikinsa na rawa ya ce "wallahi idan baki kiyaye harshen ki a gabana ba, zaki sha wahala ai yanzu ke ba yarinya karama bace da zaki dinga mini kaifin harshe".

Mahmoud kuwa da ya lura da abin da Mk yake yi ya kasa juyowa balle ya bude baki yayi magana saboda tamkar ya fashe da kuka haka yake ji.

Kuka sosai Sa'adah take tana fadin idan yafi karfinta ai bai fi karfin ubangiji ba, ya fa'da mata bakar magana, dan ta rama shine zai mata wannan wulakancin?

Har suka iso layin gidan Sumayya kuka sosai take yi, yayin da Mk ya biris tamkar bai ji ta ba, wani wula'kanci da Mahmoud ya yi mata, maimakon ya isa gidan sai ya samu gefe ya yi perking ya kunna musu a.c ya fice ya barsu, a kokarinsa na su dan sami daidaito shima kuma ya fita ya shaki isakar da zai dan samu sukunin zuciyarsa, da gaske da son Iyah zai mutu a ransa, wannan na cikin kaddararsa rashin cikar buri.

Tsawon mintina Sa'a na kuka sosai, Mk da ya tabbatar ta yi shi ba ka'dan ba, ya santa da son a rarrasheta.

Dan haka ya matsa sosai daga jikinta, ya yi gyaran murya ya ce " kukan ya isa haka My first love".

Wani azabben kishi ya duro mata na ba zata, ta sake karfin kukanta tare da cewa "karka kuma cemin first love dinka, domin ni ba ita bace, kaima kasan ba ni bace. First love dinka tana can tana jiranka wacce ba zata tsufa ba tunda bata da kamar Jawad, Ni barni a makiyarka domin bansan komai da ka mini, kuma kake kan yi mini ba Sai kiyayyya da zalunci hadi da wulakanci".

Jikin Mk ya yi sanyi ya ce da bakinki kika ce ban miki komai ba sai kiyayya da zalunci?".

Da azama ta ce "kwarai kuwa! zan kuma rokeka ka koma ka fa'dawa Hajiya da Baffah su janye dolen da suka yi maka, domin ni ba sonka nake yi ba, ko ina sonka to na ha'kura, domin a yanzu sun nuna mini ka fini a gunsu tunda sai yanzu ne zasu maka dole,to ni kuwa ina tabbatar maka na wuce haka wallahi".


Ya ce "Zan so kwarai mu fahimci juna, domin ni ban zo gurinki bisa ra'ayin wani ba, tsokanar ki nake yi, na gane ke ce cikon farin ciki na, ki zo mu rayu tare na sauran shekarun da ubangiji zai ara mana a gaba. kin san ina son ki, kin san ke kika mini laifi, na dauka ko wani kika ji ya ce na zalunce ki, zaki kare ni, amma fa'da mini me nayi miki na zalunci?"

Ta yi shiru tana kuka kasa kasa, tana jin tamkar ta tashi ta yi ta rawa dan ta nunawa duniya irin farin cikin da kasan zuciyar ta yake ciki.

Ta kasa cewa komai, ya nisa ya ce "Yanzu mu ba yara bane Sa'adah, ya kamata mu bar komai mu manta komai, mu gina sabuwar rayuwar da babu gillin bacin rai a ciki, ubangiji shine shaidata ba komai a zuciyata na yafe miki, na kuma manta komai".

"Kema ki daure ki manta duk wani zaluncin da kike ganin na yi miki, ina tsananin son na rayu da ke my Sa'adah".

Da kuka sosai ta ce "Ba haka bane a zuciyarka, kaima kasan ba haka bane, akwai dalilin da ya saka ka yafe mini amma ba dan kana sona ko dan kana son ka rayu da ni ba, daga ranar da ka jefe ni da mafi munin al'amari, a ranar na gane baka sona, wata kake so, kake neman hanyar da zaka rayu da ita, tunda ni amfani na ya kare a gurinka, ka riga ka dandana ni, shiyasa ka 'karanta tunaninka, ka kasa shaidata, ka kasa gane abin da zan yi da wadda ba zan yi ba, dama Kuma ai tun bamu yi aure ba, kake jifana da wannan zargin, yanzu kuma idan na koma maka ai cewa zaka yi har dakinka nake iskancin".


Ta nisa ta sake cewa "na tabbatar ita baka ta'ba dukanta ba, amma ni saboda rashin gata da 'kin da kake mini kanka tsaye kake duka na"

Ta fa'da cikin kuka, maimakon hankalin Mk ya tashi sai ya ji wata irin nutsuwa ta zo masa domin kuwa ya gane da gaske 'Karfi ya ke da ya ce akwai soyayyarsa mai yawa a zuciyarta duk da bakinta na kirarin 'kinsa.

Kishin Farida ke ya galgalata wannan kuwa ba yadda zata yi sai hakuri. Domin ya riga ya kudire ba zai ta'ba barin matsanancin son da yake yiwa Sa'a ya sa ya zalunci Farida ba, ba kuma zai yi kuskuren rabuwa da ita dan zai dawo da tsohuwar matarsa ba.

Bashi da burin auren mata biyu, amma tunda kaddara ta zaba masa to kuwa zai yi iya kokarinsa bai bari soyayyar daya tasa ya danne daya ba.

Cikin lallashi ya ce "sonki ne yake rufe mini ido shiyasa nake dukan ki, Amma ai kinsan iya bakinki nake duka dan shine mai dafi, amma ta yaya zan doki jikin ki alhalin shine abin hutawata. Na rantse miki banda tsoron ubangiji da a motar nan sai na shige, dan ki gane ba karamin kewar ki nake yi ba, har yau din nan 'kwarar Farida nake yi domin idan ina tarawa da ita bana samun nutsuwa, sai na ayyano ke ce a 'kasana amma kina fa'din wai ban miki komai ba sai zalinci".

Kuka sosai Sa'adah ta fashe masa maimakon ta ji da'din kalamansa, ai sai ta ji tamkar cin fuskarta yake yi, yanzu ya murde mata baki Dan ta yi jam'u ta ce wasu samarin alhalin yasan shi ka'dai ta cirewa samartaka. Amma shi yana fa'da mata yana tarawa da wata kansa tsaye.

A cikin kukan ta ce " in Sha Allah Babu sauran zama a tsakanin mu, zan yi dukkan kokarina naga ban jefa kaina a uku ba, a satin nan zan fitar da wadda zan aura, ba zan iya auren ka ba Mukhtar. Ka yiwa Allah ka rabu da ni bana sonka yanzu".

Cikin rashin damuwa ya ce "Ban damu da ki so ni ba, domin son da nake miki ya isa ya ri'ke auren mu, idan kuma kin kafe ba zaki yarda mu yi auren ba, shikenan amma ki sani ban yi al'kawarin zan iya cigaba da jarumtar kawar da ido akan ki ba, kin sanni sarai! Billahillazi ki shirya yin jegon da babu sannu, domin kuwa ciki zan miki, ki haifarwa Innah, kafin a ankara zan sake dirka miki wani sai akaiwa Hajiyar Bichi".

Gaban Sa'a ya buga da karfin gaske, mafarkin Innah ya Fa'do mata, amma sai ta waske ta daure fuska ta ce "saboda kana jin isa, ko dan ka raina gidanmu?"

Ya make kafada ya ce " whatever".

"Dan Allah Mukhtar ka bude min kofa zan fita na gaji da jin Wannan maganganun marasa azanci da kan gado".

Ya yi dariya ya ce "inace dan kin san bana son kina gatsa sunana ne yasa kike ta fa'da, to idan kin so kina iya cewa Mukhtar Kabir Bichi. Zan amsa miki amma nan gaba ka'dan Billahillazi idan akace ki fa'da ba zaki iya ba, zan fa'da miki wallahi ba zan ta bin kanki akan ki dawo gareni ba. Kina so, Ina so to karmu wahalar da juna dan wallahi kika ce zaki ja ni a kasa, ba zan yarda ba, ki rabu da Alh Mamman ban son ganin ki da shi".

Da guntun hawaye ta ce "sannu ubana, to shi nake so, domin kuwa kullum zai ta ganin yarinta ta ne, dama kuma ai tsofaffin sun fi dadiin harka.

Sosai ransa ya baci, a fusace ya dinga kwankwasa gilashin har Mahmoud ya ankra ya iso ya ja motar har kofar gidan Suka kaita, Mahmoud Yana ta faman tsokanarta ya san ai anshirya sai maganar shan biki, duk yadda take jin nauyin 'Karfi yau haushin sa take ji dan haka har ta sauka kala bata ce masa ba.

Da shigarta Sumayya ta dinga bin ba'asin kukan da take yi, bata boye mata ba, ta bata laabrin wula'kancin da Baffa ya janyo mata a wurin Mk na sawa ya kawota.

Ran Sumayya ya baci sosai ta ce "ai sai dai ki dau dangana domin kuwa Baffah burinsa bai wuce ki komawa uban Jawad ba. Duk irin bacin ran da ya jefa mu, duk irin yadda ya jingine ki shekara da shekaru, yanzu kuma dan gata da rashin kishin naka, Dan ya dawo sai ka sake bashi aure?".

Kwalla ta cika idon Sumayya tana ji a ranta Mk bai cancanci auren Iya ba, har ga Allah ta fi sonta da Anwar, amma ko ita ai ba karamin ba'kin cikin Mk ta hadiya ba.

Amma sanin maganar mahaifin su gaba take da kowa, yasa ta hadiye maganganun a zuciyarta, sannan kuma tasan komin borin da Iyah zata yi ba wadda take so irin uban na Jawad.


****


Sai bayan magariba ya isa gidansa, ya iske Farida cikin cotton din doguwar riga kirar Pakistan, kanta dauke da hular da ta dace da rigar, sai kamshi take yi, ta yi kyau sosai, amma saboda ba ita yake son gani a yanzu ba , sai yaji ba haka yake bu'katar ganin kirjinta ba, so yake ya kamo wadda zasu cika masa hannu kamar yadda dazu ya lalubo na Sa'a da nufin zai kamo bakinta.

Ya zauna a kujera ta tashi ta kawo masa ruwa da lemon coke, da cake da ta yi a yammacin yau.

Yana zaune ya rike kansa alamun yana cikin rashin sukuni.

A hankali ta ce "halan baka jin da'di ne?"

Dai-dai lokacin sai ya dinga jin muryar Sa'a na masa kuwwa tana fadin Alh Mamman take so, ai tsofaffi sun fi dadin harka.

A fusace ya mike ya ce mata "A a asibiti ne a kaina ban son katsalandan wallahi". Sannan ya wuce ya haye sama.

Jikin Farida ya yi mugun sanyi, ta zauna tana ambaton Allah.

Ta jima tana nazarin me ya same shi, kaso mafi yawa tafi zaton Sa'adah ce ta zaunguro shi, kishi ya kamata sosai, domin ta lura duk sadda ta ganshi a burkice to ba shakka itace ta birkita mata miji.

Haka ta yi ha'kuri ta kwashi abincin ta bishi da shi, abin mamaki kuma sai ya rungumeta yana fa'din ta kara hakuri da shi, Yana cikin wani irin al'amari ne da yake neman fin karfinsa Dan Allah ta kara hakuri, ta kuma yi masa uzziri.

Matsananciyar sha'awar Sa'a da ya taho da ita tasa ya kasa fita sallar isha, domin akan Farida ya sauketa, sai da suka samu nutsuwa, suka yi wanka sannan suka yi jam'i tare.




🌺 *HALIN YAU*! 🌺

NA

*SURAYYA DAHIRU*.

•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```

```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________

https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/



*_Doka mai lamba ta 68 ta nuna cewa satar fasaha babban laifi ne da yake dai satar Dukiya._*

_*A guji taba wannan labarin ba tare da izinin mai Hakkin mallaka ba.*_


*Wannan shafin Tukuici ne ga*
*Amina Mukhtar Nashe*
*Bisa yaddda kike kaunar labarin, ki yi yadda so da shafin, Allah ya raya zuri'a*


*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*


93-95.


Ana idar da Sallar isha Baffa bai tsaya a shagonsa ba, saboda yadda ya ke zumudin tattauna al'amarin da Mk ya zo masa da shi a yammacin yau, dan haka kai-tsaye gida ya dawo. Sai da ya kamallah cin abincin da aka gabatar masa ya wanke hannu da baki.

Ya kalli Inna ya ganta duk a takure tun safe haka ya ke ganinta sukuku.
Cike da kulawa ya ce "me yake damun ki ne Salamatu?"

A sanyaye ta ce "Ba komai jikin ne nake jinsa ba tsanani, amma lafiya ta kalau".

Nan kuwa mafarkin da ta yi ne ya saukar mata da rashin walwala.

"Allah ya rufa asiri" Baffa ya fa'da yana kallonta, ta amsa da "ameen a takaice.

"Ina tafe da albishir mai dadi wadda na tabbatar zai tsananta jikin nan naki saboda tsananin karfin farin-cikin da zai saukar Miki a

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login