Showing 18001 words to 21000 words out of 186291 words
masu 'kumbar susa ne, itace kadai yar talaka, ko Halima da ba wani kudi ke gare suba, sun wuce matsayin su Sa'adatu, tunda Baban ta ma, aikaci ne a ma'aikatar Revenue yayin da mahaifiyar ta take principal a wata makarantar 'yan mata ta gwamnatin jaha(GGC).
Ita Sa'adatu kawai kwalliya da gayu ne ya janyo mata 'kawaye tunda tana samun abubuwa masu tsada daga yar uwar ta Sumayya.
Tunda suka hada group basu cika mai da hankali kan karatun su ba, illa kwalliya da kuma soyayya tunda kowa ya san FGC KANO co-education ake yi, ma'ana makarantar maza da mata ne a ha'de.
Dukkan su suna da samari a ajin, inka dauke Halima da ta ce ta fi 'karfin soyayya da yara 'kananu, kasancewar tana da saurayi na gaske a gida, wadda ya kasance 'Dan 'kawar maman ta ne.
Khalil Ibrahim na cikin wadda su ke son Sa'adatu Bashir, mahaifinsa ne kwamishinan ilimi na Kano a wanccan lokacin, ita ma kuma ya fi kwanta ma ta a rai, dan haka tana kula shi, dukkan kudaden shi na kashewa a makaranta a kanta ya ke 'karewa.
Wani lokacin ma har fakar idon mahaifiyar shi ya ke ya debo mata kudi kasancewar ta shahararriyar yar kasuwa domin Dubai take fita ta shigo da kayayyakin mata na alfarma, wani lokacin har da Abaya da lace yake daukowa dan ya bawa Sa'a🤔
Suna da 'kokari amma da yake basu mai da hankali kan karatun ba sai suka sha mugun kaye.
Halima da ta kasance ogar su saboda duk tafi su 'kokari ta kuma fi su izza da buri, ita ce kawai ta yi ta shida, amma kowacce a cikinsu ta wuce ta ashirin.
Sa'adatu ita ce kashin baya ta kai ta talatin tunda duk sun fita background din makaranta mai kyau.
Dukkan su jikin su yayi sanyi da ganin sakamakon su, amma Sa'adatu ba ta wani damu ba, tunda dai ta san daga Inna har Baffa sun san tana da 'ko'kari a makarantar da ta baro. zai yi wahalar gaske ma a wani tuhume ta in dai ba Sumayya ce ta zo garin ba.
A cikin wannan yanayin suka kammala SS1, suka shiga aji biyar, budurci sosai, ya bayyana a jikinsu, duk wadda ke FGC KANO ya san da zaman 4stars.
Barin Sa'adatu Gogel, ba wai kyau ta fi su ba, a a kawai ita ma'abociyar kwalliya ce kusan kowanne term sai tasan yadda ta yi, tsakanin 'karya da gaskiya an sabun ta mata uniform, sannan ko mai na ta mai tsada ne tunda ga kan sandal, da school bag, Sumayya ta tsaya ma ta a wannan bangaren, duk kuwa da tana mamakin yadda kowanne hutu sai ta canja komai. Hakan yasa ta saje cikin Ya'yan ma su wadata har ma ta fi su daukar ido, mussaman saboda 'kirar jikin ta.
Zangon karatu na biyu, a aji biyar din su, a ka turo sabbin 'yan hidimar 'kasa (COPPERS)
Cikin su har da Mukhtar Kabir Bichi (MK Bichi).
[5/19, 18:52] +234 806 791 2288: 🌺 *HALIN YAU*! 🌺
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```
```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________
https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•
*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*.
21_22.
Ranar da ya fara shiga ajin su a matsayin malamin harshen turanci(English language), ba abin da ya musu illah introduction, wato gabatar da kai,
ya sanar musu zai koyar dasu harshen turanci.
Bayan sun masa barka da zuwa, sai ya bu'kaci da kowannen su zai tashi ya gabatar da kan shi, as he did.
Sa'adatu da hankalin ta ya yi nisa wurin rubutawa Khalil Ibrahim reply din wasi'kar da ya mata na zai je School shop mai ta ke son ci?.
Ba ta san har anzo kan ta ba, sai da Halima tace "Gogel"!
Sannan ta yi firgit ta mi'ke, ba tare da ta rufe takardar da ta ke rubuta reply din ba, cike da yanga da iyayyi tace ,"I am Sa'adatu Bashir Gogel" daidai lokacin ya 'karaso jikin desk din na ta,
Yasa hannu ya na nazarin rubutun da ya 'dauke mata hankali, baice uffan ba ya dauki takarda ya zira a aljihun sa.
Wucewa ya yi yana fadin "next"
har aka kammala ya cinye period dinshi ya fice tare da takardar.
Takaici ya kama ta, ta fara tunanin mai ta rubuta ne?
_Nagode da kulawa Khalil komai ka ga ni indai ya burgeka, ni ma zai burgeni, Sa'a luvs you_.
Abin da ta rubuta kenan, haka kawai ta ji takaicin wannan Malamin da ya kira kanshi Mukhtar ya kama ta, Ina ruwan shi da ita daga zuwan shi?
Washa gari da ya shiga, karatu sosai ya zazzaga musu cikin turancin da ya kama bakin shi tamkar a 'kasar ingila ya girma.
Ya yi tambayar an fahimta ko da akwai mai tambaya?
Serious student din cikin su ne, su ka shiga tambayar abin da basu fahimta ba, shi kuma ya sake bayani a hankali dalla dalla, har kowa ya ce ya fahimta, sai yace zai yi tambaya.
Ba zato yayi pointing Sa'adatu Bashir ta tashi ta yi masa bayanin yadda ta fahimci topic din da ya gama bayanin sa.
Nan da nan taji ta muzan ta, saboda ba wani fahimta ta yi sosai ba, ta mi'ke ta na rarraba ido ta kasa furta kalma ko guda cikin tambayoyin da ya ke mata, da 'kyar tace "ban gane explanation din ba dama"
Ido ya zuba ma ta yace
"We're not talking in Hausa but we're in English"
kunya ta kama ta, wato har ya gane ba ta iya mayar da magana da turanci? ya sake cewa "I ask all of you who didn't understand, but you mutter"!
Ita dai ba baki, sai ido tana jin wata kunya na kama ta. ya dade yana nazarin ta, sannan yace ta zauna ya sake bayani sosai, a lokacin kuma ta mai da hankali ta na sauraro tunda tana jin maganar, wurin mayar wa ne ke mata tasga'do.
Cikin 'kankanin lokaci ya fahimci ita da 'yan group din su, ba abin da suka sa gaba irin kwalliya da soyayya, mussaman idan class ba teacher to hirar kenan.
Transfer ta baza ta ce ta sami malaman makarantar, ciki har da class master din B class, na ss2 ajin su Sa'adatu, nan take kuma akasa Mukhtar Kabir Bichi a mastayin Class master din nasu.
Wannan damar da yasa mu ne ya 'kudure a ran shi sai ya canja wa'dannan daliban, abu na farko da ya yi musu ya rarraba musu gurin zama ya cillasu ta yadda sai dai hange a tsakanin su.
Haka kawai ya ji duk yafi jin haushin Sa'adatu saboda yadda ya lura wadda ta hada kai dasu din sun fita dama, kullum sai ya ga an kawo su a motoci masu kyau, an kuma zo an dauke su, sa'banin ita da ta ke zuwa da kanta cikin adaidaita sahu ko mashin,'kawarta da ya ke ganin suna zuwa tare Zainab Ma'aji sam ba halinsu 'daya ba, ba ta da hayaniya ta na kuma maida hankali wurin karatu duk da ita tana c class, ajin commercial.
Amma yayi nazarin sa ya gane buri da ra'ayin Sa'adatu ya kerewa mu'amala da irin su Zainab.
Saboda haka sai yafi matsa mata, kullum da kalar tambayar da zai mata, wadda kesa ta muzan ta.
Abin da ya lura dashi bawai 'ko'kari ne Sa'adatu ba ta da shi ba, illah mai da hankali ne ba ta yi.
sannan kuma tana da (infiority complex). ma'ana rashin 'kwarin guiwa akan kanka, tunda ya gane tsoron kar a mata dariya yasa ba ta son yin magana da turanci.
Wannan matsin da ya mata sai ya janyo tsanar shi a ranta, ta shiga fargaban zuwan period 'din shi,
a haka har akayi jarrabawar gwaji(Test). ganin a kowanne darasi bata ta'buka ko mai ba sai shiririta, sai ya canja salo ya fara disgata a gaban aji, ta hanyar 'kiran ta da sunaye kala kala, da suke nuni da ba abin da ta sani sai dai ta wanke uniform, ta yi yanga, amma empty brain, har cema ta yake bata dace da wannan makarantar ba.
Sannan kullum cikin bada misali da za'kwa'kuran dalibai masu azama yake, takaicin ta 'daya, yadda kullum misalin sa ba ya wuce da Farida Nasir Torodi , tun fil'azal ita jinin ta bai hadu da Farida ba, duk kuwa da ba ajin su 'daya ba,
Farida a A, science class kenan,
doguwa, siririya sosai, fara 'kal buzaye ne, gashin ta har gadon baya, farkon zuwan ta makaranta har nuna ta ake, na yadda ta ke tuma a cuci a kanta saboda idan ta tufke gashin yake girma, sai a hankali aka gane gashin ta ne.
Mai sanyin hali ce ko kadan ba ta da kwarafniya, bata kuma harkar 'kawaye.
'Kawar ta 'daya wadda kullum zaka gansu tare Ru'kayya mustapha.
Ga ilimi kamar me, dan kuwa tana cikin 'yan gaba gaba na 'dalibai masu haza'ka a duk fadin makarantar.
Sannan iyayen ta ma su wadata ne, domin mahaifin ta ambasadan Niger ne a Nigeria.
Wadannan abubuwan da Farida ta hada sai wasu cikin dalibai su ke mata kallon mai girman kai, da 'daukar ita wata ce yasa take ganin ta wuce kula su, shiyasa suma basa wani harka da ita ba ta da farin jini a tsakanin set dinta. barin ma da 4stars da suke ganin sai dai ta nuna musu kyan fuska amma ba dai na jiki ba😀.
Yawan misalin da yake yi da Farida ya 'kara tsanar ta a zuciyar Sa'adatu.
Cikin abubuwan da ba zata manta suba indan har za ta tuna rayuwar ta a FGC KANO, shine ranar da ya musu dictation wato yana fa'da suna rubutawa, ita kuma slow writer ce, kafin ta kammala rubuta wata kalmar, ya fadi ta gaba, kan dole ta ha'kura da bin, ashe yana lura da ita.
Sai da ya gama ta ji ya kira sunanta"Sa'adatu Bashir where's your note?"
Cikin daburcewa da tsoron yadda zai kunyata ta, murya na rawa ta tattaro kalaman da zai fahimce ta a gajarce ta ce
"My pen stop"
kafin ya yi magana anyi attishawa mai 'karfin gaske wadda ta iya shege ce, ba kowa bane illah Fahad Auwal! wadda shima haushin yadda ta za'bi Khalil ta barshi ne yasa yake jin da'din dizgin da ake mata.
Hannu ya mi'ka yana cewa "let me see"
zuciyarta ta buga amma hakan nan ta mi'ka mishi biron, ya duba ya ga lafiyar biro 'kalau ya watsa mata kallo tare da cewa "out of my class! I am tied of your manners" ta mi'ke sai kuma ta tsaya tace "Am sorry" cikin tsawa yace "don't sorry me, say sorry to ur parents who are keep westing their money".
Jin haka yasa ta fita, hawaye ya cika idonta, a baranda ta tsaya amma sai ya le'ka yace mata "on your kneels" kuka sosai ya kwace mata .
A ranta ta na tambayar kanta me ta mishi ne ya ke wula'kanta ta? mai yasa ya matsa mata? saboda ba ta da 'kokari ne dalilin? ta ke ta ji in dai 'ko'kari zai sa ta tsira da mutunci a idon wannan mutumin da ya yankewa tozarci cibiya to kuwa za ta nemo shi a ko'ina yake.
Sai da ya kammala darasinsa sannan ya fito ya kalleta yace "I want you to borrow your boyfriend's note, and copy what you can't write by urself, if not u will be in.." ya girgiza kan shi ba tare da ya fadi mai zai biyo baya ba .
Ya wuce ta yana sa ke fadin "useless girl, you can go back to ur class".
Tsawon lokaci ta shafe a gun tana kuka tsabar ba'kin ciki zuciyarta Kamar ta fashe, har sai da ta hango Mr uche's wadda ya ke 'daukan su darasin tsumi da tanadi(economics). sannan ta mik'e ta na kar ka'de jikin ta, ta shige ajin ta na ganin wa'danda dama su na jin haushin su, ita da 'yan group din su, su na bin ta da wani irin kallo, mai kama da madallah.
AL'KALAMIN
SURAYYA DAHIRU
✍️✍️.
[5/20, 16:04] +234 806 791 2288: 🌺 *HALIN YAU*! 🌺
•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```
```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________
https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•
*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*.
*Fatan alheri ga marubuciya*
*Zainab Ilyas Mazawaje*.
23_24.
Tsananin matsin da Uncle Mukhtar ya mata yasa ta zama shiru shiru, ta matu'kar rage kaudi da iyayyi.
Kullum tana ri'ke da littafan koyon turanci, ire-iren su Teach ur self.
Ta sake mannewa Safina Bunkure. kasancewar Safeena girman Lagos ce, mafi yawan maganarta turanci ne, dan haka ba ta yarda su yi magana da hausa tare da safina, itama kuma Safina ba ta gajiya da gyara mata a inda ta ji ta yi kuskure.
Ba'a dauki lokaci mai tsayi ba,ta fara rage tsoron kar ta yi turanci a mata dariya, ganin ta na iya mayar da magana cikin harshen da ke mata nauyi, sai kuma ta mai da hankali akan ragowan darussan gaba 'daya.
Ta matu'kar rage shiririta, yanga, da hirar soyayya, da duk wata sharholiyar da su ke, abu 'daya ne ba ta bari ba, kwalliya, wadda wannan kam a jinin ta ne.
Su Halima cewa su ke basu ga Malamin da zai uzzura mu su, babu dalili basu yi maganin sa ba.
Ita ko tsaki take ja a fili, ta yi shiru.
A zuciyarta ko cewa take ai ku ya ga kun iya turanci, kuma yana ganin yadda ake zuwa 'daukan ku a motoci na garari,
ni kuwa ya ga ba ko 'daya, ba dole kowacce shara ya debo ya juye a kaina ba.
Tabbas tana takaicin yadda ita kadai ya ke gallazawa.
Shikuma ganin yadda ta yi laushi ta kuma maida hankali kan karatun ta, sai ya sassauta mata, duk kuwa da zai yi wahalar gaske ya yi darasi bai ce ta tashi tayi bayanin yadda ta fahimci darasin ba, kawai dai kyara da disgin ya rage.
A haka har suka yi jarrabawar mock wadda duk 'dalibi ya ke tsoro da fargaban kar ya fa'di.
Ana yin hutu da kwana biyu mijin Sumayya ya turo takanas a dauki kannen shi 'yan mata guda biyu da yar autar dakin su, da kuma wadda suka hada uba yar amaryar Baban su, sai ya ro'ki Baffah! akan ya basu Sa'adah ta yi musu hutu tare da 'kannen shi. ba musu ya amince, har gida suka zo suka dauke ta, sannan suka dauki hanyar jos kwata, ta yamma da Bauchi😀.
Wannan hutun yana cikin abubuwan da Sa'a bata Mantawa da shi, domin kuwa ta yi matu'kar jin dadin zama da 'kannen Idris yadda suka kasance yara kamammu, marasa hayaniya amma kuma yan kwalliya ne na sosai, shiyasa abotar su ta yi da'di.
Sumayya kuwa ba ta matsa musu, hatta abinci wadda suke so shi zata ce su yi, mai gidan kuma kusan kullum sai yasa direbansu ya zaga dasu, sunga gari, da wuraren sha'katawa , sannan kuma duk fita sai ya basu kudin kashewa, wadda ba abin da suke siya sai kayan kwalliya ko dai abin da ya shafi sutura.
Ba abin da ya dame su illah tunanin mock exam din da suke fargaban fitowar ta, tunda dukkan su set daya suke Amma makaranta daban daban.
Haka suka 'kare hutunsu cikin jin Dadi da mutunta juna, da kanshi Idris ya kawo su har gida tare da kayan tsarabar ni'ki ni'ki, barin ma dankalin turawa da dangin su cabbage da Kara's, harta atile kamar wadda za'a ci a tsawon wata.
Baffa da Inna sai godiya suke,tare da sake godiya ga Allah, na yadda Sumayya ta sami mijin daya San alheri yake kuma rama alherin da kyautatawa da mutunci.
Barinma idan ta zauna tana bawa Inna labarin daular da Anti Sumayya ke ciki, sai dai ta yi murmushi mai nuna yadda zuciyar ta ke cikin farin ciki.
Ba zata yi magana ba sai dai ta bige da cewa kema Allah ya ba ki mijin rufin asiri, yasa ki dace kamar na yar'uwarki.
Ita kuwa kai tsaye take cewa
"Amma fa Inna gaskiya ni bana son irin tsarinsa, ace mutum duk inda matarka zata fita kace sai ta zumbula hijabi har 'kasa, kuma wai dole sai ansa safa? ko 'dan wanne mazahaba ne?"
Cikin mamaki Innar ta zuba mata ido, tare da tafa hannu tana sallallami tace
"ke kuwa Iyah wannan tsarin da yake yi na martaba shari'a ne bai Miki ba?
Na mijin kwarai shi ke kishin matarsa, ya 'dora ta akan ka'idojin shari'a, wadda zasu gudu tare su kuma tsira tare!
"Daular da ya sanyata a ciki ta burge ki, kina kuma fatan ki samu irinta, amma abin mamaki, hijabin da Ubangiji ne yace a saka shine bai miki ba?
Anya Iyah, Baffan ku bai yi kuskuren barinki shiga wannan makarantar da ta ke sake girmama burinki ba?"
Da sauri tace
"Haba mana Inna! ni fa ba cewa nayi kar asa hijabi ba, gani na yi tana da tsala tsala dogayen riguna tunda ga kan yan 'kasashen Oman, Qatar, Saudi, Dubai, masu tsadar gaske masu kauri, amma wai dan 'kauyanci kuma sai akawo hijabi a maka, bayan su karan kansu hijaban ne".
Ta fa'da tana fashe wa da dariya.
Allah ya shirye ki kawai, Inna ta fada tare da mi'kewa ta yi tsakar gida, tana fadin wannan dogon burin na ki yana ban mamaki Iyah.
Ban da 'karya da fariya, da kai kanka inda Allah bai kai ka ba, gidan uban wa kika san 'kasashen da suke sarrafa riguna masu tsada?
Naga dai ke kam baki da halin samun su, ban da Allah ya miki gata ya baki yar'uwa mai halin girma tana baki kuncen su, wasu ma ko saka su bata yi, ta ke baki, amma har ki zauna ki karkace baki kina min lissafin inda ake sarrafa su?".
Ta cika fam saura 'kiris ta fashe cikin turo baki tace
"Amma Inna abin har da gori?"
Da sauri tace
"Eh dole na goranta miki, dan na ga nema kike ki manta cewa ke'din ba yar kowa bace, face malam Basiru mai 'yar tireda😀wadda ko hanyar inda jirgi ya ke sauka ba ki ta'ba zuwa ba,
Amma kina bada labarin 'kasashen duniya, wallahi Iyah ki canja wadannan halayen da nake ganin kina sake arowa kina