Showing 174001 words to 177000 words out of 186291 words

Chapter 59 - Halin Yau By Surayyah Dee

18 Dec 2025

9721

ta ce "Inna zanje asibiti, daga nan kuma zan wuce gidan Maman Khalifa".

Ido Innah ta bita da shi tabbas tana ganin kasala a tare da ita, kuma ba kasafai take cin abinci ba.

Ta ce "wanne asibitin zaki je?"
"Ban san wadda zai kai ni ba, Ni ba dan ya dage bama, da ba wani asibitin da zani, na san zazzabin cizon sauro ne".

"To sai kin dawo, amma kar ki kwana gidan su Khalifa, Baffan ku baya gari, gara ki dawo mu kwana tare".

Sa'adah ta amsa da cewa "To Innah".

Innah ta sake cewa "ki kula da kanki, ki lalla'ba shi, kar ki yi abin da zai ja hankalinsa akan ki, har sai anyi tariya. Ni ba gaskiya ba zaki mini wata uku a gidan nan da auren ki ba, wanan watan da wani watan ya isa, koma kudin bai isa ba, kina dakinki sai ki dinga siyan abin da kike so, tunda dai ai ansan mu masu karamin karfi ne".

A sanyaye Sa'a ta ce "Hakane Innah! Ni idan kin ce ma a wannan watan na tare zan yi biyayya ba dan Ina so ba, sai dan na nuna miki na fi girmama ra'ayin ki akan nawa".

Sosai Innah ta zuba mata ido tana son ta gasgata maganar Iyah, amma bata san meyasa take ganin tamkar akwai wani abu da yasa ta sauko haka da wuri akan tariyar ba.

Ta tafi, Inna ta bita da addu'ar dawowa lafiya.

Suna tafe yana ta yawo da su akan titi, shi kansa tunanin inda zai kaita yake yi.

Can ya kalleta ya ce "wanne asibitin kike zuwa yanzu?"

A hankali ta ce "Ni fa na je asibitin an duba ni, ta butde jakarta ta fito da magungunan da aka bata tana nuna masa.

Ya ce "To sannu My Sa'adah".

"Yanzu bari ki raka ni unguwa"

Basu zame ko ina ba sai gidansa na rijiyar zaki.



*Ina ta shan korafi daga makaranta cewar yanzu yanga nake yi, ko kadan ba wannan maganar, a farkon fara posting Ina da pages masu yawa a 'kasa, a yanzu kuma babu, sai na yi typing kafin na turo, kowa ya san akwai hidimomi irin na yau da gobe akan kowanne bawa.*

*Ni Kuma har da ciwon idon da yake sani rauni a typing din, Ina fatan za'a yi hakuri, saura kiris ma mu kammala, ban yi tsammani labarin zai yi tsayi haka ba*

*Zan sanar da cewa ba kullum zaku ga update ba, amma ba zai dinga daukan lokaci ba*
*Na gode sosai da yabawar ku kan rubutuna*.







Surayya Dahiru
✍️✍️.




*HALIN YAU*!

*NA*

*SURAYYA DAHIRU*.


*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```

```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________

https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/


*TAIMIYYAH*❤️

Ina kuke ne masoya kuma makaranta littafan Hausa,me kuke jira baku afka cikin wannan tafiya ba? ko kuna da labarin cewa shahararriyar marubuciyan wato Ayshat Ɗansabo Lemu,marubuciyan👇🏻

*LAIFIN ƁOYE*
*HAMAL*
*HURAYYAH*
*BURIN ZUCIYA*
*ƘALUBALE*
*NAILAH*
*INA DA HUJJA*

ta sake yinƙurawa domin tazo muku da zazzafan labarin ta me suna asama,domin faɗakar da ku da kuma nishaɗantar da ku,haɗi da koyar da ku dibarun girkunan zamani da gwangwaje ku da salon soyayya me tsayawa a zuci,duk acikin wannan shahararran labarin nata me suna *TAIMIYYAH!* Labarin da yazo da wani irin salo me cike da ban tausayi do motsa zuciyan me karatu,duka wannan zai zo muku akan farashi me sauƙi,da kuɗin ki 500 kacal zaki mallaki naki don gujewa shiga hakkin marubuciyan,zaku biya kuɗinku ta wannan asusun kamar haka👇🏻

*0504192664 Aisha Ibrahim Dansabo GTbank.Sai ku aiko da shaidan biyanku ta wannan layin 08167768704.*

*Masu turo katin waya zaku turo katin MTN ta wannan line ɗin 08167768704.*

Kada ku bari abaku labari domin wannan karan salon na daban ne,tuna da sunan *TAIMIYYAH!* sai ku garzayo don ji wacece TAIMIYYAN ya rayuwanta zai kasance alhali ta kasance gurguwa!


Masu buƙatan a tallata muku jahar ku a wannan daddaɗan labari zaku tuntuɓi marubuciyan ta wannan layin 08167768704.


Share it ga wanda taci karo da wannan tallan,tayi sharing ɗinsa fisabilillah! 👏🏻

THANK U ❤️


*GAISUWAR GIRMA GA*
*IYAYENA! KUMA MANYA MATA!*
*HAJ HAMZIYA ALI(MRS BELLO BAFFAH MAITAMA)*
*AUNTY ZAHRAH IBRAHIM*
*AUNTY KHADIJA ABDULLAHI(MRS IBRAHIM BABA)*
*HAJIYA MAIJIDDA TA GWARAM(MRS ALI BUKAR MAKO'DA)*
*AUNTY AISHA HAMISU KANO(MRS ABDULAZIZ SHEHU)*
*AUNTY AISHA SANI GWARAM*
*AUNTY SA'ADATU SANI GWARAM*
*AUNTY SHEMA'U SANI GWARAM*
*AUNTY AMINA SANI GWARAM*
*AUNTY ZARA'U BILYAMINU USMAN HADEJIA*
*AUNTY A'I GARBA*
*AUNTY SHAMSIYYA USAINI*
*AUNTY ZAINAB SIBA*
*AUNTY FIDDAUSI 'DAYYABU TAURA*
*AUNTY WASILA MUHAMMAD* *(AMINYAR AUNTINA TA KAINA RABI SANI)*
*FATAN ALHERI ALLAH YA KARA MUKU LAFIYA DA NISAN KWANA MAI ALBARKA*.


*FATAN ALHERI GA AISHA JOS MARUBUCIYAR TA CUCE NI*.
*ALLAH YA 'KARA BASIRA*


*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*


111-112.


Katon gida ne mai dauke da babbar haraba, ga wasu irin gini flat guda biyu, a tsakiyar filin.

Sai daga can kusa da karshe kuma wani flat din mai kama da boys quarters.

Shuke shuken fulawowiyi sun 'kawata harabar, sosai gidan ya burgeta, saboda tsarin gini ne na kasashen ketare inda zaka samu yalwar iska(ventilation).

A jere suke da juna, sai dai akwai Yar tazara a tsakanin gidajen.

Kai tsaye ya nufi wadda yafi kusa da 'bangaren dama.

Ya fito da mukalli a aljihunsa ya bu'de babbar kofar, tunda akwai karamar kofa wadda 'karamin falo ne da toilet a ciki saboda zama da abokansa ko ba'kinsa maza. katon falo ne a farko mai dauke da wurin cin abinci da kicin sito, akwai kofar a kicin din da zaka iya shigowa daga waje. Sai ta gefe kuma dakunan barci ne suma manya guda biyu kowanne da bandakinsa a ciki.

Har ilah yau daga can karshe akwai wata kofa idan ka bu'de dogon corridor zaka ga ni mai dauke da wasu 'dakuna guda biyu, da bandakinsu.

Ta jikin wannan koridon akawai kofar da zaka iya fita waje ba sai ka shigo falon ba.

Sosai tsarin ya burge Sa'a marbles din da aka shimfida a ko ina, da kuma girman falon da dakunan ya sake sawa ginin ya zama na mussaman.

Sannan ko ina ansaka labule masu tsadar gaske.

Cikin dakin guda da suka yada zango har da madaidaicin karfet a shimfide.

Suka a zuana akan karfet din.
Ya ce" ina fatan ya yi miki?"

A hankali ta ce "ko gidan da muka fara rayuwa ka kai ni, ya yi mini sosai, bare wannan".

Ya tsura mata ido yana gasgata ta domin yanzu babu dogon buri a tare da ita, amma da yake tana samun hanyoyin samun ku'di bata yiwa kanta kwangen sutura da kayan kwalliya na alfarma. Son ta yi gayu a jininta ne ba wai 'karya ko fariya ba ne.

Ya matsa sosai kusa da ita, yana shakar 'kamshinta, ya na kuma yi mata wani irin kallo mai tsanani.

Ta sunkuyar da kanta 'kasa tana Jin kallon har a zuciyarta.

Ya nisa ya ce "yunwa kike ji ko?"

Da sauri ta 'daga masa kai.

"Shine kuma ba zaki fa'da mini ba? Ai da na tsaya a hanya na siyo miki".

Bata ce komai ba.

"To me zaki ci?".

A hankali ta ce gasheshshen nama da yourgt mai sanyi".

A zuciyarsa sai ayyana irin haka ta yi a cikin Jawad, ba rashin lafiya, sai kasala da rashin cin abinci sai kayan kwadayi, da barci.

Ya mike da sauri ya ce "zamu je mu siyo, ko na je na dawo?"

"Je ka dawo! na gaji".

Bai 'dauki lokaci mai yawa ba, ya dawo da dukkan abin da take bu'kata, ya tarar da ita, tana sharar barci hankali kwance.

Bai tashe ta ba, ya ajiye ledojin ya shiga bayi ya 'doro alwallah ganin 12:45 pm ta yi, yanzu za'a fara 'kiran sallah.

Ai kuwa yana fitowa ya jiyo Kiran sallah, sai da ya yi nafila, sannan ya fice zuwa masallaci.

'Karar rufe kofar ya tasheta, a hankali ta yun'kura ta zauna da salati a bakinta.
Kamshin nama ya bugeta, da sauri ta mike ta wanko bakinta ta dawo ta fara cin naman nan a hanzarce saboda yadda ta tara yunwa. Bata son cin abinci, sannan bata iya siyan abin da take so dan kar ta janyo hankalin Innah. Ko a gidan Sumayya bata iya cewa ga abin da take sha'awa shiyasa take zaman yunwa, sai ta ga zata galabaita ne take zuwa gidan Zainab, ko ta siya ta samu inda zata buya ta ci.

Duk yawan nama da gurasar da suke na'de a poil paper 'dan ka'dan ta rage, ta bude dadda'dan yougurt ta fara sha tana jin sanyinsa har cikinta.

Sai da ta huta, sannan ta yi gyatsa ta mike ta 'doro alwallah.

Ta kusa idarwa ya shigo. Ya zauna yana jan ledar gabansa dan shima ya ci, mamaki ya matu'kar kama shi, saboda ganin wanda ta rage.

Ya karasa cinyewa ya bude yoghurt ya sha.

Bata yi masa magana ba, ta sa hannu ta dauko robar ruwa ta bude ta kai bakinta.

Sai da ya kammala ya matsa kusa da ita sosai, ya ru'ko ta. Yana cewa "zo ki ji wata magana, na sani ba iya yunwar nama kike ji ba".

Ta fara ture shi tana cewa "Ni wallahi iyakacin yunwar kenan, kuma na koshi sosai".

"To ai ni ban koshi ba, tunda dai baki rage mini na kirki ba".

Ta 'ki tsayawa, shi kuma ya'ki sakinta, ganin da ya yi da gaske ba amincewar zata yi da shi cikin kwanciyar hankali ba, sai ya saketa.

Ya koma gefe ya na jin bacin rai sosai.
Jikinta ya yi sanyi, amma bata san me yasa take jin tsananin bacin rai idan ya nemi kusantarta ba.

Tsawon lokaci suna zaune ba um, ba um um, a tsakanin su.

Ta saci kallonsa ta ga yadda yake cikin fishi sosai, ta hadiye maganar da take son amayarwa.

Ya mike yana cewa "Tashi mu tafi"!

Ta 'ki yin ko da motsi, balle ta tashi.

Dan jim ka'dan! Ya nufi hanyar barin dakin yana cewa "ki same ni a mota".

Ta daga murya ta ce "Ba ka ce mini komai ba akan maganar da na yi maka 'dazu, kuma ka ce mu tafi?"

Ya dawo ya tsaya akanta fuska ba walwala ya ce "wacce magana ce? Tuna mini, dan ni na manta".

Takaici ya shaketa, amma hakanan sai ta daure ta ce "Tariyar Mana".

Kai-tsaye ya ce "Ban kammala shiri na ba, ba kuma ku'di a hannu na".

Ta fara kuka tana cewa "Ni ko ba ku'din zan tare, kar ka mini haka, so kake na kunyata?"

"To ki ta kunyata mana! Ina ruwana? idan kuma kina da yadda zaki yi da cikin dan ki tsallake kunyatar sai ki yi".

Ta dago a razane dan ta ga shine yake wannan maganar ko kuwa?. Ai kuwa suka ha'da ido, fuskarsa a matu'kar 'daure.

Ta Sanyaya murya, hawaye na zubo mata, ta ce "Haka ka ce mini?"

Take ya ji tausayinta! Ya zauna ya ce "Haka na fa'da miki Sa'adatu. Hakan kuma shine gaskiyar magana, ba zai yiwu kina wulakanta ni tun yanzu ba, sannan ki yi tunanin zan miki abin da kike so, bakya yarda da ni, na sani ko tariyar aka yi haka zaki cigaba da yi mini, dan haka ki zauna ki haihu a gida. Zuwa lokacin idan kin ji a ranki, kin shirya zama da ni bisa tsarin sharia sai na saka ranar tariyar".

Hawaye ya dinga zubo mata ba kakkautawa, a hankali ta ce "kar ka mini haka dan Allah".

Nan da nan ko ya ci laya da cewa "Wallahi ba zan yi abin da kike so alhalin har yau din nan bani da mutunci a idonki ba, inace dai jikina ne ba kya so ya rabe ki? To ba zan sake ba, zan ta siyo miki nama da yogurt da duk abin da kike son ci, nima kuma in sha Allah ba zaki ji, ko ki ga na mutu ba adalilin ba kya yarda da ni".

Ta dinga kuka sosai, ya dinga jin wani iri, ya sassauta ya ce "daina kukan haka! Ta shi mu tafi"

"Ni ba inda zani sai an tsayar da maganar nan".

"To ai na gama, sai dai tunda ni zan biki dole, sai ki tsara na ki, ki kuma sa ni biyayyar dole".

Ta goge hawayen ta ce "Na yarda ni zan bika".

Ya mi'ke ya ce "To tashi mu tafi, tunda Ni na zartar da nawa hukuncin, ba kuma zan canja ba, sai na tabbatar da gaske kin daina mini wulakanci".

Da rawar murya ta ce "Ai yanzu ma na yarda! Ba zan sake tureka ba".

Da'di ya yi matu'kar kamashi, dama abin da yake so kenan.
Da rawar jiki ya isa ya rungumeta.

Ya dinga jifa da Hijabinta da komai ma, haka ya dauki lokaci yana abin da ya ga dama da ita.
Yayin da itakuma ta ke share hawaye.

Har ya yi wanka ya fito bata bar kuka irin na sharbe ba.

Ya waske ya yi kamar bai gani ba.
Suna tafe a mota da rawar murya ta ce "Yanzu yaushe ne tariyar?"

A gajarce ya ce "sai kin daina mini kukan da babu dalili, sai na gamsu da gaske idan kin tare din zaki barni na dinga samu nutsuwa da ke".

Da kuka ta ce "kawai na gane yawo kake mini da hankali! Dan kasan ka gama da ni, inace yanzun ba abin da baka yi da ni ba, amma yanzu kana wata magana".

"Tabbas na yi, amma mai na tsinta ban da bacin rai, dame kika taimake ni? inace zama kika yi tamkar ruwa, sannan kina ta Kuka".

A matu'kar gajiye ta ce "To ai ba zan sake yi maka kukan ba".

"To zame mini tamkar gawa fa?"

Da sauri ta ce "Na daina".


"To ki bari sai na tabbatar da gaske kin daina din har zuciyarki".

Cikin kwantar da murya ta ce "yaushe to zaka tabbatar din?"

Ya dauke kai ya ce mu barshi nan da wata daya, idan yanayin biyayyar da kike mini ya gamsar da ni, shikenan sai ki tare abin ki".

Da rawar murya ta ce "idan na kara wata Innah zata gane halin da nake ciki".

"To wai ke wannan boye boyen da kike yi na menene? Abin kunya ne, Inace an daura auren?"

"Ni dai bana so a sani ne kawai".

Ya murmusa ya ce "ai dole ki ji kunya, kin gama fadin ba kya sona a gabansu, sai gashi daga dan ta'ba ki ka'dan, kin yi ciki, ai dole ki ji kunya, ina kika kai 'kiyayyar?"

Ta kasa bashi amsa.

To mu barshi sati biyu nan gaba, amma sai na tabbatar fah".

Tunda ga wannan ranar Mk ya mayar da Sa'a tamkar ya tare da ita ne, domin kullum sai ya fita da ita, ya yi abin da zai yi sannan su dawo.

Har satin biyun ta cika amma baice komai ba, a lokacin cikinta yana shirin shiga wata na uku.

Rannan suna gidan da suke yini, zuwansu kenan, ta kalle shi, ta ce na gane so kake dai sai na kunyata dole. Banda haka menene bana yi maka Kullum sai ka fita da ni, amma ka dage akan bana yi maka yadda kake so?
Fa'da mini me zan yi maka kuma?"


Cikin rashin damuwa ya ce "ba Kya mayar mini da martani kamar da can, sannan kullum na kusance ki da kuka ake karewa, ke yarinyace? Sannan ba har zuciyarki kike amincewa ba, kina yarda ne akan dole, sai dan kina son ki tare kar agane kina da ciki.
Abin da baki gane ba, ni ba abin kunya na yi ba, tunda na yi hakuri sai da aka 'daura aure, ke kika ce ba zaki tare ba da bakin ki. Babana ya goya miki baya, yanzu kuma sai ki dame ni da maganar tariya alhalin kin san inda zaki fa'di kin matsu ki tare, asa ni dole, ko bana so".

Ya nisa ya ce "ki kira Baba da bakinki kice zaki tare".

Idonta ya ciko da kwalla ta ce "Kaine zaka kira ka ce ka shawo kaina na amince, idan ya nemi jin ta bakina sai na yi shiru alamun kunya, shikenan sai ya gane ina bu'katar tarewar da gaske".

Ya tsura mata ido ya murmusa ya ce "Sannu Sa'adah! Ke idan kina son abu, kin iya shirya zance".

Daga haka ya janyota jikinsa yana kissing dinta.

Sai dai yau yana kammalawa ta dinga kelaya amai tana kuka.

Sosai ta yi, sai da ta kammala ta koma gefe ta cigaba da kukanta.
Haka Mk ya kwashe Aman nan, ya sa tissue ya goge.

Ya kalleta ya ce "je ki yi wanka".

Bata Musa ba ta mike ta shiga toilet.

Ta fito ta same shi ya yi tagumi da hannuwa biyu.

Ta zauna a sanyaye.


Ya kalleta ya ce "Anya kuwa Sa'adatu kina jin tsoron ubangiji? Anya kuwa baki kafirta ba?"

Da saurinta ta dago ya ce "kwarai kuwa! Na sani kishi ne yake son halaka ki! Amma ki sani ubangiji ne ya halasta, sannan shine ya bada umarnin a auri bibbiyu ko uku ko hudu. Aaya ce sukutum cikin al'kura'ani mai girma.
'Kin amincewa da hukuncin Allah kuwa tamkar ka kafirta ne".

Ya yi shiru yana nazarinta.
Ya nisa ya cigaba da cewa "ina jiye miki kada ki halaka kanki, ki halaka ni, Ina jiye miki tsoron kada na samu aljannah adalilin ba'kin cikin da kike ta 'kunsa mini, ke kuma ki tsince kanki a wuta.
Annabi ya ce akwai mazan da suke rabauta da aljannah adalilin hakuri da taurin kan matayensu da kaifin harshensu.
Ina jiye miki na shiga aljannah, na hadu da Farida ba da ke ba".

Dai-dai nan ta rushe da wani irin kuka, fiye da kukan da ta yi ranar da ya saketa.

Da sauri ya matso ya rungumeta, domin ya tabbatar wannan kukan ba na shagwaba ko iyashege bane, na tsantsar damuwa ne.

Bai hanata ba, ya barta ta yi, iya yinta, ganin yana neman wuce ka'ida ya sanya ya fara lallashinta da gwalagwalan kalmomin da suke nuna kololuwar matsayinta a zuciyarsa.

Cikin kukan ta ce "Me yasa sai ita zaka aura? Me yasa na shafe shekaru hudu, Ina binka ka mini afuwa ka 'ki, karshe sai ka hukunta ni da auren wadda na tsana, Dan Allah baka ji a zuciyarka ka tozartani ba?"

Da sauri ya ce " Ni ban tozarta ki ba, domin 'auren da na yi 'kaddarata ne, wadda ko muna tare ba zan iya tsallakewa ba.

Ta ture shi ta ce "Ai kuwa zamu rayu a haka cikin damuwa, domin zuciyata ba zata huce ba, har sai ka yarda ka wulakantani, ka mini hukuncin da ya wuce laifina".

Ya sake rungumeta tsantsan tamkar zai mayar da ita cikinsa ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login