Showing 162001 words to 165000 words out of 186291 words

Chapter 55 - Halin Yau By Surayyah Dee

18 Dec 2025

9709

da su, sai sun zayyane mata komai, a hada da sharri ma, daga nan girman ki ya zube a idonta, itama kuma ta sami damar da zata dinga fa'din munanan dabi'un ki".

"Na gode miki Zainab! Na sani ke din mai sona ce ubangiji ya sanya mu cikin masu zumunci dominsa".

Sa'a ta fa'di hakan a sanyaye.

Zainab ta ce "gida zan ajiye ki, ko gidan Anty Sumayya?".

A tunzure ta ce "gidan ubana zaki ajiye Ni, ai Ni da gidanta sai ta neme Ni".

Zainab ta yi shiru! ta san tana tofawa baza su rabu cikin da'din rai ba.
Wasu daga cikin halayyar Sa'a a jinita ne ilimi ko shekaru ba zai sa ta sauya ba, rikici na cikin abin da ba zata daina ba.

A Daren ranar Baba Isa ya dawo asibitin ya fa'dawa Mk ranar juma'ah mai zuwa za'a mayar da aurensa da Sa'adatu, amma ta nemi abarta ta kintsa kafin ayi maganar tariya tunda titsiye ubanta ya yi mata, ba dan tana so ba.
Ya ce " Na kuma yi mata wannan laminin, dan haka ba zata tare ba, sai ta shirya, wannan umarni na ne".

Baban ya nisa ya ce "Soyayya da sanin darajar Dan Adam ne kawai ya sanya Malam Basiru zai sake baka aure a Karo na biyu! Ka sani da ni da mahaifinka ra'ayin mu daya, shawarar mu daya, hakanan neman kudinmu daya, abin da Zan fa'da maka yau, na tabbatar da yana raye a gabansa zan fa'da maka domin ka sani idan ina waje baya ta'ba nuna shine ubanku yana dora ni akan komai nasa matu'kar anan Kano ne, da bashi da dan'uwan jini.
To ka saurare ni da kyau ni na karba maka amanar yarinyar nan, idan har ka bari ta wulakanta ina rantse maka da Allah ni ka wulakanta, na kuma tabbatar idan har ka wulakanta ni, zaka wulakanta Kabiru, hakkin abotarmu ba zai bari ka ga haske ba, ko bayan ba raina, ina maka wasiyya akan yarinyar Malam Basiru domin ni dai banga mai arziki a wannan zamanin irinsa ba, Ubangiji ya bashi wadatar zuciya, ya bashi alheri mai yawa, wadannan kuma sune kololuwar arziki".

Da tsananin farin ciki Mk ya ce "Na ji Baba, in sha Allah ba zan sake kunyata ku ba, komai zata yi zan yi ta ha'kuri, zan kara hakuri akan ha'kuri. Ya sauko ya durkushe a gaban dattijon ya ru'ko hannun sa ya ce " Baba ina maka shaida baka watsar da iyalin amininka ba, har yau din nan da tsufa ya cimma maka sosai, baka huta da yi mana hidima ba. Ina yi maka fatan samun aljannar da Annabi ya yi bishara ga masu kyautatawa iyalan wadda suka rasu".

Jin wannan albishir din ya sake 'karfafawa Mk jiki, domin zuciyarsa ta yi haske. Washagari da safe aka sallame shi.
Ya isa gida bisa rakiyar Dr 'Karfi, tarba na mussaman ya samu daga Farida.

'Karfi bai jima sosai ba ya tafi. Mk ya dinga biyewa Farida na yadda take ina ka saka da shi.

Ya fito wanka ya tarar da ta ajiye masa kaya a bakin gado, gajeran wando ne tiri kwata kalar ruwan 'kasa, sai farar riga ti.shet ya fesa body spray ya sanya kayan da ta riga ta feshe su da turaransa na Versace.

Tawul din da ya dauro, ya dauka ya rataye shi a bandakin, yana fitowa ita kuma ta shigo dauke da tiren kayan abinci.

Yana zaune bakin gado yana kallon yadda ta yi masa shimfida, ta fara zuba masa abincin da ya kasance dankalin turawa da miyar albasa sai gashashiyar kaza, gefe yankakkiyar kankana ce jawur da ita, an lullubeta da ledar rufe abinci.

Sama sama ya ci abincin, ya mayar da hankalinsa wurin shan kankana, ya kalleta ya ce "zanga ranar da zaki daina bani lemo da safe".

Ta mike da sauri tana cewa"wallahi na dafa maka shayin ga su cups nan flask din na manta".
Cikin kankanin lokaci ta kawo masa, da kanta ta zuba masa, tunda ba ma'abocin shan shayi da madara bane.

Bayan ya kammala ta 'ballo masa magungunansa ya sha.

Ya mike ya ce " Bari na sauka na dan kewaya, bana jin ciwo a tare da ni, amma sam jikina babu karfi".

Ta ce "hakan ma babu laifi, ko na dauko maka lucozade it will help".

Ya kalleta ya ce "Bari na kewayo dai, so nake mu yamutsa shimfidar can."
Ya yi nuni da gado.

Kunya ta kamata ta yi murmushi, ba tare da ta sake cewa komai ba.
Ya juya ya fita.

Hakan kuwa aka yi, domin bai wani jima ba ya dawo, hakanan duk yadda yake jin rashin kuzari, sai da ya zartar da kudirinsa. Duk yadda take ro'kon ya bari ya warware sosai, amma bai ji ba.

Sai fa'di yake "kewar ki na yi sosai, har addu'a nake na samu sauki na dawo gida, ba dan komaai ba, sai dan na kasance tare da ke".

Da'di ya matu'kar kamata, ta tabbatar tana da matsuguni a zuciyar mijinta. duk dai abin da Sa'adah ta yi mata a asibiti, yasa ta gane har gobe tana da karfi a zuciyarsa.

Yini guda bai fita ko ina ba, da aka yi azahar ya ci abinci, ya sha magani barci ya yi sosai.

Dan haka bai fita ba, sai a washagari, ya fita zuwa gidan Hajiya, fa'da da Jan kunnen da ta yi masa akan ya ri'ke Sa'a da girma ba ka'dan bane.

Fa'di take "ubanta mutum ne har da rabi, ka ji tsoron ubangiji ka ri'ke ta da Amana, na sha fa'da maka ba hankalin ku daya ba".
Ya amsa da zai kiyaye.

Daganan ya leka shagonsa, ya kuma gaida Baffah.

Baffah ya ce "wannan karon ma sadaki kawai zaka bata"

Da sauri ya ce "A a Baffah bar ni kawai na yi mata komai, gatan zai mini yawa, yanzu Ina da halin yin dukkan abin da ake yi, na gode sosai da karamci, Ina fatan kar Allah ya sa na sake kunyata ka Baffah".

"A a ni ba ka kunyata ni, bare ka nemi tsari da sake maimaitawa, ba komai tsakanin mu sai karramawa, domin tunda kaki fa'dar abin da ya hadaku, kuma kowa ya gane itace mai laifin, sai na gane kai din jarumine, adaline, mai kuma kaunata ne, Koda ha'kurin ka ya kwace amma ai hankalinka bai kwace ba, domin baka tozarta mini Iyah ta hanyar fa'din aibunta ba, dan haka Ni baka mini komai ba, sai alheri."

Ya zarce da cewa "a farko da zan baka ita, sai da na jaddada maka kar ka bari ta kangare maka, duk kuma wadda ka ga tana mu'amala da su, hankalinka bai kwanta da su ba, ka shata musu layi, Ina jin dai baka dauki wannan shawarar ba shiyasa kuka tsinci kanku a halin da kuke ciki, ba fa zan rufe ka ba, kaima kana bari soyayyarta na rinjayar ka a gurare da dama, a farkon rikicin banyi magana bane saboda yadda ka boye komai ka sata itama ta rufe komai"

Mk da ya san Baffah gaskiya ya fa'da sai ya sunkuyar da kansa kasa, ya kasa cewa komai.

Tsawon lokaci kafin Baffa ya sake cewa "Na horeka da yin adalci a gidanka, ka yi iyakacin bakin kokarinka, ka yi adalci, sai kuma ka barwa Allah ya taya ka. Domin a yanzu ma ina sake fa'da maka duk abin da bai maka a tare da Iyah ba, tun kafin ku yi nisa ka taka burgi akansa, su mata da ka gansu idan ba a kula da tarbiyar su ba, nan da nan zasu halaka kansu su halaka mazansu".

Jikin Mk ya yi sanyi, domin kuwa a kullum dabi'un Baffah na fahimtar da shi bai gama saninsa ba, har yau din nan bai ci karo da mutumin da ya fi mahaifin Sa'a karamci da fadar gaskiya ba, ko da kuwa gaskiyar akan kansa ne.

Mk da ya rasa mai zai ce sai kawai ya sunkuyar da kansa kasa ya ce "Madallah da zuciya irin taka, dama ka sha fa'da mini ba Sa'a ce ta hada mu ba, ba kuma zata zama dalilin rabuwarmu ba, tabbas na gasgata hakan".

Mk ya zarce da fa'din
" Alherinka yawa ne da shi Baffah! A duk lokacin da nake gabanka sai nake jina tamkar ina cikin shekaru irin na Jawad. Saboda zuciyata tana samun nutsuwa, domin tana tare da wadda yake girmamata, yake ganin kimarta. Kai ka'dai ne baka ga laifina akan kaddarar rabuwarmu ba, Kai ka'dai ne ka yi mini shaidar fin 'karfina al'amarin ya yi, haka kai ka'dai ne a duk tsayin wannan tafiyar bai juya mini baya. Haka nan yanzu kowa jan kunne yake mini akan na rike Sa'adah komai zata mini na yi hakuri, kar na ce komai.
Kai ka'dai ka ce na yiwa 'daya matar tawa adalci, kai ka'dai ne ka ce kar na yi hakuri da Sa'adah a inda zata kuskure ko ta sab'awa ka'ida.
A yau na sake ganewa kai din ba uban Sa'adah bane nawa ne"

Ya yi shiru saboda yadda yake jin rauni na shigar sa, ko mutane nawa ne irin Baffaha a Yau?

Ya tuna kwanakin baya yadda ya zaunar da shi yana fa'da masa tsananin son da yake yiwa Iyah! Amma a yau ya ture wannan soyayyar ya fa'di gaskiya, ayiwa Farida adalci, kar kuma ya bawa Sa'a damar da zata halaka, ta halaka shi.

Ya dago idansa da suka ka'da ya ce "Baffah kwanakin baya ka ce mini baka ta'ba mallakar abin da kake so kamar Iyah ba".

"Eh"
Baffah ya amsa a taikace .

Mk ya ce "Nima yau zan fa'da maka ban ta'ba son wata mace a duniya kamarta ba. Zan yi iyakacin kokarina na dauki shawararka na kar na bari ta halaka mu, Amma fa'da mini maganin rikicinta Baffah! Ita din sarka ce mai rikicin gan-gan".

Dariya ya yi ya ce "ai ba zata daina ba, Amma ina tabbatar maka zata rage da yawa daga cikin rikicin nata mussaman na dogon buri da kawaye yan karya domin ka shayar da ita mamaki. Abin da na san ba zata daina ba, shagwaba, saurin kuka, da kishi. Wannan kuma kaine zaka kiyaye motsuwar kishin, shagwaba da kuka kuwa idan ta yi ai sai ka rarrashi abarka".

Kunya ta kama Mk ya kasa cewa komai

Sosai ya yi godiya sannan ya mike yana cewa "Makaranta zan tafi".
Da sigar tsokana Baffa ya ce "Ba zaka leka ku yi tozali ba?"

Kunya ya ta sake kama Mk ya ce "Ai mun yi fa'da Baffah, ba zan nemeta ba, sai ta neme Ni".

Dariya sosai ya yi tare da cewa "Anya kuwa ka yi gaskiya Mutari? Amma dai ba ruwana".

Ko wayar Sa'adah bai nema ba, bare ya je gidan wurinta, ya wuce makaaranta.

Sa'adah ganin kwanaki biyu da sallamo Mk amma bai nemeta ba, ya sake hauhawar fishinta, yayin da shima fishin yake yi da ita mai tsanani, kawai ya samu salama ne na tabbacin zata dawo hannunsa, amma ganinta da ya yi da Khalil ba 'karamin haushin ta ya ji ba, kullum da aikinta yake kwana, yake tashi tunda shine sanadin da yasa take mua'amala da ahalin Khalil.

Kwanaki uku ya rage daurin aurensu amma babu fahimta a tsakanin su lamarin da yake ciwa Sa'a tuwo a kwarya, wani sashi na zuciyarta ya ce saboda yana da wata matar ne, wani sashen kuma ya kore wannan tunanin tare da tuno mata, tana budurwa ma haka ya dinga Wannan wula'kancin har ta yi zaton soyayyar ne bai iya ba.

A daren Mk na zaune a falon sama yayin da Farida ta yi filo da cinyarsa, yana wasa da dogon gashinta tamkar mai yin kitso, sai fama yake da bugun zuciya adalilin yana son fa'da mata, juma'a mai zuwa daurin aurensa da Sa'adatu.

Sau uku yana yun'kurin fa'da sai ya kasa, da 'kyar ya yi kundubalar cewa " My ferial tashi ki zauna magana zamu yi da nake bu'katar nutsuwar ki'.

Ta tashi da sauri kuwa, ta zauna sosai tana fuskantar sa.

Cikin karfin hali ya ce " Ranar juma'ah mai zuwa idan muna cikin rayayyu, za'a mayar da aurenmu da Sa'adah".

Wani irin tashin hankali ya ziyarci Farida, irin wadda bata ta'ba hasashen zata ji shiga ba, ta dinga yun'kurin bude baki ta yi magana amma hakan ya gagari Kundila.

Ta dinga karanto addu'a, amma duk da hakan sai da hawaye ya goce mata, wani irin tukuki ya mamaye zuciyarta, ta dinga jin tamkar ta mutu ta huta.

Da sauri ya janyota jikinsa ya rungume sosai, ya dinga fa'din sorry a hankali, wannan rarrashin ya sanya kukan ya kwace sosai, ta dinga yi, shikuma yana saka tissue yana goge mata. Ta jima a hakan, sannan ya ce "Ya isa haka, Yi shiru ki fada mini menene ya kidima ko haka".

Cikin kuka ta ce "Tsoro nake ji kar na rasaka, tsoro nake ji kar juya mini baya, tsoro nake ji kar ka kasa yin adalci ka halaka".

Cikin rarrashi sosai ya ce "Na ta'ba fa'da miki ba macen da zata sa na rabu da ke saboda ita, sai idan tamu ce ta hado mu, ba yadda za'ayi na juya miki baya Farida! Ina mamakin har yanzu da muka yi shekaru uku baki fahimci iri son da nake miki ba zai tan'kwabu bisa 'karamin dalili marar tushe ba.
Ba zan miki 'karya ba, da gaske an jarrabeni akan Sa'a! Amma ki taimake ni ki fa'da mini shin ina miki wani abu da kika kasa gamsuwa son da nake mata, ba zai hana na so ki ba"

Ta yi shiru tana ajiyar zuciya! Ta sani bai ta'ba mata wani abu da zata ce baya sonta, ko ya tauye ta ba, amma da ace zata iya da ta ce so take ya fi sonta akan Gogel, sai dai ba zata iya ba, shima kuma bata jin zai iya hakan, tunda ta san ubangiji ne yake cusa soyayya a zukatan bayi.

Ya sake rungumeta tsantsan ya ce "fa'da mini mana ke nake sauraro"

Ta girgiza kai ta ce "Babu"
Ya ce "Zan fa'da miki gaskiyar magana! Wallahi ina sonki, Ina tsananin sonki, hakuri da kawaicin ki ya 'kara miki 'kima a idona da zuciyata, kar ki bari kishi ya kwace miki wadannan halayyar, domin kina jan hankalina da su, ina jin kunyar bata miki. Sannan zan ro'ke ki arziki! Ki bani hadin kai ta yadda zan yi muku adalcin da zaki gamsu, idan na kuskure dan Allah ki mini uzziri wallahi ba zanyi abin da muzanta ki da gangan ba".

Ta saki ajiyar zuciya taare da cewa "To".

Ya dinga yi mata maganganu masu da'di, Wanda wasu ta tabbatar ya fa'da ne dan hankalinta ya kwanta amma dai ta ji da'di kwarai da gaske, ta samu sau'kin daurewar da kirjinta ya yi.

Ya kalli agogo ya ga har sha'dayan dare ta gota ya mike da ita cak tamkar yar jinjira ya shige daki da ita ya dire kan gado ya ce"Ashe ma fafaloloce ba nauyi"

Ta dan murmusa kadan ba tare da ta ce komai ba.
A haka ya dinga hilatarta sai da ya raya daren da ita cikin wata irin soyayya mai tsayawa a zuciyar mace.

Har ranar daurin aure ta zo ba wani jituwa tsakanin Mk da Sa'adah.

Ranar juma'ah 15/7 aka sake daura auren Mukhtar Kabir Bichi da Sa'adatu Bashir Gogel akaro na biyu akan sadaki Mai darajah.

Sai yamma suka baro Gogel, duk yadda Mahmoud ya so suje gun amarya Amma Mk ya ce ba inda za shi.

Dr 'Karfi ya kalli Dr Mk da ya yi kicin kicin da fuska ya ja tsaki ya ce "aikin kawai duk wani cin magananinka na 'karya ne, wato yanzu ka sami kwanciyar hankali shine zaka hau wani fiffika, to dan ma dai tsiyar Sa'adah ta fi taka, yanzun nan zata sumar da kai, farfadowa sai a gadon asibiti".

Fuska a daure Mk ya ce 'Tunda ba a lahira zan ji ni ba, ai da sau'ki, ka takura ni fa ".

Da dariya 'Karfi ya ce wallahi ka bini a hankali ka san ina da dorinar da idan na zuba maka sau uku, amarcin da kake rawar jikin zaka sabunta shi ba zai yiwu ba".

Dariya ta kwace musu dukkansu Mk ya guntse ya ce "Na rantse kuwa da ba zan yarda ba".

Har suka rabu caccaka Mk yake sha a wurin Mahmoud.

Washagari da hantsi Mk ya yiwa Sa'adah siyayyar komai na amfani, karon farko da shi a karan kansa ya siya ba wai Jawad ya saka shi akan dole ba, ya tuno sadda take cewa idan ya sake yi mata wani abu na alheri ba zai gama da Hajiya lafiya ba.

Ya fesar da zazzafar ajiyar zuciya yana ayyana banda zuciya ba a ganinta bare a hukunta ta ai bai kamata zuciyar tasa ta zarme akan soyayyarta haka ba.

Ya nisa a fili ya ce "Albarka cin Baffah na yafe wannan maganar".

Amma haushin ganinta da Khalil da kuma tariyar da ta ce ba zata yi yanzu ba, ya matu'kar bata masa rai, shiyasa kullum ya yi sallah sai ya roki ya samu dalilin da itace zata nemi ta tare da bakinta.

Ya cika mota da kayayyakin ya nufi gidan su Sa'adah.
Domin ya kai mata ,tunda yanzu ta rataya a wuyansa, duk da ita bata da niyyar sauke nasa hakkin da ya rataya a wuyanta.





Surayya Dahiru
โœ๏ธโœ๏ธ.


๐ŸŒบ *HALIN YAU*! ๐ŸŒบ

*NA*

*SURAYYA DAHIRU*.


*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ยฎ_* โœ๏ธ
โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ษ—amfare da bin ฦ™a'idar Adabin Hausa.```

```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` โœ๏ธโœ๏ธโœ๏ธ
____________(โœช)______________

https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/


*GAISUWA GA*.
*Haj Zulaihatu Sani Kagara*
*Haj Maimuna Beli*.
*Hassana 'Danlarabawa*.
*Ku Dade, ku yi 'karko irin na Dabino*.



*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*.

107-108.


Sannu a hankali yake yin tuki, har ya isa gidansu Sa'a.

A zauren kofar gidan, ya tsaya, ya fito da wayarsa, ya dinga 'kiran layin Sa'adah amma tana gani ta yi mirisisi, yana tsaye Baffah ya shigo, suka gaisa ya ce "Ya ka tsaya shigo mana".

Tare suka shiga cikin gidan, Inna ce a Zaune tana kwadon zogale.

Mk

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login