Showing 189001 words to 192000 words out of 245004 words

Chapter 64 - Abban Sojoji Book 2 Complete Pdf Download

17 Mar 2025

25260

da Marshal Ya tura masu suka ga iri ɗaya fuskar,sae ransu ya basu cewa itace yarinyar da Omar yace su nemo mashi,
Da sauri suka tsayar da motocin nasu tare da diddirowa daga saman motocin tamkar wasu zakuna haka suka tunkari sehrish,
Kamar ance ta juya,idanunta sukayi arba da waɗannan sojojin dake tunkararta hannunsu ruke da bindigu,bakomai ne ya fado mata a ranta ba face Ƴan boko haram da ƴan bindiga daɗin dake ta sace mutane agari,
ja da baya tashiga yi gabanta na faduwa
maimakon suyi mata magana cikin daɗin rae sai suka daka mata tsawa tare da cewa"ke zonan"!
Aikuwa a firgice sehrish ta watsa da gudun gaske ta saki jakar makarantarta ƙasa,bin ta sukayi da gudun gaske,tana gudu suna bin ta tamkar zata tashi sama,
yarda kasan wadda taci ƙafar kare haka ta dinga gudu,ita kanta batasan inda ta dosa ba,gudu kawai takeyi,

adaidai nan su Omar suka ƙaraso gidan uncle Abusufyan,Wayarshi ta shiga ruri,cikin sauri ya fiddota daga cikin aljihun wandonshi,yayi picking call ɗin tare da kara wayar a kunnanshi yayi sallama,
Muryar ɗaya daga cikin sojojin ce yaji yana cewa"Sir,munga yarinyar da ake nema,amma taƙi bari mu kama ta,'
Hankali tashe Omar yace"Kada ku bari ta kufce maku,kuyi ƙoƙari ku kamota,kuyi mata magana cikin sanyin murya,saboda yarinyar tana da tsoro sosai,kun firgitata ne shiyasa ta gudu,
"Okey sir,ya amsa mashi tare da katse kiran,
"Yalla6ai meya faru ne"!
Cike da takaici Omar yace"Major,an samu matsala!sojojin dana tura don su nemo mun jahad,sunyi arba da yarinyar gidan mu,dama na faɗa maka cewa kamanninsu sak iri ɗaya,ɗazu nace ma Osman Ya ɗauko mun hoton fuskar hosana,saboda in tura masu suyi amfani dashi wurin nemo min jahad,to da wannan hoton su kayi amfani wurin nemanta shine Allah ya haɗasu da ita yarinyar da junaid yayi musanya da jahad,'
Tunda yasoma magana jahad ke kallonshi cike da mamakin wannan wani irin kamanni ne,dayasa har ba'a gane banbancinsu!?
Major yace"Amma nayi mamaki yalla6ai!wannan wata irin kamanceceniya ce atsakaninsu da har ba'a iya bambanta tsakaninsu"!
Omar yace"nikaina major abun ya jima yana ɗaure mun kai wlh,da farko nayi tunanin cewa saboda ƙaunar da nakeyi ma su hosana ne yasa nake ganin fuskarsu akan fuskar yarinyar,amma yau da junaid ya dauko jahad a matsayin ita yarinyar,sai na tabbatar da cewar ba gizau bane,tabbas kamanninsu ne ɗaya!
Major yace"abun mamaki abun al'ajabi!yalla6ai kada kace na cika ka da surutu,dan Allah yaya kuke da ita yarinyar?ko ƴar wurin uncle ɗinku ce,' ya ƙarasa maganar adaedae lokacin da yayi parking ɗin motar a cikin gidan Abusufyan,
murmushi Omar yayi tare da cewa"ƴar aikin gidanmu ce,sunanta Sehrish! Yarinyar tana da kirki sosai shiyasa Abbanmu ya mayar da ita tamkar ɗiyarshi,yanzu amatsayin kanwarmu take............'
Waro ido waje Jahad tayi cike da tsananin mamaki ta furta"SEHRISH!!!!!!!!!!!!!!!!"

juyawa Omar yayi yana kallonta jin yarda ta ambaci sunan kamar tasanta,shima major juyowa ya danyi daga zaunen da yake a front seat din suna kallonta,
"Jahad kin santa ne!"?
Muryarta na kerma tace"Ya...Omar...Bansan ko ita bace ba,amma akwai ƴar uwarmu da muka jima muna nemanta,kamanninmu sak iri ɗaya,Mu ƴan ukune dani da hosana da kuma ita,Sunanta Sehrish atare aka haife mu,ciki ɗaya muka fito tare da ita,arana ɗaya kuma a lokaci ɗaya.......'
Kallon juna Omar da major sukayi cike da mamaki suke sauraronta,sae da takai ƙarshen maganarta,sannan Omar yace"Dama ke da Hosana ba twins bane!!!"?
ɗaga mashi kai tayi alamar eh,tace"WE'RE TRIPLET".


Wannan shirin da kuke karantawa ba ammasco bane suka ɗauki nauyin kawo maki shi ba,Boss bature ce da kanta,ta shirya kuma ta gabatar,😂

Idan har kinji daɗin wannan update ɗin,kiyi following din acct dina a tiktok😍😂ga link can na bada daga sama

*💋Boss Bature💋*



Join this link to follow my tiktok acct👇

https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1




قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖

Abban sojoji paid book ne,ga duk maison karanta cigabanshi zai biya 300 ne za'a tura mashi nabaya har inda muka tsaya,ga mai buƙata direct zaiyi mun magana ta whatsapp ɗina 08103884440, pls banda phone calls,Mijina ya hana ana kira na awaya🤭🤫


❤🤍❤


Gaba ɗaya farin ciki ya lullu6e Marshal Omar da kuma major,tunda su kaji bayanin Jahad suka tabbatar da cewar ba shakka Itace ƴar uwartasu da take magana akai,
"Jahad,wannan maganar ba anan ya kamata muyi ta ba,mu shiga daga ciki"
buɗe motar Omar yayi tun kafin major ya buɗe mashi,fitowa jahad tayi itama,sannan shima major ya fito,duka dae a tare suka ɗunguma izuwa cikin gidan,har lokacin jikin jahad rawa yake yi,saboda tsabar doki da kuma zumuɗin ganin cewa Sehrish ce yarinyar da Omar ke magana akai,

Lokacin da suka shiga cikin palour ɗin atare,hosana na a kwance saman 3 seater,tasha kuka harta gaji shine ta ɗan kishingiɗa nan,bacci ya kwashe ta, ko uniform din bata cire ba,bin ta da kallo Omar yayi bakomai ya faɗo mashi a rai ba,face abunda yayi ƙoƙarin aikata mata,tausayinta ne ya kama shi sosae,tsayawa yayi atsaye ya zuba mata ido ko kyaftawa baiyi,
"Ya Omar,ka zauna mana,"muryar jahad ce ta katse mashi kallon da yake ma hosana,
  Wuri ya samu saman 2 seater ya zauna,jahad kuma ta zauna asaman 1 seater,mayar da idonshi yayi kan major ganin ya tsaya daga tsaye yace"bismilllah mana,ave seat," ya nuna mashi gefen shi,murmushi major yayi tare da ƙarasawa ya zauna daga gefen Marshal,
  "Jahad,inaso kiyimun bayani sosai yarda zan fahimta game da ƴar uwarku,taya akai kuka rabu da ita har tsawon wannan lokacin'? Omar ne ya jefa mata tambayar,gaba ɗaya suka zuba mata ido suna sauraron jin abunda Jahad zata ce,
   "Ya omar ba da son ran mu muka rabu da ita ba,ƙaddara ce ta rabamu da ita,amma muna son junan mu sosai.....'dakatawa tayi da maganar yayin da idanunta suka cicciko da kwalla,
  Anatse taci gaba da magana"ƴar uwarmu tana son mu sosai,tasha wahala akanmu,a lokacin baya Dani da hosana an ta6a kwantar damu asibiti,za'ayi ma hossana aiki,ana neman kuɗi kusan dubu ɗari tara da za'ayi mata aikin,bamu da ko sisi,bamu da mai taimakon mu sae Allah,mu kaɗae muke rayuwarmu tare da wata tsohuwa wadda take ruƙon mu a wurinta,wannan dalilin ne yasa sehrish ta nemi aikatau,don ta biya kuɗin aikin hosana da kuma na maganin da za'a siyamun,babu yarda muka iya alokacin wannan kaɗae ce mafita,muna ji muna gani ƴar uwarmu ta tafi neman kuɗi saboda ta nema mana lafiyarmu,ya Omar Sehrish tayi duk wata gwagwarmaya akanmu,damu da ita duk kanmu ɗaya,amma ita tamkar uwa take a wurinmu,tamkar yaya take a wurinmu,bamu da tamkarta aduniyar nan,rishi har ranta zata iya sadaukarwa saboda mu,nayi kukan rashinta sosai,nayi baƙin cikin yin nesa da ita........tun muna yara muke tsananin son junan mu,rayuwarmu a wulaƙance mukayi ta sakamakon mugun uba da muke dashi wanda bai ta6a nuna mana soyayya ba........'fashewa tayi da matsanancin kuka,
  Gaba daya jahad ta gama kashe masu jikinsu yayi sanyi,
  dakyar ta tsagaita da yin kukan taci gaba da magana"bayan sehrish ta tafi aiki,cikin sa'a ta samu kuɗin aikin hosana ta biya,lokacin da aka sallame mu daga asibiti,muka koma gidan tsohuwar da take kula damu,anan muke rayuwarmu,kullum muna kiranta awaya mu gaisa da ita,ita ma kuma tana kiran mu awaya taji ya lafiyar mu take,akwai wani lokaci da maganin hosana ya ƙare,ciwonta ya soma dawowa ta dinga hauka tana ƴan buge buge,hankali na ya tashi,gashi bamu da kuɗin da za'a siya mata wasu magungunan,shine na yanke shawarar sanar ma rishi halin da ake ciki,don ta taimaka mana dana magani,na tura mata saƙo ta waya,sai gashi ta turo mun da amsar cewa mu tura mata da acct number,cike da zumuɗi na zura hijabi na shiga gidan makwabtanmu wurin ɗiyar matar,don ta rubutamin acct number ɗinta tun da mu bamu da ita,ashe lokacin da na fita daga gidan,hosana tafarka daga bacci tana son shiga toilet,shine ta ɗauki wayar dana bari saman jakar kayanmu ta shiga toilet da ita,kafin nadawo cikin gidan hosana ta jefar da wayar cikin masan,wannan shine silar da muka rasa sehrish gaba ɗaya,saboda ba mu da wata hanyar da zamu iya magana da ita,sae ta wannan wayar.......'ƙarasa maganar tayi tana faman share kwallar da ke kwaranyowa daga idanunta,
  sunnar dakai omar ya ɗanyi,yayin da yake jin zuciyarshi wani kala ba daɗi,haka shima major duk tausayin yaran ya kamashi,musamman ƴar uwarnan tasu sehrish,yarinyar tayi bajinta sosai,
  ɗagowa omar yayi tare da kallonta yace"Jahad,inaso ki faɗamu taya akai kuka shiga hannun ƴan sanda?wane laifi kuka aikata ne"?
  Cikin shessheƙar kuka tace"bamu aikata laifin komai ba ya Omar,sharri ne akayi mana,abunda ya faru bayan hosana ta jefar da wayar acikin rami,sae ga tsohuwar nan da take rainon mu ta shigo cikin gidan,anan ta same mu ni da hosana muna faɗa akan wayar da ta jefar mana,sai take tambayar meya faru ne muke faɗa,shine na sanar da ita abunda ya faru,hankalinta ya tashi sosai akan wayarta da mukayi mata asararta,rai a6ace ta shige cikin ɗaki ta rufe ƙopa,duk bamuji daɗi ba lokacin saboda bata ta6a nuna mana 6acin ranta ba irin na ranar,atsaye muka kwana muna bata haƙuri akan ta buɗe mana ƙopa mu shiga ciki,saboda a gidan ɗaki biyu ne,amma ɗaya ya rushe saboda ruwan saman da aka ta6ayi mana mai ƙarfi,ya Omar aranar waje muka kwana har ciwon hosana ya tashi,kafin washe gari kuma taji sauƙi,koda muka farka munyi tsammanin zata buɗe mana ƙopar amma abun mamaki sae muka ga ƙopar adatse,tun muna sa ran zata buɗe mana kopar har muka fidda rae,a ƙarshe agidan makwabtan mu muka shiga yin sallar asuba,anan ma muka ci abinci,da mamansu yarinyar ta tambayemu meya faru,muka sanar da ita duk abunda ya faru,shine yarinyar gidan ta rakomu har gidan mu,muka haɗu tare da ita muna babbuga ƙopar,a ƙarshe hosana ce tayi ƙoƙarin 6alle ƙopar......anan muka samu gawarta,ashe tun daren jiyan ta mutu.......mutane kuma suka daura mana laifin kisan nata,saboda sun gano cewa guba aka bata taci,wannan ne dalilin da yasa ƴan sanda suka kaimu police station,bayan an gama tattara hujjojin da za'a miƙa mu kotu dasu,sae kuma ciwon hosana ya tashi acikin cell,wannan ne farkon fitarmu daga cikin cell aka kai hosana asibiti,Ya omar kaji yarda akai muka kasance a hannun ƴan sanda..... "Ƙarasa maganar tayi yayin da hawaye ke ta faman sintiri a fuskarta,
  "Ina mahaifiyarku take ne"?omar ne ya kuma tambayarta,
  Jahad tace"bamu san inda take ba,bani da tabbacin cewa tana a raye kota mutu,abu ɗaya nasani koma a wane hali take yanzu indae tana araye to bata acikin hankalinta,"
  Jinjina kai Omar yayi kafin yace"Insha Allah zan bincika komai a sannu zan gano duk wanda yayi sanadiyar shigarku cikin wannan halin,bazan ƙyaleshi ba,koda uban da ya haifeku ne,zan yanke mashi hukunci daidai da zunubin da ya aikata,'
   major yace"wannan gaskiya ne,yalla6ai Allah ya taimaka kuma yayi jagora,nidae yanzu babban burina shine ƴan ukun nan,su kasance a ƙarƙashin kulawar family ɗinku,"

  Omar yace"abun ya ɗaure mun kai major,kaji wani iko na Allah nan,gaba ɗaya yaran su ukun suna a ƙarƙashin kulawar family dinmu,duka Allah ya haɗasu awurinmu batare da saninsu ba,kuma batare da sanin mu ba,ita ɗayar ƙaddarar aiki ce ta kawota gidan mu,yayin da su kuma su hosana da jahad,ƙaddarar zaman asibiti ce ta haɗani dasu a lokacin da hosana ke hauka hannunta ruƙe da bindiga,Major abun akwai wata sarƙaƙiya acikinshi,tabbas akwai abunda Allah yake nufi da waɗannan yaran!akwai wani abu da Allah ke son bayyana mana shiyasa ya haɗasu duka awurin mu!"
  Zuba mashi ido jahad tayi tana kallonshi ita kanta abun ya ɗaure mata kai,
  Shi kanshi major ya shiga kokonton cewa Anya yaran basu da alaƙa dasu Marshal Omar?juyawa yayi ya dan kalli fuskar marshal sannan ya mayar da idonshi akan hosana,sae lokacin ya dinga ganin wata irin kamanceceniya atsakaninsu sosae,tabbas akwai wata alaƙa ta jini a tsakaninsu,shiru kawai yayi baice komai ba,
  Kowa ya tafi duniyar tunani hafsat bature ma,ta ɗan ajiye typing tana tunanin wannan abun daya ɗaure mata kai tamau...,
  "Ya Omar,"gaba dayansu sukayi firgit suna kallon Hosana dake kwance tafarka tana faman mutsistsike idanunta,jin muryar Omar yasa ta ambaci sunan shi,
  Murmushi ya dan saki tare da ambaton sunanta "Hosana",
  miƙewa tayi zaune tana ƙare masu kallo gaba ɗayansu,tashi Omar yayi ya koma gefenta ya zauna yana kallonta,
   lokacin da ta tabbatar cewa shine saita fashe mashi da kuka tana cewa"Ya omar fushi nake dakai,meyasa ka tafi kabarmu kadaina zuwa wurin mu?laifin me mukayi maka da har kayi mana wannan horon"?
Lallashinta ya shiga yi yana cewa"Am really sorry hosana..pls stop crying and wipe ur tears,komai ya wuce yanzu muna tattaunawa ne game da ƴar uwarku Sehrish...... '
  Tunda ya ambaci sunan sehrish hosana tayi tsit ta nemi kukan da takeyi ta rasa la66anta har rawa sukeyi wurin cewa"Anganta ne ya omar?"
  Murmushi Omar ya saki tare da cewa"An ganta hosana!ƴar uwarku da ku ka jima kuna nema,ashe itace yarinyar dake yi mana aiki agidan......"bai ƙarasa maganar ba hosana ta fashe da kukan murna tana cewa"Ya omar tana ina?ina rishi ɗinmu take?inaso naganta!tana ina,wayyo Allah na....'
  Yarfa hannunta tashiga yi saboda tsabar farin ciki bakinta yaƙi rufuwa hawaye na zuba fuskar kuma ɗauke da dariyar farin ciki,
  Itama jahad farin cikin ne tsantsa afuskarta yau takasance babbar rana agaresu rana mafi girma arayuwarsu ranar da Allah yasa suka gano inda ƴar uwarsu sehrish take,dole suyi farin ciki,bama su kaɗai ba,hatta masu karanta labarin rayuwarsu da kuma marubuciyar data zauna ta tsara labarin ita da kanta tana taya su farinciki,Ya Allah ka ƙara danƙon ƙauna atsakaninmu da ƴan uwanmu masu son mu,Allah ka bamu ikon faranta ma juna da kuma taimakon junanmu,a gudu tare kuma atsira tare❤

Omar ya jima a wurinsu hosana kamar karya tafi ya barsu haka yaji,abunda yasa bai tafi dasu yau ba saboda Yarinyar gidan tasu da ba'a gani ba,yafi son sai sun ɗauko yarinyar sannan ya kaisu gidan nasu don suga ƴar uwarsu ido da ido,zai so yaga wannan farin cikin a fuskokinsu,
Bayan tafiyar su Marshal Omar,jahad da hosana duk sun bi sun ruɗe saboda tsabar murna ko abincin rana basu ci ba,sai faman sintiri sukeyi acikin babban falon nasu,aƙagare suke dasu ga sehrish,zuciyarsu sae faman azalzalarsu take akan son ganinta kamar suyi hauka.

💋BOSS BATURE💋

Ga wani tashin hankalin kuma,duk yadda sojojin nan suka so su kama sehrish abun yaci tura domin kuwa sehrish ta kubce masu,babu irin neman da basuyi mata ba,amma babu ita 6at ta 6ace kamar al'jana,abu kamar wasa har bayan sallar La'asar basu ganta ba,
Niko sehrish ina kika shiga ne!kai jama'a daga antaro nan sae kuma nan ya ruguje,

tunda Abbansu ya sanar mashi game da zuwan Aunty azeema,jiki na rawa junaid ya fito daga dakin Abbansu da gudun gaske ya nufi ɗakin da aka saukar da ita,faɗawa cikin ɗakin yayi ko sallama babu saboda tsabar ɗoki,a lokacin tana daga zaune saman gadonta tana daddana wayarta,sam bata lura dashi ba,bata ji shigowarshi ba,sae dae kwatsam taji faɗowarshi jikinta,gaba ɗaya ya ƙanƙameta sosai,yana yi mata kukan shagwa6a wai yayi missing ɗinta sosai,
Dariya sosai hajiya Azeema tashiga yi tana cewa"Oh ni junaid,tun ɗazu nake ta tambayar ina babynmu yake ina babyn mu yake,duk na ƙosa naganka naso ace ina shigowa cikin gidan nan kaine mutun na farko da zaka fara tarbata da wannan sumbatar taka,"
  ta ƙarasa maganar tare da ɗago shi daga jikinta tana bin shi da kallo tace"Masha Allah,junaid kaine ka koma haka?ka ƙara girma sosai kyakkyawan yarona,nayi missing ɗinka sosai,"
  murmushi junaid ya sakar mata tare da cewa"mommy azeema ina tsarabata?me kika kawo mun"?
  Dariya tayi tana girgiza kai tace"Tsarabarka na nan junaid,wannan karan nazo maka da abun ban mamaki,inaso inga farin cikin da zakayi idan nabaka tsarabar nan,"
  cike da zumudi junaid yace"tana ina,"
  Harara ta ɗan watsa mashi tare da cewa"Shine damuwarka?ka manta baka bani kiss dina ba,"
  matsawa junaid yayi tare da kai bakinshi gefen fuskarta ya manna mata kiss sannan ya ɗago yana kallonta yace"yanzu sai aban tsarabata ko"?
  Dariya tayi tace"ɗaukomin trolley ɗin kayana,"tayi maganar tana yi mashi nuni da trolleyn da Kanal yousouf ya jingine mata ajikin wardrobe,
  jiki na rawa junaid ya saukko daga saman gadon ya taka izuwa wurin wardrobe din ya ruƙo trolleyn tare da janyoshi har wurin gadon ya miƙa mata shi,sannan ya zauna daga gefe ya zuba ido yana jiran ganin tsabar da tayi mashi,
   hannu tasa ta buɗe trolley din ta curo wani ɗan kit ƙarami sai faman ƙyalƙyali yake yi yadda kasan da gold akayi jikinshi,tunkan ta buɗe shi junaid ke ta faman haɗiye yawu yarda kasan yaga abunci,
    Murmushi ta danyi tare da kallon fuskarshi tace"close ur eyes,"
  Rufe ido junaid yayi kamar yarda ta umarta,
   Murmushi ta kuma yi tare da buɗe akwatin tace"Now Open ur eyes,"
   A hankali junaid ya buɗe idanunshi kai tsaye suka sauka akan danƙareran Zoben diamond ɗin da ta siya mashi tare da agogonshi,sae faman ƙyalli suke suna ɗaukar ido,diamond bana wasa ba,wanda aƙalla price ɗinsu yayi miliyan ɗari uku,
  Waro ido waje junaid yayi yana bin su da kallo saboda tsabar farin ciki ya gaza rufe bakinshi,hannunshi na kerma ya kar6i akwatin yana ƙare masu kallo,
Cikin tsantsar farin ciki yace"aun...aunty..wannan duk nawa ne"?
   dariya Azeema tayi ganin yarda yabi ya rikice ta wani 6angaren kuma ba ƙaramin daɗi taji ba,saboda bata da wani burin daya wuce taga ta faranta mashi,tana son ganin farin cikin junaid sosai,yaron tun yana ƙarami take tsananin son shi,
  "Junaid duk naka ne wannan,Na musamman ne nasa akayi maka shi,duk duniya babu mai irin shi sae kai kaɗae,ni da kaine na bada sample ɗin yadda za'a haɗa maka shi,ka duba a jikin zoben ka gani,Harafin J ne ajiki wato farin sunanka,"
Wani irin farin ciki ne,ya cika junaid,a ƙarshe daya rasa abun cewa kawai sae ya fashe mata da kuka Yana cewa"mommy azeema,narasa da wasu kalmomi zan iya gode maki,babu su abakina,kin sanyani farin ciki sosai da wannan kyautar da kika bani.

   Hannu tasa tare da shafo gefen fuskarshi izuwa cikin sumar kanshi tace"kasan dae babu godiya atsakaninmu ko?nayi maka wannan ne saboda inga farin cikin ka,kuma Alhamdulillah nagani kuma naji daɗi sosai,abu ɗaya zakayi mun yanzu shine ka share hawayenka,bana son ganinsu suna zuba,"
  Cikin sauri junaid ya sanya hannunshi tare da goge hawayenshi duka,sannan ya mayar da hankali yana kallonta,
  Cigaba da magana tayi a natse"junaid kana addu'a kuwa"?
  gabanshi ne yaji yayi wani

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login